< 1 Tarihi 4 >

1 Zuriyoyin Yahuda su ne, Ferez, Hezron, Karmi, Hur da Shobal.
Os filhos de Judá foram: Perez, Hezrom, Carmi, Hur, e Sobal.
2 Reyahiya ɗan Shobal shi ne mahaifin Yahat, Yahat shi ne mahaifin Ahumai da Lahad. Waɗannan su ne gidajen Zoratiyawa.
E Reaías, filho de Sobal, gerou a Jaate; e Jaate gerou a Aumai e a Laade. Estas são as famílias dos Zoratitas.
3 Waɗannan su ne’ya’yan Etam. Yezireyel, Ishma da Idbash.’Yar’uwarsu ita ce Hazzelelfoni.
E estas são as do pai de Etã: Jezreel, Isma, e Idbás. E o nome da irmã deles era Hazelelponi.
4 Fenuwel shi ne mahaifin Gedor, kuma Ezer shi ne mahaifin Husha. Waɗannan su ne zuriyar Hur, ɗan farin Efrata da mahaifin Betlehem.
E Penuel foi pai de Gedor, e Ézer pai de Husá. Estes foram os filhos de Hur, primogênito de Efrata, pai de Belém.
5 Asshur mahaifin Tekowa yana da mata biyu, Hela da Na’ara.
E Asur, pai de Tecoa, teve duas mulheres: Helá, e Naará.
6 Na’ara ta haifi Ahuzzam, Hefer, Temeni da Hawahashtari. Waɗannan su ne zuriyar Na’ara.
E Naará lhe gerou a Auzão, Héfer, Temeni, e a Haastari. Estes foram os filhos de Naará.
7 ’Ya’yan Hela maza su ne, Zeret, Zohar, Etnan,
E os filhos de Helá foram: Zerete, Zoar, e Etnã.
8 da Koz. Koz ne mahaifin Anub da Hazzobeba, shi ne kuma kakan iyalin da suka fito daga zuriyar Aharhel ɗan Harum.
E Coz gerou a Anube, e a Zobeba, e as famílias de Aarel, filho de Harum.
9 Yabez ya fi’yan’uwansa martaba. Mahaifiyarsa ta sa masa suna Yabez, tana cewa, “Na haife shi da azaba.”
E Jabez foi mais honrado que seus irmãos; sua mãe o chamara de Jabez, dizendo: Pois com dores eu o dei à luz.
10 Yabez ya yi kuka ga Allah na Isra’ila ya ce, “Ka yi mini albarka ka fadada yankina! Bari hannunka yă kasance tare da ni, yă kuma kiyaye ni daga abin da zai cuce ni, don kada in shiga wahala.” Sai Allah ya ji roƙonsa.
Mas Jabez invocou ao Deus de Israel, dizendo: Ah, se tu me abençoares muito, e ampliares os meus limites, e se tua mão for comigo, e me protegeres do mal, para que eu não sofra! E Deus fez suceder o que ele havia pedido.
11 Kelub, ɗan’uwan Shuha, shi ne mahaifin Mehir, wanda shi ne mahaifin Eshton.
E Quelube, irmão de Suá gerou a Maquir, que foi o pai de Estom.
12 Eshton shi ne mahaifin Bet-Rafa, Faseya da Tehinna wanda ya haifi Ir Nahash. Waɗannan su ne mutanen Reka.
E Estom gerou a Bete-Rafa, Paseia, e a Teína, pai da cidade de Naás; estes foram os homens de Reca.
13 ’Ya’yan Kenaz maza su ne, Otniyel da Serahiya.’Ya’yan Otniyel maza su ne, Hatat da Meyonotai.
Os filhos de Quenaz foram: Otniel e Seraías. Os filhos de Otniel: Hatate [e Meonotai].
14 Meyonotai shi ne mahaifin Ofra. Serahiya shi ne mahaifin Yowab, mahaifin Ge-Harashim. An kira shi haka domin mutanensa masu sana’ar hannu ne.
E Meonotai gerou a Ofra; e Seraías gerou a Joabe, pai [dos moradores] do Vale dos Artesãos, porque foram artesãos.
15 ’Ya’yan Kaleb ɗan Yefunne maza su ne, Iru, Ela da Na’am. Ɗan Ela shi ne, Kenaz.
