< 1 Tarihi 5 >

1 ’Ya’yan Ruben maza ɗan farin Isra’ila (shi ne ɗan fari, amma sa’ad da ya ƙazantar da gadon auren mahaifinsa, sai aka ba wa’yancin ɗan farinsa wa’ya’yan Yusuf maza ɗan Isra’ila; don kada a lissafta shi a tarihin zuriya bisa ga matsayin haihuwarsa,
The sons of Reuben the firstborn of Israel—now Reuben was Israel's firstborn, but his birthright was given to the sons of Joseph son of Israel because Reuben had defiled his father's couch. So he is not recorded as being the oldest son.
2 ko da yake Yahuda shi ne mafi ƙarfi cikin’yan’uwansa kuma mai mulki ya fito daga gare shi,’yancin zaman ɗan fari na Yusuf ne),
Judah was the strongest of his brothers, and the leader would come from him. But the birthright was Joseph's—
3 ’ya’yan Ruben ɗan farin Isra’ila maza su ne, Hanok, Fallu, Hezron da Karmi.
the sons of Reuben, the firstborn of Israel were Hanok, Pallu, Hezron, and Karmi.
4 Zuriyar Yowel su ne, Shemahiya, Gog, Shimeyi,
The descendants of Joel were these: Joel's son was Shemaiah. Shemaiah's son was Gog. Gog's son was Shimei.
5 Mika, Reyahiya, Ba’al,
Shimei's son was Micah. Micah's son was Reaiah. Reaiah's son was Baal.
6 da Beyera, wanda Tiglat-Fileser sarkin Assuriya ya ɗauka zuwa zaman bauta. Beyera shi ne shugaban mutanen Ruben.
Baal's son was Beerah, whom Tiglath-Pileser king of Assyria took into exile. Beerah was a leader in the tribe of Reuben.
7 Danginsu bisa ga iyalansu da aka jera bisa ga tarihin zuriyarsu su ne, Yehiyel shi ne sarki, akwai Zakariya,
Beerah's relatives according to their clans, listed according to their genealogical records: Jeiel the leader, Zechariah, and
8 da Bela ɗan Azaz. Azaz ɗan Shema daga dangin Yowel. Yowel ya yi zama a yankin Arower har zuwa Nebo da Ba’al-Meyon.
Bela son of Azaz son of Shema son of Joel. They lived in Aroer, as far as Nebo and Baal Meon,
9 Ta waje gabas sun zauna a ƙasar har zuwa bakin hamadan da ya nausa zuwa Kogin Yuferites, domin dabbobinsu sun ƙaru a Gileyad.
and eastward to the start of the wilderness that extends to the Euphrates River. This was because they had many cattle in the land of Gilead.
10 A zamanin Shawulu zuriyar Ruben sun yi yaƙi da Hagirawa, suka ci su da yaƙi, suka zauna a wuraren zaman Hagirawan ko’ina a dukan yankin gabashin Gileyad.
In the days of Saul, the tribe of Reuben attacked the Hagrites and defeated them. They lived in the Hagrites' tents throughout all the land east of Gilead.
11 Mutanen Gad sun zauna kusa da mutanen Ruben a Bashan, har zuwa Saleka.
The members of the tribe of Gad lived near them, in the land of Bashan as far as Salekah.
12 Yowel shi ne babba, sai Shafan na biyu, sa’an nan Yanai da Shafat, su ne tushen Bashan.
Joel was their leader; Shapham was second; and Janai and Shaphat in Bashan.
13 Danginsu, bisa ga iyalai su ne, Mika’ilu, Meshullam, Sheba, Yorai, Yakan, Ziya da Eber, su bakwai ne duka.
Their relatives, by their fathers' families, were Michael, Meshullam, Sheba, Jorai, Jakan, Zia, and Eber—seven in all.
14 Waɗannan su ne’ya’yan Abihayil ɗan Huri, ɗan Yarowa, ɗan Gileyad, ɗan Mika’ilu, ɗan Yeshishai, ɗan Yado, ɗan Buz.
These persons named above were the descendants of Abihail, and Abihail was the son of Huri. Huri was the son of Jaroah. Jaroah was the son of Gilead. Gilead was the son of Michael. Michael was the son of Jeshishai. Jeshishai was the son of Jahdo. Jahdo was the son of Buz.
