< 1 Tarihi 4 >

1 Zuriyoyin Yahuda su ne, Ferez, Hezron, Karmi, Hur da Shobal.
Judah's descendants were Perez, Hezron, Karmi, Hur, and Shobal.
2 Reyahiya ɗan Shobal shi ne mahaifin Yahat, Yahat shi ne mahaifin Ahumai da Lahad. Waɗannan su ne gidajen Zoratiyawa.
Shobal was the father of Reaiah. Reaiah was the father of Jahath. Jahath was the father of Ahumai and Lahad. These were of the clans of the Zorathites.
3 Waɗannan su ne’ya’yan Etam. Yezireyel, Ishma da Idbash.’Yar’uwarsu ita ce Hazzelelfoni.
These were the ancestors of the clans in the city of Etam: Jezreel, Ishma, and Idbash. Their sister's name was Hazzelelponi.
4 Fenuwel shi ne mahaifin Gedor, kuma Ezer shi ne mahaifin Husha. Waɗannan su ne zuriyar Hur, ɗan farin Efrata da mahaifin Betlehem.
Peniel was the ancestor of the clans in the city of Gedor. Ezer was the originator of the clans in Hushah. These were descendants of Hur, the firstborn of Ephrathah and the originator of Bethlehem.
5 Asshur mahaifin Tekowa yana da mata biyu, Hela da Na’ara.
Ashhur the father of Tekoa had two wives, Helah and Naarah.
6 Na’ara ta haifi Ahuzzam, Hefer, Temeni da Hawahashtari. Waɗannan su ne zuriyar Na’ara.
Naarah bore him Ahuzzam, Hepher, Temeni, and Haahashtari. These were Naarah's sons.
7 ’Ya’yan Hela maza su ne, Zeret, Zohar, Etnan,
Helah's sons were Zereth, Zohar, Ethnan,
8 da Koz. Koz ne mahaifin Anub da Hazzobeba, shi ne kuma kakan iyalin da suka fito daga zuriyar Aharhel ɗan Harum.
and Koz, who became the father of Anub and Hazzobebah, and of the clans descended from Aharhel son of Harum.
9 Yabez ya fi’yan’uwansa martaba. Mahaifiyarsa ta sa masa suna Yabez, tana cewa, “Na haife shi da azaba.”
Jabez was more respected than his brothers. His mother called him Jabez. She said, “Because I bore him in pain.”
10 Yabez ya yi kuka ga Allah na Isra’ila ya ce, “Ka yi mini albarka ka fadada yankina! Bari hannunka yă kasance tare da ni, yă kuma kiyaye ni daga abin da zai cuce ni, don kada in shiga wahala.” Sai Allah ya ji roƙonsa.
Jabez called out to the God of Israel and said, “If only you would truly bless me, expand my territory, and your hand will be with me. When you do this you will keep me from harm, so that I may be free from pain!” So God granted him his prayer.
11 Kelub, ɗan’uwan Shuha, shi ne mahaifin Mehir, wanda shi ne mahaifin Eshton.
Kelub brother of Shuhah became the father of Mehir, who was the father of Eshton.
12 Eshton shi ne mahaifin Bet-Rafa, Faseya da Tehinna wanda ya haifi Ir Nahash. Waɗannan su ne mutanen Reka.
Eshton became the father of Beth Rapha, Paseah, and Tehinnah, the father of Ir Nahash. These were men who lived in Rekah.
13 ’Ya’yan Kenaz maza su ne, Otniyel da Serahiya.’Ya’yan Otniyel maza su ne, Hatat da Meyonotai.
Kenaz's sons were Othniel and Seraiah. Othniel's sons were Hathath and Meonothai.
14 Meyonotai shi ne mahaifin Ofra. Serahiya shi ne mahaifin Yowab, mahaifin Ge-Harashim. An kira shi haka domin mutanensa masu sana’ar hannu ne.
Meonothai became the father of Ophrah, and Seraiah became the father of Joab, the originator of Ge-Harashim, whose people were craftsmen.
15 ’Ya’yan Kaleb ɗan Yefunne maza su ne, Iru, Ela da Na’am. Ɗan Ela shi ne, Kenaz.
The sons of Caleb son of Jephunneh were Iru, Elah and Naam. Elah's son was Kenaz.
16 ’Ya’yan Yahallelel su ne, Zif, Zifa, Tiriya da Asarel.
Jehallelel's sons were Ziph, Ziphah, Tiria, and Asarel.
17 ’Ya’yan Ezra maza su ne, Yeter, Mered, Efer da Yalon. Ɗaya daga cikin matan Mered ta haifi Miriyam, Shammai da Ishba wanda ya haifi Eshtemowa.