Os filhos de Calebe, filho de Jefoné foram: Iru, Elá, e Naã; e filho de Elá foi Quenaz.
16 ’Ya’yan Yahallelel su ne, Zif, Zifa, Tiriya da Asarel.
Os filhos de Jealelel foram: Zife, Zifa, Tíria, e Asareel.
17 ’Ya’yan Ezra maza su ne, Yeter, Mered, Efer da Yalon. Ɗaya daga cikin matan Mered ta haifi Miriyam, Shammai da Ishba wanda ya haifi Eshtemowa.
E os filhos de Ezra foram: Jéter, Merede, Efer, e Jalom. E [sua mulher] também deu à luz a Miriã, Samai, e a Isbá, pai de Estemoa.
18 (Matarsa mutuniyar Yahuda kuwa ta haifi Yared mahaifin Gedor, Heber mahaifin Soko, da kuma Yekutiyel mahaifin Zanowa.) Waɗannan su ne’ya’yan Bitiya’yar Fir’auna, wadda Mered ya aura.
E sua mulher Judia lhe deu à luz a Jerede pai de Gedor, a Héber pai de Socó, e a Jecutiel pai de Zanoa. Estes foram os filhos de Bitias, filha de Faraó, a qual Merede teve por esposa.
19 ’Ya’yan matar Hodiya,’yar’uwar Naham su ne, suka haifi Keyila Bagarme, da Eshtemowa mutumin Ma’aka.
E os filhos da mulher de Hodias, irmã de Naã, foram: o pai de Queila o garmita, e Estemoa o maacatita.
20 ’Ya’yan Shimon maza su ne, Amnon, Rinna, Ben-Hanan da Tilon. Zuriyar Ishi su ne, Zohet da Ben-Zohet.
E os filhos de Simeão foram: Amnom, Rina, Ben-Hanã, e Tilom. E os filhos de Isi foram: Zoete, e Ben-Zoete.
21 ’Ya’yan Shela ɗan Yahuda maza su ne, Er mahaifin Leka, La’ada mahaifin Maresha da kuma gidajen masu aikin lilin a Bet-Ashbeya,
Os filhos de Selá, filho de Judá foram: Er, pai de Leca, e Lada, pai de Maressa, e as famílias da casa dos [trabalhadores] do linho em Bete-Asbeia;
22 da Yokim, mutanen Kozeba, da Yowash da Saraf wanda ya yi mulkin Mowab da kuma Yashubi Lehem (Waɗannan rubutattun tarihi ne na tun dā.)
Como também Joquim, os homens de Cozeba, Joás, e Sarafe (os quais dominaram sobre os moabitas), e Jasubi-Leem. Estes registros, porém, são antigos.
23 Su ne maginan tukwane waɗanda suka zauna a Netayim da Gedera; sun zauna a can suka kuma yi wa sarki aiki.
Estes foram oleiros, e habitavam em Netaim e Gedera; eles ficaram ali com o rei em sua obra.
24 Zuriyar Simeyon su ne, Nemuwel, Yamin, Yarib, Zera da Shawulu;
Os filhos de Simeão foram: Nemuel, Jamim, Jaribe, Zerá, Saul;
25 Shawulu ya haifi Shallum, Shallum ya haifi Mibsam. Mibsam ya haifi Mishma.
Cujo filho foi Salum, cujo filho foi Mibsão, cujo filho foi e Misma.
26 Zuriyar Mishma su ne, Hammuwel ɗansa, wanda ya haifi Zakkur, shi Zakkur kuma ya haifi Shimeyi.
Os filhos de Misma foram: seu filho Hamuel, cujo filho foi Zacur, cujo filho foi Simei.
27 Shimeyi yana da’ya’ya maza goma sha shida da’ya’ya mata shida, amma’yan’uwansa ba su da’ya’ya da yawa; saboda haka gidansu gaba ɗaya ba tă zama mai mutane da yawa kamar mutanen Yahuda ba.
E Simei teve dezesseis filhos e seis filhas, porém seus irmãos não tiveram muitos filhos, e toda a sua família não se multiplicou tanto como a dos filhos de Judá.
