< 1 Tarihi 4 >

1 Zuriyoyin Yahuda su ne, Ferez, Hezron, Karmi, Hur da Shobal.
Les fils de Juda: Pharès. Hesron, Charmi, Hur et Sobal.
2 Reyahiya ɗan Shobal shi ne mahaifin Yahat, Yahat shi ne mahaifin Ahumai da Lahad. Waɗannan su ne gidajen Zoratiyawa.
Or Raïa, fils de Sobal, engendra Jabath, dont naquirent Ahumaï et Laad; ce sont là les familles de Sarathi.
3 Waɗannan su ne’ya’yan Etam. Yezireyel, Ishma da Idbash.’Yar’uwarsu ita ce Hazzelelfoni.
Voici aussi la lignée d’Etam: Jezrahel, Jéséma et Jédébos. De plus, le nom de leur sœur fut Asalelphuni.
4 Fenuwel shi ne mahaifin Gedor, kuma Ezer shi ne mahaifin Husha. Waɗannan su ne zuriyar Hur, ɗan farin Efrata da mahaifin Betlehem.
Or Phanuel fut père de Gédor, et Eser, père d’Hosa; ce sont là les fils d’Hur, premier-né d’Ephratha, et père de Bethléhem.
5 Asshur mahaifin Tekowa yana da mata biyu, Hela da Na’ara.
Mais Assur, père de Thécua, avait deux femmes: Halaa et Naara.
6 Na’ara ta haifi Ahuzzam, Hefer, Temeni da Hawahashtari. Waɗannan su ne zuriyar Na’ara.
Or Naara lui enfanta Oozam, Hépher, Themani et Ahasthari; ce sont là les fils de Naara;
7 ’Ya’yan Hela maza su ne, Zeret, Zohar, Etnan,
Mais les fils de Halaa: Séreth, Isaar et Ethnan.
8 da Koz. Koz ne mahaifin Anub da Hazzobeba, shi ne kuma kakan iyalin da suka fito daga zuriyar Aharhel ɗan Harum.
Et Cos engendra Anob et Soboba, et la famille d’Aharéhel, fils d’Arum.
9 Yabez ya fi’yan’uwansa martaba. Mahaifiyarsa ta sa masa suna Yabez, tana cewa, “Na haife shi da azaba.”
Mais Jabès fut plus illustre que ses frères; et sa mère lui donna le nom de Jabès, disant: C’est parce que je l’ai enfanté dans la douleur.
10 Yabez ya yi kuka ga Allah na Isra’ila ya ce, “Ka yi mini albarka ka fadada yankina! Bari hannunka yă kasance tare da ni, yă kuma kiyaye ni daga abin da zai cuce ni, don kada in shiga wahala.” Sai Allah ya ji roƙonsa.
Or Jabès invoqua le Dieu d’Israël, disant: Ô si, me bénissant, vous me bénissiez, et si vous étendiez mes limites; si votre main était avec moi, et si vous faisiez que je ne sois pas opprimé par la malice! Et Dieu lui accorda ce qu’il demanda.
11 Kelub, ɗan’uwan Shuha, shi ne mahaifin Mehir, wanda shi ne mahaifin Eshton.
Quant à Caleb, frère de Sua, il engendra Mahir, qui fut père d’Esthon.
12 Eshton shi ne mahaifin Bet-Rafa, Faseya da Tehinna wanda ya haifi Ir Nahash. Waɗannan su ne mutanen Reka.
Or Esthon engendra Bethrapha, Phessé, et Téhinna, le père de la ville de Naas: ce sont là les hommes de la ville de Récha.
13 ’Ya’yan Kenaz maza su ne, Otniyel da Serahiya.’Ya’yan Otniyel maza su ne, Hatat da Meyonotai.
Mais les fils de Cénez furent Othoniel et Saraïa. Et les fils d’Othoniel: Hathath et Maonathi.
14 Meyonotai shi ne mahaifin Ofra. Serahiya shi ne mahaifin Yowab, mahaifin Ge-Harashim. An kira shi haka domin mutanensa masu sana’ar hannu ne.
Maonathi engendra Ophra; mais Saraïa engendra Joab, le père de la Vallée des ouvriers; car là étaient des ouvriers.
15 ’Ya’yan Kaleb ɗan Yefunne maza su ne, Iru, Ela da Na’am. Ɗan Ela shi ne, Kenaz.
