< 1 Tarihi 4 >
1 Zuriyoyin Yahuda su ne, Ferez, Hezron, Karmi, Hur da Shobal.
Fils de Juda: Pérets, Hetsron, Carmi, Hur et Schobal.
2 Reyahiya ɗan Shobal shi ne mahaifin Yahat, Yahat shi ne mahaifin Ahumai da Lahad. Waɗannan su ne gidajen Zoratiyawa.
Reaja, fils de Schobal, engendra Jachath; Jachath engendra Achumaï et Lahad. Ce sont les familles des Tsoreathiens.
3 Waɗannan su ne’ya’yan Etam. Yezireyel, Ishma da Idbash.’Yar’uwarsu ita ce Hazzelelfoni.
Voici les descendants du père d’Étham: Jizreel, Jischma et Jidbasch; le nom de leur sœur était Hatselelponi.
4 Fenuwel shi ne mahaifin Gedor, kuma Ezer shi ne mahaifin Husha. Waɗannan su ne zuriyar Hur, ɗan farin Efrata da mahaifin Betlehem.
Penuel était père de Guedor, et Ézer père de Huscha. Ce sont là les fils de Hur, premier-né d’Éphrata, père de Bethléhem.
5 Asshur mahaifin Tekowa yana da mata biyu, Hela da Na’ara.
Aschchur, père de Tekoa, eut deux femmes, Hélea et Naara.
6 Na’ara ta haifi Ahuzzam, Hefer, Temeni da Hawahashtari. Waɗannan su ne zuriyar Na’ara.
Naara lui enfanta Achuzzam, Hépher, Thémeni et Achaschthari: ce sont là les fils de Naara.
7 ’Ya’yan Hela maza su ne, Zeret, Zohar, Etnan,
Fils de Hélea: Tséreth, Tsochar et Éthnan.
8 da Koz. Koz ne mahaifin Anub da Hazzobeba, shi ne kuma kakan iyalin da suka fito daga zuriyar Aharhel ɗan Harum.
Kots engendra Anub et Hatsobéba, et les familles d’Acharchel, fils d’Harum.
9 Yabez ya fi’yan’uwansa martaba. Mahaifiyarsa ta sa masa suna Yabez, tana cewa, “Na haife shi da azaba.”
Jaebets était plus considéré que ses frères; sa mère lui donna le nom de Jaebets, en disant: C’est parce que je l’ai enfanté avec douleur.
10 Yabez ya yi kuka ga Allah na Isra’ila ya ce, “Ka yi mini albarka ka fadada yankina! Bari hannunka yă kasance tare da ni, yă kuma kiyaye ni daga abin da zai cuce ni, don kada in shiga wahala.” Sai Allah ya ji roƙonsa.
Jaebets invoqua le Dieu d’Israël, en disant: Si tu me bénis et que tu étendes mes limites, si ta main est avec moi, et si tu me préserves du malheur, en sorte que je ne sois pas dans la souffrance!… Et Dieu accorda ce qu’il avait demandé.
11 Kelub, ɗan’uwan Shuha, shi ne mahaifin Mehir, wanda shi ne mahaifin Eshton.
Kelub, frère de Schucha, engendra Mechir, qui fut père d’Eschthon.
12 Eshton shi ne mahaifin Bet-Rafa, Faseya da Tehinna wanda ya haifi Ir Nahash. Waɗannan su ne mutanen Reka.
Eschthon engendra la maison de Rapha, Paséach, et Thechinna, père de la ville de Nachasch. Ce sont là les hommes de Réca.
13 ’Ya’yan Kenaz maza su ne, Otniyel da Serahiya.’Ya’yan Otniyel maza su ne, Hatat da Meyonotai.
Fils de Kenaz: Othniel et Seraja. Fils d’Othniel: Hathath.
14 Meyonotai shi ne mahaifin Ofra. Serahiya shi ne mahaifin Yowab, mahaifin Ge-Harashim. An kira shi haka domin mutanensa masu sana’ar hannu ne.
Meonothaï engendra Ophra. Seraja engendra Joab, père de la vallée des ouvriers; car ils étaient ouvriers.
15 ’Ya’yan Kaleb ɗan Yefunne maza su ne, Iru, Ela da Na’am. Ɗan Ela shi ne, Kenaz.
