< 1 Tarihi 4 >
1 Zuriyoyin Yahuda su ne, Ferez, Hezron, Karmi, Hur da Shobal.
Los hijos de Judá: Fares, Hezrón, Carmi, Hur y Sobal.
2 Reyahiya ɗan Shobal shi ne mahaifin Yahat, Yahat shi ne mahaifin Ahumai da Lahad. Waɗannan su ne gidajen Zoratiyawa.
Y Reaia, hijo de Sobal, era el padre de Jahat; y Jahath fue el padre de Ahumai y Lahad. Estas son las familias de los zoratitas.
3 Waɗannan su ne’ya’yan Etam. Yezireyel, Ishma da Idbash.’Yar’uwarsu ita ce Hazzelelfoni.
Y estos fueron los hijos de Etam: Jezreel e Isma e Idbas, y el nombre de su hermana fue Haze-lelponi;
4 Fenuwel shi ne mahaifin Gedor, kuma Ezer shi ne mahaifin Husha. Waɗannan su ne zuriyar Hur, ɗan farin Efrata da mahaifin Betlehem.
Y Penuel, el padre de Gedor, y Ezer, el padre de Husa. Estos son los hijos de Hur, el hijo mayor de Efrata, el padre de Belén.
5 Asshur mahaifin Tekowa yana da mata biyu, Hela da Na’ara.
Y Asur, el padre de Tecoa, tenía dos esposas, Hela y Naara.
6 Na’ara ta haifi Ahuzzam, Hefer, Temeni da Hawahashtari. Waɗannan su ne zuriyar Na’ara.
Y Naara dio a luz a Ahuzam, Hefer Temeni y Ahastari. Estos fueron los hijos de Naara.
7 ’Ya’yan Hela maza su ne, Zeret, Zohar, Etnan,
Y los hijos de Hela fueron Zeret, Izar y Etnan.
8 da Koz. Koz ne mahaifin Anub da Hazzobeba, shi ne kuma kakan iyalin da suka fito daga zuriyar Aharhel ɗan Harum.
Y Cus fue el padre de Anub y Zobeba, y las familias de Aharhel, hijo de Harum.
9 Yabez ya fi’yan’uwansa martaba. Mahaifiyarsa ta sa masa suna Yabez, tana cewa, “Na haife shi da azaba.”
Y Jabes fue más honrado que sus hermanos; pero su madre le había dado el nombre de Jabes, diciendo: Porque lo di a luz con tristeza.
10 Yabez ya yi kuka ga Allah na Isra’ila ya ce, “Ka yi mini albarka ka fadada yankina! Bari hannunka yă kasance tare da ni, yă kuma kiyaye ni daga abin da zai cuce ni, don kada in shiga wahala.” Sai Allah ya ji roƙonsa.
Y Jabes hizo una oración al Dios de Israel, diciendo: Si tan solo me dieras una bendición, y ampliaras los límites de mi territorio, y que tu mano esté conmigo, y me guarde del mal, para que no me dañe! Y Dios le dio su deseo.
11 Kelub, ɗan’uwan Shuha, shi ne mahaifin Mehir, wanda shi ne mahaifin Eshton.
Y Quelub, el hermano de Sua, fue el padre de Mehir, quien fue el padre de Eston.
12 Eshton shi ne mahaifin Bet-Rafa, Faseya da Tehinna wanda ya haifi Ir Nahash. Waɗannan su ne mutanen Reka.
Y Eston fue el padre de Bet-rafa, Paseah y Tehina, fundador de Ir-nahas. Estos son los habitantes de Reca.
13 ’Ya’yan Kenaz maza su ne, Otniyel da Serahiya.’Ya’yan Otniyel maza su ne, Hatat da Meyonotai.
Y los hijos de Cenaz: Otoniel y Seraías; Y los hijos de Otoniel: Hatat,
14 Meyonotai shi ne mahaifin Ofra. Serahiya shi ne mahaifin Yowab, mahaifin Ge-Harashim. An kira shi haka domin mutanensa masu sana’ar hannu ne.
Y Meonotai, fue el padre de Ofra; y Seraías fue el padre de Joab, el padre de los habitantes del Valle de Carisim; Eran trabajadores artesanos.
15 ’Ya’yan Kaleb ɗan Yefunne maza su ne, Iru, Ela da Na’am. Ɗan Ela shi ne, Kenaz.