Or les fils de Caleb, fils de Jéphoné, furent Hir, Ela et Naham. De plus, les fils d’Ela: Cénez.
16 ’Ya’yan Yahallelel su ne, Zif, Zifa, Tiriya da Asarel.
Les fils de Jaléléel aussi furent Ziph, Zipha, Thiria, et Asraël;
17 ’Ya’yan Ezra maza su ne, Yeter, Mered, Efer da Yalon. Ɗaya daga cikin matan Mered ta haifi Miriyam, Shammai da Ishba wanda ya haifi Eshtemowa.
Et les fils d’Ezra: Jéther, Méred, Epher et Jalon; il engendra encore Marie, Sammaï et Jesba, père d’Esthamo.
18 (Matarsa mutuniyar Yahuda kuwa ta haifi Yared mahaifin Gedor, Heber mahaifin Soko, da kuma Yekutiyel mahaifin Zanowa.) Waɗannan su ne’ya’yan Bitiya’yar Fir’auna, wadda Mered ya aura.
Sa femme aussi, Judaïa, enfanta Jared, père de Gédor, Héber, père de Socho, et Icuthiel, père de Zanoé; or voilà les fils de Béthie, fille de Pharaon, que Méred prit pour femme.
19 ’Ya’yan matar Hodiya,’yar’uwar Naham su ne, suka haifi Keyila Bagarme, da Eshtemowa mutumin Ma’aka.
Et les fils de sa femme Odaïa, sœur de Naham, père de Céila, furent Garmi, et Esthamo, qui était de Machathi.
20 ’Ya’yan Shimon maza su ne, Amnon, Rinna, Ben-Hanan da Tilon. Zuriyar Ishi su ne, Zohet da Ben-Zohet.
De même les fils de Simon furent Amnon et Rinna, fils d’Hanan, et Thilon. Et les fils de Jési: Zoheth et Benzoheth.
21 ’Ya’yan Shela ɗan Yahuda maza su ne, Er mahaifin Leka, La’ada mahaifin Maresha da kuma gidajen masu aikin lilin a Bet-Ashbeya,
Les fils de Séla, fils de Juda: Her, père de Lécha, et Laada, père de Marésa, et les familles de la maison de ceux qui travaillent le fin lin dans la Maison du serment;
22 da Yokim, mutanen Kozeba, da Yowash da Saraf wanda ya yi mulkin Mowab da kuma Yashubi Lehem (Waɗannan rubutattun tarihi ne na tun dā.)
Celui qui a fait arrêter le soleil, et les hommes de Mensonge, et le Sur, et l’Incendiaire, qui furent princes dans Moab, et qui revinrent à Lahem: or ces paroles sont anciennes.
23 Su ne maginan tukwane waɗanda suka zauna a Netayim da Gedera; sun zauna a can suka kuma yi wa sarki aiki.
Ce sont là les potiers habitant dans des plantations et dans des haies, auprès du roi, pour ses ouvrages, et qui ont demeuré là.
24 Zuriyar Simeyon su ne, Nemuwel, Yamin, Yarib, Zera da Shawulu;
Les fils de Siméon furent Namuel, Jamin, Jarib, Zara, et Saül,
25 Shawulu ya haifi Shallum, Shallum ya haifi Mibsam. Mibsam ya haifi Mishma.
Dont le fils, Sellum, dont le fils, Mapsam, dont le fils, Masma.
26 Zuriyar Mishma su ne, Hammuwel ɗansa, wanda ya haifi Zakkur, shi Zakkur kuma ya haifi Shimeyi.
Les fils de Masma: Hamuel, dont le fils, Zachur, dont le fils, Séméi.
27 Shimeyi yana da’ya’ya maza goma sha shida da’ya’ya mata shida, amma’yan’uwansa ba su da’ya’ya da yawa; saboda haka gidansu gaba ɗaya ba tă zama mai mutane da yawa kamar mutanen Yahuda ba.
Les fils de Séméi furent au nombre de seize, et ses filles, au nombre de cinq; mais ses frères n’eurent pas beaucoup d’enfants, et toute leur parenté ne put égaler le nombre des enfants de Juda.
