< 1 Tarihi 4 >

1 Zuriyoyin Yahuda su ne, Ferez, Hezron, Karmi, Hur da Shobal.
Descendants de Juda: Héçron, Karmi, Hour et Chobal.
2 Reyahiya ɗan Shobal shi ne mahaifin Yahat, Yahat shi ne mahaifin Ahumai da Lahad. Waɗannan su ne gidajen Zoratiyawa.
Reaïa, fils de Chobal, engendra Yahat; celui-ci, Ahoumaï et Lahad. Telles étaient les familles des Çoratiens.
3 Waɗannan su ne’ya’yan Etam. Yezireyel, Ishma da Idbash.’Yar’uwarsu ita ce Hazzelelfoni.
Ceux-ci fondèrent Etham, Jezreël, Yichma et Yidbach; leur sœur s’appelait Hacelélponi.
4 Fenuwel shi ne mahaifin Gedor, kuma Ezer shi ne mahaifin Husha. Waɗannan su ne zuriyar Hur, ɗan farin Efrata da mahaifin Betlehem.
Penouêl fut le père de Ghedor, Ezer, de Houcha. Tels furent les descendants de Hour, le premier-né d’Ephrata, le père de Bethléem.
5 Asshur mahaifin Tekowa yana da mata biyu, Hela da Na’ara.
Achhour, père de Tekoa, eut deux femmes: Hélea et Naara.
6 Na’ara ta haifi Ahuzzam, Hefer, Temeni da Hawahashtari. Waɗannan su ne zuriyar Na’ara.
Naara lui enfanta Ahouzzam, Héfer, Tèmeni et l’Ahachtarien. Tels furent les fils de Naara.
7 ’Ya’yan Hela maza su ne, Zeret, Zohar, Etnan,
Ceux de Hélea furent: Céreth, Çohar et Etnân.
8 da Koz. Koz ne mahaifin Anub da Hazzobeba, shi ne kuma kakan iyalin da suka fito daga zuriyar Aharhel ɗan Harum.
Koç engendra Anoub, Haçobêba, et les familles d’Aharhêl, fils de Haroum…
9 Yabez ya fi’yan’uwansa martaba. Mahaifiyarsa ta sa masa suna Yabez, tana cewa, “Na haife shi da azaba.”
Yabêç était le plus considéré de ses frères. C’Était sa mère qui lui avait donné le nom de Yabêç, en disant: "Certes, j’ai enfanté avec douleur."
10 Yabez ya yi kuka ga Allah na Isra’ila ya ce, “Ka yi mini albarka ka fadada yankina! Bari hannunka yă kasance tare da ni, yă kuma kiyaye ni daga abin da zai cuce ni, don kada in shiga wahala.” Sai Allah ya ji roƙonsa.
Yabêç adressa au Dieu d’Israël cette supplique: "Si tu daignes me bénir, accroître mon territoire, et que ta main soit avec moi, que tu me gardes du mal pour m’éviter la douleur…" Et Dieu lui accorda ce qu’il avait demandé.
11 Kelub, ɗan’uwan Shuha, shi ne mahaifin Mehir, wanda shi ne mahaifin Eshton.
Keloub, frère de Chouha, engendra Mehir, qui fut le père d’Echtôn.
12 Eshton shi ne mahaifin Bet-Rafa, Faseya da Tehinna wanda ya haifi Ir Nahash. Waɗannan su ne mutanen Reka.
Echtôn engendra Beth-Rafa, Passéêah et Tehinna, le père de la ville de Nahach. C’Étaient là les gens de Rêkha.
13 ’Ya’yan Kenaz maza su ne, Otniyel da Serahiya.’Ya’yan Otniyel maza su ne, Hatat da Meyonotai.
Kenaz eut pour fils Othoniel et Seraïa. Les fils d’Othoniel furent Hatath…
14 Meyonotai shi ne mahaifin Ofra. Serahiya shi ne mahaifin Yowab, mahaifin Ge-Harashim. An kira shi haka domin mutanensa masu sana’ar hannu ne.
Meonotaï engendra Ofra, et Seraïa Joab, le père de la "Vallée des Artisans", car c’étaient des artisans.
15 ’Ya’yan Kaleb ɗan Yefunne maza su ne, Iru, Ela da Na’am. Ɗan Ela shi ne, Kenaz.
Les fils de Caleb, fils de Yefounné, furent: Irou, Ela et Naam; les fils d’Ela… et Kenaz.