28 Sun zauna a Beyersheba, Molada, Hazar Shuwal,
E habitaram em Berseba, Moladá, Hazar-Sual,
29 Bilha, Ezem, Tolad
E em Bila, Ezém, Tolade,
30 Betuwel, Horma, Ziklag,
Betuel, Hormá, Ziclague.
31 Bet-Markabot, Hazar-Susim, Bet-Biri da Sha’arayim. Waɗannan su ne garuruwansu har lokacin mulkin Dawuda.
Bete-Marcabote, Hazar-Susim, Bete-Birai, e em Saaraim. Estas foram suas cidades até quando Davi começou a reinar.
32 Ƙauyukan da suke kewayensu su ne Etam, Ayin, Rimmon, Token da Ashan, garuruwa biyar;
E suas aldeias foram: Etã, Aim, Rimom, e Toquém, e Asã, cinco cidades;
33 da kuma dukan ƙauyuka kewaye da waɗannan garuruwa har zuwa Ba’al. Waɗannan ne wuraren zamansu. Suka kuma ajiye tarihin zuriya.
E todas as suas aldeias que estavam ao redor destas cidades, até Baal. Estas foram suas habitações, e suas genealogias.
34 Zuriyar Simeyon ta ƙunshi Meshobab, da Yamlek, da Yosha ɗan Amaziya.
Porém Mesobabe, Janleque, Josias filho de Amazias;
35 Akwai Yowel, da Yehu ɗan Yoshibiya. Yoshibiya ɗan Seraya ne. Serahiya kuma ɗan Asiyel ne.
Joel, Jeú filho de Josibias, filho de Seraías, filho de Asiel;
36 Akwai Eliyohenai da Ya’akoba, da Yeshohahiya, da Asahiya, da Adiyel, da Yesimiyel, da Benahiya.
E Elioenai, Jaacobá, Jesoaías, Asaias, Adiel, Jesimiel, Benaia;
37 Akwai Ziza ɗan Shifi. Shifi ɗan Allon ne. Allon ɗan Yedahiya ne. Yedahiya ɗan Shimri ne. Shimri kuma ɗan Shemahiya ne.
E Ziza filho de Sifi, filho de Alom, filho de Jedaías, filho de Sinri, filho de Semaías.
38 Mutanen da aka jera sunayensu a bisa, shugabannin gidajensu ne. Iyalansu sun ƙaru sosai,
Estes registrados por [seus] nomes foram os líderes de suas famílias, e que foram multiplicados muito nas casas de seus pais.
39 suka tafi bayan garin Gedor wajajen gabashin kwari suna neman makiyaya domin garkunansu.
E chegaram até a entrada de Gedor, até o oriente do vale, buscando pastos para suas ovelhas.
40 Suka sami makiyaya mai ciyawa mai kyau, ƙasar kuma tana da fāɗi, da salama, kuma zaman lafiya. A dā waɗansu mutanen Ham sun zauna a can.
E acharam pastos férteis e bons, e a terra era espaçosa, quieta, e descansada, porque os de Cam tinham habitado ali antes.
41 Mutanen da aka jera sunayensu sun zo ne a zamanin Hezekiya sarkin Yahuda. Suka yaƙi mutanen Ham a wuraren zamansu, haka kuma suka yi da Meyunawa da suke can, suka hallaka su ƙaƙaf, yadda yake har yă zuwa yau. Sa’an nan suka zauna a wurin, gama akwai makiyaya domin garkunansu.
Estes, pois, que foram escritos por seus nomes, vieram nos dias de Ezequias rei de Judá, e derrubaram as tendas e habitações dos que se acharam ali, e os destruíram até hoje; e habitaram ali em seu lugar, porque ali havia pastos para suas ovelhas.
42 Mutum ɗari biyar na waɗannan mutane Simeyon, waɗanda Felatiya, Neyariya, Refahiya da Uzziyel,’ya’yan Ishi maza suka jagorance, sun mamaye ƙasar tudu ta Seyir.
Também [alguns] deles, quinhentos homens dos filhos de Simeão, se foram ao monte de Seir, levando como capitães a Pelatias, Nearias, Refaías, e a Uziel, filhos de Isi;
43 Suka karkashe raguwar Amalekawan da suka tsere, suka kuma zauna a can har yă zuwa yau.
E mataram os que haviam restado dos amalequitas, e habitaram ali até hoje.

< 1 Tarihi 4 >