28 Sun zauna a Beyersheba, Molada, Hazar Shuwal,
Or ils habitèrent dans Bersabée, dans Molada, dans Hasarsuhal,
29 Bilha, Ezem, Tolad
Dans Bala, dans Asom, dans Tholad,
30 Betuwel, Horma, Ziklag,
Dans Bathuel, dans Horma et dans Sicéleg,
31 Bet-Markabot, Hazar-Susim, Bet-Biri da Sha’arayim. Waɗannan su ne garuruwansu har lokacin mulkin Dawuda.
Dans Bethmarchaboth, dans Hasarsusim, dans Bethbéraï et dans Saarim: ce furent leurs villes jusqu’au roi David.
32 Ƙauyukan da suke kewayensu su ne Etam, Ayin, Rimmon, Token da Ashan, garuruwa biyar;
Leurs villages aussi furent Etam, Aën, Remmon, Thochen et Asan: cinq villes.
33 da kuma dukan ƙauyuka kewaye da waɗannan garuruwa har zuwa Ba’al. Waɗannan ne wuraren zamansu. Suka kuma ajiye tarihin zuriya.
Et toutes les bourgades aux environs de ces villes jusqu’à Baal furent à eux: voilà leur habitation, et la distribution de leurs demeures.
34 Zuriyar Simeyon ta ƙunshi Meshobab, da Yamlek, da Yosha ɗan Amaziya.
De plus, Mosobab, Jemlech, et Josa, fils d’Amasias,
35 Akwai Yowel, da Yehu ɗan Yoshibiya. Yoshibiya ɗan Seraya ne. Serahiya kuma ɗan Asiyel ne.
Joël, et Jéhu, fils de Josabia, fils de Saraïa, fils d’Asiel,
36 Akwai Eliyohenai da Ya’akoba, da Yeshohahiya, da Asahiya, da Adiyel, da Yesimiyel, da Benahiya.
Elioénaï, Jacoba, Isuhaïa, Asaïa, Adiel, Ismiel et Banaïa,
37 Akwai Ziza ɗan Shifi. Shifi ɗan Allon ne. Allon ɗan Yedahiya ne. Yedahiya ɗan Shimri ne. Shimri kuma ɗan Shemahiya ne.
Ainsi que Ziza, fils de Séphéi, fils d’Allon, fils d’Idaïa, fils de Semri, fils de Samaïa;
38 Mutanen da aka jera sunayensu a bisa, shugabannin gidajensu ne. Iyalansu sun ƙaru sosai,
Ceux-là sont les princes renommés dans leurs familles; et ils se multiplièrent extrêmement dans la maison de leurs alliances.
39 suka tafi bayan garin Gedor wajajen gabashin kwari suna neman makiyaya domin garkunansu.
Et ils partirent pour pénétrer dans Gador, jusqu’à l’orient de la vallée, afin de chercher des pâturages pour leurs troupeaux.
40 Suka sami makiyaya mai ciyawa mai kyau, ƙasar kuma tana da fāɗi, da salama, kuma zaman lafiya. A dā waɗansu mutanen Ham sun zauna a can.
Et ils trouvèrent des pâturages abondants et excellents, et une terre très spacieuse, paisible et fertile, dans laquelle s’étaient établis des descendants de Cham.
41 Mutanen da aka jera sunayensu sun zo ne a zamanin Hezekiya sarkin Yahuda. Suka yaƙi mutanen Ham a wuraren zamansu, haka kuma suka yi da Meyunawa da suke can, suka hallaka su ƙaƙaf, yadda yake har yă zuwa yau. Sa’an nan suka zauna a wurin, gama akwai makiyaya domin garkunansu.
Ceux-ci donc, que plus haut nous avons désignés nommément, vinrent aux jours d’Ézéchias, roi de Juda, attaquèrent leur tabernacles, et les habitants qui s’y trouvèrent; et ils les ont détruits jusqu’au présent jour; et ils y ont habité en leur place, parce qu’ils ont trouvé là même de très abondants pâturages.
42 Mutum ɗari biyar na waɗannan mutane Simeyon, waɗanda Felatiya, Neyariya, Refahiya da Uzziyel,’ya’yan Ishi maza suka jagorance, sun mamaye ƙasar tudu ta Seyir.
Parmi les mêmes fils de Siméon, cinq cents hommes s’en allèrent à la montagne de Séir, ayant pour chefs Phaltias, Naaria, Raphaïa et Osiel, fils de Jési;
43 Suka karkashe raguwar Amalekawan da suka tsere, suka kuma zauna a can har yă zuwa yau.
Et ils défirent les restes qui avaient pu échapper des Amalécites; et ils ont habité dans ce pays, en leur place, jusqu’à ce jour.

< 1 Tarihi 4 >