16 ’Ya’yan Yahallelel su ne, Zif, Zifa, Tiriya da Asarel.
Les fils de Yehallèlêl: Zif, Zifa, Tiria et Assarêl.
17 ’Ya’yan Ezra maza su ne, Yeter, Mered, Efer da Yalon. Ɗaya daga cikin matan Mered ta haifi Miriyam, Shammai da Ishba wanda ya haifi Eshtemowa.
Le s fils d’Ezra: Yeter, Méred, Efer et Yalôn. Et elle conçut et enfanta Miriam, Chammaï et Yichbah, père d’Echtemoa.
18 (Matarsa mutuniyar Yahuda kuwa ta haifi Yared mahaifin Gedor, Heber mahaifin Soko, da kuma Yekutiyel mahaifin Zanowa.) Waɗannan su ne’ya’yan Bitiya’yar Fir’auna, wadda Mered ya aura.
Sa femme, la Judéenne, enfanta Yéred, père de Ghedor, Héber, père de Sokho, Yekoutiël, père de Zanoah. Ceux-là, furent les enfants de Bitia, fille de Pharaon, qu’avait épousée Méred.
19 ’Ya’yan matar Hodiya,’yar’uwar Naham su ne, suka haifi Keyila Bagarme, da Eshtemowa mutumin Ma’aka.
Les fils de la femme de Hodia, sœur de Naham, furent le "père" de Keïla, le Garmien, et d’Echtemoa, le Maakhatien.
20 ’Ya’yan Shimon maza su ne, Amnon, Rinna, Ben-Hanan da Tilon. Zuriyar Ishi su ne, Zohet da Ben-Zohet.
Les fils de Chimôn furent Amnôn et Rinna, Ben-Hanân et Tilôn; les fils de Yichi: Zohêth et Ben-Zohéth.
21 ’Ya’yan Shela ɗan Yahuda maza su ne, Er mahaifin Leka, La’ada mahaifin Maresha da kuma gidajen masu aikin lilin a Bet-Ashbeya,
Les fils de Chêla, fils de Juda, furent Er, "père" de Lêkha, Lada, "père" de Marêcha, et les familles de la maison du travail de byssus, de la maison d’Achbêa;
22 da Yokim, mutanen Kozeba, da Yowash da Saraf wanda ya yi mulkin Mowab da kuma Yashubi Lehem (Waɗannan rubutattun tarihi ne na tun dā.)
en outre, Yokim, les gens de Kozêba, Yoach et Saraf, qui dominèrent sur Moab, et Yachoubi-Léhem. Ce sont là choses anciennes.
23 Su ne maginan tukwane waɗanda suka zauna a Netayim da Gedera; sun zauna a can suka kuma yi wa sarki aiki.
C’Étaient les potiers et les habitants des plantations et des parcs. Ils y demeuraient pour être plus près du roi en vue de son service.
24 Zuriyar Simeyon su ne, Nemuwel, Yamin, Yarib, Zera da Shawulu;
Les fils de Siméon furent: Nemouêl, Yamîn, Yarib, Zérah, Chaoul.
25 Shawulu ya haifi Shallum, Shallum ya haifi Mibsam. Mibsam ya haifi Mishma.
Celui-ci eut pour fils Challoum, celui-ci Mibsam, celui-ci Michma.
26 Zuriyar Mishma su ne, Hammuwel ɗansa, wanda ya haifi Zakkur, shi Zakkur kuma ya haifi Shimeyi.
Les descendants de Michma furent Hammouêl, qui eut pour fils Zakkour, celui-ci Chimeï.
27 Shimeyi yana da’ya’ya maza goma sha shida da’ya’ya mata shida, amma’yan’uwansa ba su da’ya’ya da yawa; saboda haka gidansu gaba ɗaya ba tă zama mai mutane da yawa kamar mutanen Yahuda ba.
Chimeï eut seize fils et six filles, tandis que ses frères n’eurent pas beaucoup d’enfants; toutes leurs familles n’atteignirent pas le nombre des descendants de Juda.
28 Sun zauna a Beyersheba, Molada, Hazar Shuwal,
Ils habitèrent Bersabée, Molada, Haçar-Choual,
29 Bilha, Ezem, Tolad
Bilha, Ecem, Tolad,
30 Betuwel, Horma, Ziklag,
Betouêl, Horma, Ciklag,
31 Bet-Markabot, Hazar-Susim, Bet-Biri da Sha’arayim. Waɗannan su ne garuruwansu har lokacin mulkin Dawuda.
Beth-Marcabot, Haçar-Soussim, Beth-Bireï et Chaaraïm. Telles furent leurs villes jusqu’à l’avènement de David.