Y los hijos de Caleb, hijo de Jefone: Iru, Ela y Naam; y el hijo de Ela: Cenaz.
16 ’Ya’yan Yahallelel su ne, Zif, Zifa, Tiriya da Asarel.
Y los hijos de Jehaleel: Zif, Zifa, Tirias y Asareel.
17 ’Ya’yan Ezra maza su ne, Yeter, Mered, Efer da Yalon. Ɗaya daga cikin matan Mered ta haifi Miriyam, Shammai da Ishba wanda ya haifi Eshtemowa.
Y los hijos de Esdras: Jeter, Mered, Efer Jalón; y estos son los hijos de Bitia, la hija de faraón, la esposa de Mered, la madre de Miriam y Samai e Isba, el padre de Estemoa.
18 (Matarsa mutuniyar Yahuda kuwa ta haifi Yared mahaifin Gedor, Heber mahaifin Soko, da kuma Yekutiyel mahaifin Zanowa.) Waɗannan su ne’ya’yan Bitiya’yar Fir’auna, wadda Mered ya aura.
Y tuvo también una esposa, una mujer de la tribu de Judá, se convirtió en la madre de Jered, el padre de Gedor, y Heber, el padre de Soco, y Jecutiel, el padre de Zanoa.
19 ’Ya’yan matar Hodiya,’yar’uwar Naham su ne, suka haifi Keyila Bagarme, da Eshtemowa mutumin Ma’aka.
Y los hijos de la mujer de Hodias, la hermana de Naham, fueron los padres de Keila, él Garmita, y Estemoa él maacateo.
20 ’Ya’yan Shimon maza su ne, Amnon, Rinna, Ben-Hanan da Tilon. Zuriyar Ishi su ne, Zohet da Ben-Zohet.
Y los hijos de Simón: Amnon, Rina, Ben-hanan, Tilon. Y los hijos de Isi, Zohet; y el hijo de Zohet.
21 ’Ya’yan Shela ɗan Yahuda maza su ne, Er mahaifin Leka, La’ada mahaifin Maresha da kuma gidajen masu aikin lilin a Bet-Ashbeya,
Los hijos de Sela, el hijo de Juda: Er, el padre de Leca, Laada, el padre de Maresa, y las familias de los que hicieron ropa de lino, de la familia de Asbea;
22 da Yokim, mutanen Kozeba, da Yowash da Saraf wanda ya yi mulkin Mowab da kuma Yashubi Lehem (Waɗannan rubutattun tarihi ne na tun dā.)
Y Joacim, y los hombres de Cozeba, y Joás y Saraf, que eran gobernantes en Moab, y regresaron a Belén, según antiguas crónicas.
23 Su ne maginan tukwane waɗanda suka zauna a Netayim da Gedera; sun zauna a can suka kuma yi wa sarki aiki.
Estos eran los alfareros y la gente que vivía en Gedera entre campos plantados con muros alrededor de ellos; Ellos estaban allí para hacer el trabajo del rey.
24 Zuriyar Simeyon su ne, Nemuwel, Yamin, Yarib, Zera da Shawulu;
Los hijos de Simeón: Nemuel, Jamin, Jarib, Zera, y Saul;
25 Shawulu ya haifi Shallum, Shallum ya haifi Mibsam. Mibsam ya haifi Mishma.
Salum su hijo, Mibsam su hijo, Misma su hijo.
26 Zuriyar Mishma su ne, Hammuwel ɗansa, wanda ya haifi Zakkur, shi Zakkur kuma ya haifi Shimeyi.
Y los hijos de Misma: Hamuel su hijo, Zacur su hijo, Simei su hijo.
27 Shimeyi yana da’ya’ya maza goma sha shida da’ya’ya mata shida, amma’yan’uwansa ba su da’ya’ya da yawa; saboda haka gidansu gaba ɗaya ba tă zama mai mutane da yawa kamar mutanen Yahuda ba.
Y Simei tenía dieciséis hijos y seis hijas, pero sus hermanos tenían pocos hijos, y su familia no era tan fértil como los hijos de Judá.