Fils de Caleb, fils de Jephunné: Iru, Éla et Naam, et les fils d’Éla, et Kenaz.
16 ’Ya’yan Yahallelel su ne, Zif, Zifa, Tiriya da Asarel.
Fils de Jehalléleel: Ziph, Zipha, Thirja et Asareel.
17 ’Ya’yan Ezra maza su ne, Yeter, Mered, Efer da Yalon. Ɗaya daga cikin matan Mered ta haifi Miriyam, Shammai da Ishba wanda ya haifi Eshtemowa.
Fils d’Esdras: Jéther, Méred, Épher et Jalon. La femme de Méred enfanta Miriam, Schammaï, et Jischbach, père d’Eschthemoa.
18 (Matarsa mutuniyar Yahuda kuwa ta haifi Yared mahaifin Gedor, Heber mahaifin Soko, da kuma Yekutiyel mahaifin Zanowa.) Waɗannan su ne’ya’yan Bitiya’yar Fir’auna, wadda Mered ya aura.
Sa femme, la Juive, enfanta Jéred, père de Guedor, Héber, père de Soco, et Jekuthiel, père de Zanoach. Ceux-là sont les fils de Bithja, fille de Pharaon, que Méred prit pour femme.
19 ’Ya’yan matar Hodiya,’yar’uwar Naham su ne, suka haifi Keyila Bagarme, da Eshtemowa mutumin Ma’aka.
Fils de la femme d’Hodija, sœur de Nacham: le père de Kehila, le Garmien, et Eschthemoa, le Maacathien.
20 ’Ya’yan Shimon maza su ne, Amnon, Rinna, Ben-Hanan da Tilon. Zuriyar Ishi su ne, Zohet da Ben-Zohet.
Fils de Simon: Amnon, Rinna, Ben-Hanan et Thilon. Fils de Jischeï: Zocheth et Ben-Zocheth.
21 ’Ya’yan Shela ɗan Yahuda maza su ne, Er mahaifin Leka, La’ada mahaifin Maresha da kuma gidajen masu aikin lilin a Bet-Ashbeya,
Fils de Schéla, fils de Juda: Er, père de Léca, Laeda, père de Maréscha, et les familles de la maison où l’on travaille le byssus, de la maison d’Aschbéa,
22 da Yokim, mutanen Kozeba, da Yowash da Saraf wanda ya yi mulkin Mowab da kuma Yashubi Lehem (Waɗannan rubutattun tarihi ne na tun dā.)
et Jokim, et les hommes de Cozéba, et Joas et Saraph, qui dominèrent sur Moab, et Jaschubi-Léchem. Ces choses sont anciennes.
23 Su ne maginan tukwane waɗanda suka zauna a Netayim da Gedera; sun zauna a can suka kuma yi wa sarki aiki.
C’étaient les potiers et les habitants des plantations et des parcs; ils demeuraient là près du roi et travaillaient pour lui.
24 Zuriyar Simeyon su ne, Nemuwel, Yamin, Yarib, Zera da Shawulu;
Fils de Siméon: Nemuel, Jamin, Jarib, Zérach, Saül.
25 Shawulu ya haifi Shallum, Shallum ya haifi Mibsam. Mibsam ya haifi Mishma.
Fils de Saül: Schallum. Mibsam, son fils; Mischma, son fils.
26 Zuriyar Mishma su ne, Hammuwel ɗansa, wanda ya haifi Zakkur, shi Zakkur kuma ya haifi Shimeyi.
Fils de Mischma: Hammuel, son fils. Zaccur, son fils; Schimeï, son fils.
27 Shimeyi yana da’ya’ya maza goma sha shida da’ya’ya mata shida, amma’yan’uwansa ba su da’ya’ya da yawa; saboda haka gidansu gaba ɗaya ba tă zama mai mutane da yawa kamar mutanen Yahuda ba.
Schimeï eut seize fils et six filles. Ses frères n’eurent pas beaucoup de fils. Et toutes leurs familles ne se multiplièrent pas autant que les fils de Juda.