32 Ƙauyukan da suke kewayensu su ne Etam, Ayin, Rimmon, Token da Ashan, garuruwa biyar;
Ils eurent pour dépendances Etam, Ayîn, Rimmôn, Tokhén et Achàn, soit cinq villes,
33 da kuma dukan ƙauyuka kewaye da waɗannan garuruwa har zuwa Ba’al. Waɗannan ne wuraren zamansu. Suka kuma ajiye tarihin zuriya.
et toutes les campagnes, aux environs de ces villes, jusqu’à Baal. Telles furent leurs résidences et leur filiation par familles.
34 Zuriyar Simeyon ta ƙunshi Meshobab, da Yamlek, da Yosha ɗan Amaziya.
Quand à Mechobab, Yamlêkh, Yocha, fils d’Amacia,
35 Akwai Yowel, da Yehu ɗan Yoshibiya. Yoshibiya ɗan Seraya ne. Serahiya kuma ɗan Asiyel ne.
Joël, Yêhou, fils de Yochibia, fils de Seraïa, fils d’Assiël,
36 Akwai Eliyohenai da Ya’akoba, da Yeshohahiya, da Asahiya, da Adiyel, da Yesimiyel, da Benahiya.
Elyoênaï, Yaakoba, Yechohaïa, Assaïa, Adiêl, Yessimiêl, Benaïa,
37 Akwai Ziza ɗan Shifi. Shifi ɗan Allon ne. Allon ɗan Yedahiya ne. Yedahiya ɗan Shimri ne. Shimri kuma ɗan Shemahiya ne.
et Ziza, fils de Chifeï, fils d’Allôn, fils de Yedaïa, fils de Chimri, fils de Chemaïa,
38 Mutanen da aka jera sunayensu a bisa, shugabannin gidajensu ne. Iyalansu sun ƙaru sosai,
ceux-là, qui sont désignés nominativement, et qui étaient princes dans leurs familles, leurs lignées paternelles débordèrent beaucoup
39 suka tafi bayan garin Gedor wajajen gabashin kwari suna neman makiyaya domin garkunansu.
et allèrent jusqu’à l’entrée de Ghedor, à l’est de la vallée, afin d’y chercher des pâturages pour leurs troupeaux.
40 Suka sami makiyaya mai ciyawa mai kyau, ƙasar kuma tana da fāɗi, da salama, kuma zaman lafiya. A dā waɗansu mutanen Ham sun zauna a can.
Ils y trouvèrent des pâturages gras et bons et un pays vaste, tranquille et pacifique, car ceux qui y habitaient auparavant étaient des descendants de Cham.
41 Mutanen da aka jera sunayensu sun zo ne a zamanin Hezekiya sarkin Yahuda. Suka yaƙi mutanen Ham a wuraren zamansu, haka kuma suka yi da Meyunawa da suke can, suka hallaka su ƙaƙaf, yadda yake har yă zuwa yau. Sa’an nan suka zauna a wurin, gama akwai makiyaya domin garkunansu.
Ceux donc qui ont été désignés par leurs noms vinrent à l’époque d’Ezéchias, roi de Juda; ils détruisirent leurs tentes et les habitations qui s’y trouvaient et ils les vouèrent à l’interdit, ce qui se voit encore aujourd’hui; puis ils s’y établirent à leur place, car ils avaient là des pâturages pour leurs troupeaux.
42 Mutum ɗari biyar na waɗannan mutane Simeyon, waɗanda Felatiya, Neyariya, Refahiya da Uzziyel,’ya’yan Ishi maza suka jagorance, sun mamaye ƙasar tudu ta Seyir.
D’Entre eux, c’est-à-dire des descendants de Siméon, cinq cents hommes allèrent se fixer sur la montagne de Séïr. Ils avaient à leur tête Pelatia, Nearia, Refaïa et Ouzziël, fils de Yicheï.
43 Suka karkashe raguwar Amalekawan da suka tsere, suka kuma zauna a can har yă zuwa yau.
Ils exterminèrent le reste des survivants d’Amalec, et ils habitent là encore aujourd’hui.

< 1 Tarihi 4 >