15 Ahi ɗan Abiyel, ɗan Guni, shi ne kan iyalinsu.
Ahi son of Abdiel son of Guni, was head of their fathers' family.
16 Mutanen Gad sun zauna a Bashan da ƙauyukan da suke kurkusa da shi, da kuma a dukan makiyayan Sharon har zuwa iyaka inda suka kai.
They lived in Gilead, in Bashan, in its towns, and in all the pasturelands of Sharon as far as its borders.
17 Dukan waɗannan sun shiga tarihin zuriya a lokacin mulkin Yotam sarkin Yahuda da Yerobowam sarkin Isra’ila.
All these were listed by genealogical records in the days of Jotham king of Judah and of Jeroboam king of Israel.
18 Mutanen Ruben, mutanen Gad da rabin kabilar Manasse sun kasance da mutane 44,760 shiryayyu don aikin soja, jarumawan da za su iya riƙe garkuwa da takobi, waɗanda suke iya yin amfani da baka, waɗanda kuma aka horar don yaƙi.
The Reubenites, the Gadites, and the half tribe of Manasseh had 44,760 soldiers trained for war, who carried shield and sword, and who drew the bow.
19 Suka yi yaƙi da Hagirawa, Yetur, Nafish da Nodab.
They attacked the Hagrites, Jetur, Naphish, and Nodab.
20 Aka taimake su a yaƙin, Allah kuma ya ba da Hagirawa da dukan abokansu gare su, domin sun yi kuka gare shi a lokacin yaƙin. Ya amsa addu’o’insu, domin sun dogara gare shi.
They received divine help against them. In this way, the Hagrites and all who were with them were defeated. This was because the Israelites cried out to God in the battle, and he responded to them, because they put their trust in him.
21 Suka ƙwace dabbobin Hagirawa, raƙuma dubu hamsin, tumaki dubu ɗari biyu da hamsin da kuma jakuna dubu biyu. Suka kuma kame mutane dubu ɗari ɗaya,
They captured their animals, including fifty thousand camels, 250,000 sheep, two thousand donkeys, and 100,000 men.
22 waɗansu suka mutu, domin yaƙin na Allah ne. Suka zauna a ƙasar har lokacin da aka kai su zaman bauta.
Many fell because the battle was from God. They lived in their land until the captivity.
23 Mutanen rabin kabilar Manasse sun yi yawa; suka zauna a ƙasar daga Bashan har zuwa Ba’al-Hermon, wato, zuwa Senir (Dutsen Hermon).
The half tribe of Manasseh lived in the land of Bashan as far as Baal Hermon and Senir (that is, Mount Hermon).
24 Waɗannan su ne kawunan iyalansu. Efer, Ishi, Eliyel, Azriyel, Irmiya, Hodawiya da Yadiyel. Su jarumawa ne, sanannu, su ne kuma kawunan iyalansu.
These were the heads of their fathers' houses: Epher, Ishi, Eliel, Azriel, Jeremiah, Hodaviah, and Jahdiel. They were mighty men, famous men, heads of their fathers' houses.
25 Amma ba su yi aminci da Allahn kakanninsu ba, suka kuma yi karuwanci ga waɗansu allolin mutanen ƙasar, waɗanda Allah ya hallaka a gabansu.
But they were unfaithful to their ancestors' God. Instead, they worshiped the gods of the peoples of the land, whom God had destroyed before them.
26 Saboda haka Allah na Isra’ila ya zuga ruhun Ful sarkin Assuriya (wato, Tiglat-Fileser sarkin Assuriya), wanda ya kwashe mutanen Ruben, mutanen Gad da rabin kabilar Manasse zuwa zaman bauta. Ya kwashe su zuwa Hala, Habor, Hara da kuma kogin Gozan, inda suke har wa yau.
The God of Israel stirred up Pul king of Assyria (also called Tiglath-Pileser, king of Assyria). He took into exile the Reubenites, Gadites, and the half tribe of Manasseh. He brought them to Halah, Habor, Hara, and to the river of Gozan, where they remain to this day.

< 1 Tarihi 5 >