28 Sun zauna a Beyersheba, Molada, Hazar Shuwal,
Ils habitaient à Beer-Schéba, à Molada, à Hatsar-Schual,
à Bilha, à Étsem, à Tholad,
30 Betuwel, Horma, Ziklag,
à Bethuel, à Horma, à Tsiklag,
31 Bet-Markabot, Hazar-Susim, Bet-Biri da Sha’arayim. Waɗannan su ne garuruwansu har lokacin mulkin Dawuda.
à Beth-Marcaboth, à Hatsar-Susim, à Beth-Bireï et à Schaaraïm. Ce furent là leurs villes jusqu’au règne de David, et leurs villages.
32 Ƙauyukan da suke kewayensu su ne Etam, Ayin, Rimmon, Token da Ashan, garuruwa biyar;
Ils avaient encore Étham, Aïn, Rimmon, Thoken et Aschan, cinq villes;
33 da kuma dukan ƙauyuka kewaye da waɗannan garuruwa har zuwa Ba’al. Waɗannan ne wuraren zamansu. Suka kuma ajiye tarihin zuriya.
et tous les villages aux environs de ces villes, jusqu’à Baal. Voilà leurs habitations et leur généalogie.
34 Zuriyar Simeyon ta ƙunshi Meshobab, da Yamlek, da Yosha ɗan Amaziya.
Meschobab; Jamlec; Joscha, fils d’Amatsia;
35 Akwai Yowel, da Yehu ɗan Yoshibiya. Yoshibiya ɗan Seraya ne. Serahiya kuma ɗan Asiyel ne.
Joël; Jéhu, fils de Joschibia, fils de Seraja, fils d’Asiel;
36 Akwai Eliyohenai da Ya’akoba, da Yeshohahiya, da Asahiya, da Adiyel, da Yesimiyel, da Benahiya.
Éljoénaï; Jaakoba; Jeschochaja; Asaja; Adiel; Jesimiel; Benaja;
37 Akwai Ziza ɗan Shifi. Shifi ɗan Allon ne. Allon ɗan Yedahiya ne. Yedahiya ɗan Shimri ne. Shimri kuma ɗan Shemahiya ne.
Ziza, fils de Schipheï, fils d’Allon, fils de Jedaja, fils de Schimri, fils de Schemaeja.
38 Mutanen da aka jera sunayensu a bisa, shugabannin gidajensu ne. Iyalansu sun ƙaru sosai,
Ceux-là, désignés par leurs noms, étaient princes dans leurs familles, et leurs maisons paternelles prirent un grand accroissement.
39 suka tafi bayan garin Gedor wajajen gabashin kwari suna neman makiyaya domin garkunansu.
Ils allèrent du côté de Guedor jusqu’à l’orient de la vallée, afin de chercher des pâturages pour leurs troupeaux.
40 Suka sami makiyaya mai ciyawa mai kyau, ƙasar kuma tana da fāɗi, da salama, kuma zaman lafiya. A dā waɗansu mutanen Ham sun zauna a can.
Ils trouvèrent de gras et bons pâturages, et un pays vaste, tranquille et paisible, car ceux qui l’habitaient auparavant descendaient de Cham.
41 Mutanen da aka jera sunayensu sun zo ne a zamanin Hezekiya sarkin Yahuda. Suka yaƙi mutanen Ham a wuraren zamansu, haka kuma suka yi da Meyunawa da suke can, suka hallaka su ƙaƙaf, yadda yake har yă zuwa yau. Sa’an nan suka zauna a wurin, gama akwai makiyaya domin garkunansu.
Ces hommes, inscrits par leurs noms, arrivèrent du temps d’Ézéchias, roi de Juda; ils attaquèrent leurs tentes et les Maonites qui se trouvaient là, ils les dévouèrent par interdit jusqu’à ce jour, et ils s’établirent à leur place, car il y avait là des pâturages pour leurs troupeaux.
42 Mutum ɗari biyar na waɗannan mutane Simeyon, waɗanda Felatiya, Neyariya, Refahiya da Uzziyel,’ya’yan Ishi maza suka jagorance, sun mamaye ƙasar tudu ta Seyir.
Il y eut aussi des fils de Siméon qui allèrent à la montagne de Séir, au nombre de cinq cents hommes. Ils avaient à leur tête Pelathia, Nearia, Rephaja et Uziel, fils de Jischeï.
43 Suka karkashe raguwar Amalekawan da suka tsere, suka kuma zauna a can har yă zuwa yau.
Ils battirent le reste des réchappés d’Amalek, et ils s’établirent là jusqu’à ce jour.