28 Sun zauna a Beyersheba, Molada, Hazar Shuwal,
Y vivían en Beer-seba, Molada, Hazar-sual,
30 Betuwel, Horma, Ziklag,
Y Betuel, Horma, Siclag,
31 Bet-Markabot, Hazar-Susim, Bet-Biri da Sha’arayim. Waɗannan su ne garuruwansu har lokacin mulkin Dawuda.
Y Bet-marcabot, Hazar-susim, Bet-birai, y en Saaraim. Estas fueron sus ciudades hasta que David se convirtió en rey.
32 Ƙauyukan da suke kewayensu su ne Etam, Ayin, Rimmon, Token da Ashan, garuruwa biyar;
Y sus pueblos pequeños eran Etam, Ain, Rimon, y Toquen y Asán, cinco pueblos;
33 da kuma dukan ƙauyuka kewaye da waɗannan garuruwa har zuwa Ba’al. Waɗannan ne wuraren zamansu. Suka kuma ajiye tarihin zuriya.
Y todos los lugares pequeños alrededor de estas ciudades, hasta Baalat, el lugar alto del sur. Estos eran sus lugares donde vivieron, y tienen listas de sus generaciones.
34 Zuriyar Simeyon ta ƙunshi Meshobab, da Yamlek, da Yosha ɗan Amaziya.
Y Mesobab, Jamlec y Josías, hijo de Amasías,
35 Akwai Yowel, da Yehu ɗan Yoshibiya. Yoshibiya ɗan Seraya ne. Serahiya kuma ɗan Asiyel ne.
Y Joel y Jehú, hijo de Josibías, hijo de Seraías, hijo de Asiel,
36 Akwai Eliyohenai da Ya’akoba, da Yeshohahiya, da Asahiya, da Adiyel, da Yesimiyel, da Benahiya.
Y Elioenai, Jaacoba, Jesohaia, Asaias Adiel, Jesimiel y Benaia,
37 Akwai Ziza ɗan Shifi. Shifi ɗan Allon ne. Allon ɗan Yedahiya ne. Yedahiya ɗan Shimri ne. Shimri kuma ɗan Shemahiya ne.
Y Ziza, el hijo de Sifi, el hijo de Alón, el hijo de Jedaias, el hijo de Simri, el hijo de Semaías;
38 Mutanen da aka jera sunayensu a bisa, shugabannin gidajensu ne. Iyalansu sun ƙaru sosai,
Estos, cuyos nombres se dan, eran jefes en sus familias, y sus familias llegaron a ser muy grandes en número.
39 suka tafi bayan garin Gedor wajajen gabashin kwari suna neman makiyaya domin garkunansu.
Y fueron a la entrada de Gedor, hasta el lado este del valle, en busca de pastos para sus rebaños.
40 Suka sami makiyaya mai ciyawa mai kyau, ƙasar kuma tana da fāɗi, da salama, kuma zaman lafiya. A dā waɗansu mutanen Ham sun zauna a can.
Y llegaron a un buen pasto fértil, en un país ancho y tranquilo de gente que ama la paz; Porque las personas que vivían allí antes eran de la descendencia de Cam.
41 Mutanen da aka jera sunayensu sun zo ne a zamanin Hezekiya sarkin Yahuda. Suka yaƙi mutanen Ham a wuraren zamansu, haka kuma suka yi da Meyunawa da suke can, suka hallaka su ƙaƙaf, yadda yake har yă zuwa yau. Sa’an nan suka zauna a wurin, gama akwai makiyaya domin garkunansu.
Y estos cuyos nombres aparecen en los días de Ezequías, rey de Judá, atacaron a los meunitas que vivían allí y los pusieron fin hasta el día de hoy, y tomaron su lugar, porque allí había hierba para sus rebaños.
42 Mutum ɗari biyar na waɗannan mutane Simeyon, waɗanda Felatiya, Neyariya, Refahiya da Uzziyel,’ya’yan Ishi maza suka jagorance, sun mamaye ƙasar tudu ta Seyir.
Y algunos de ellos, quinientos de los hijos de Simeón, fueron a la región montañosa de Seir, con Pelatias, Nearias, Refaias y Uziel, los hijos de Isi, a la cabeza.
43 Suka karkashe raguwar Amalekawan da suka tsere, suka kuma zauna a can har yă zuwa yau.
Y mataron al resto de los amalecitas que se habían escapado a salvo y lo convirtieron en su lugar de residencia hasta el día de hoy.