Ezrah's sons were Jether, Mered, Epher, and Jalon. Mered's Egyptian wife bore Miriam, Shammai, and Ishbah, who became the father of Eshtemoa.
18 (Matarsa mutuniyar Yahuda kuwa ta haifi Yared mahaifin Gedor, Heber mahaifin Soko, da kuma Yekutiyel mahaifin Zanowa.) Waɗannan su ne’ya’yan Bitiya’yar Fir’auna, wadda Mered ya aura.
These were the sons of Bithiah, daughter of Pharaoh, whom Mered married. Mered's Judahite wife bore Jered, who became the father of Gedor; Heber, who became the father of Soko; and Jekuthiel, who became the father of Zanoah.
19 ’Ya’yan matar Hodiya,’yar’uwar Naham su ne, suka haifi Keyila Bagarme, da Eshtemowa mutumin Ma’aka.
Of the two sons of Hodiah's wife, sister of Naham, one became the father of Keilah the Garmite. The other was Eshtemoa the Maakathite.
20 ’Ya’yan Shimon maza su ne, Amnon, Rinna, Ben-Hanan da Tilon. Zuriyar Ishi su ne, Zohet da Ben-Zohet.
The sons of Shimon were Amnon, Rinnah, Ben-Hanan, and Tilon. The sons of Ishi were Zoheth and Ben-Zoheth.
21 ’Ya’yan Shela ɗan Yahuda maza su ne, Er mahaifin Leka, La’ada mahaifin Maresha da kuma gidajen masu aikin lilin a Bet-Ashbeya,
The descendants of Shelah son of Judah, were Er father of Lekah, Laadah father of Mareshah and the clans of the linen workers at Beth Ashbea,
22 da Yokim, mutanen Kozeba, da Yowash da Saraf wanda ya yi mulkin Mowab da kuma Yashubi Lehem (Waɗannan rubutattun tarihi ne na tun dā.)
Jokim, the men of Kozeba, and Joash and Saraph, who ruled in Moab and Jashubi Lehem. (This information is from ancient records.)
23 Su ne maginan tukwane waɗanda suka zauna a Netayim da Gedera; sun zauna a can suka kuma yi wa sarki aiki.
These were the potters who lived in Netaim and Gederah and worked for the king.
24 Zuriyar Simeyon su ne, Nemuwel, Yamin, Yarib, Zera da Shawulu;
Simeon's descendants were Nemuel, Jamin, Jarib, Zerah, and Shaul.
25 Shawulu ya haifi Shallum, Shallum ya haifi Mibsam. Mibsam ya haifi Mishma.
Shallum was Shaul's son, Mibsam was Shallum's son, and Mishma was Mibsam's son.
26 Zuriyar Mishma su ne, Hammuwel ɗansa, wanda ya haifi Zakkur, shi Zakkur kuma ya haifi Shimeyi.
Mishma's descendants were Hammuel his son, Zakkur his grandson, and Shimei his great-grandson.
27 Shimeyi yana da’ya’ya maza goma sha shida da’ya’ya mata shida, amma’yan’uwansa ba su da’ya’ya da yawa; saboda haka gidansu gaba ɗaya ba tă zama mai mutane da yawa kamar mutanen Yahuda ba.
Shimei had sixteen sons and six daughters. His brothers did not have many children, so their clans did not increase greatly in numbers as the people of Judah did.
28 Sun zauna a Beyersheba, Molada, Hazar Shuwal,
They lived at Beersheba, Moladah, and at Hazar Shual.
29 Bilha, Ezem, Tolad
They also live at Bilhah, Ezem, Tolad,
30 Betuwel, Horma, Ziklag,
Bethuel, Hormah, Ziklag,
31 Bet-Markabot, Hazar-Susim, Bet-Biri da Sha’arayim. Waɗannan su ne garuruwansu har lokacin mulkin Dawuda.
Beth Markaboth, Hazar Susim, Beth Biri, and Shaaraim. These were their cities until the reign of David.
32 Ƙauyukan da suke kewayensu su ne Etam, Ayin, Rimmon, Token da Ashan, garuruwa biyar;
Their five villages were Etam, Ain, Rimmon, Token, and Ashan,
33 da kuma dukan ƙauyuka kewaye da waɗannan garuruwa har zuwa Ba’al. Waɗannan ne wuraren zamansu. Suka kuma ajiye tarihin zuriya.
together with the outlying villages as far as Baalath. These were their settlements, and they kept the genealogical records.
34 Zuriyar Simeyon ta ƙunshi Meshobab, da Yamlek, da Yosha ɗan Amaziya.
Clan leaders were Meshobab, Jamlech, Joshah son of Amaziah,
35 Akwai Yowel, da Yehu ɗan Yoshibiya. Yoshibiya ɗan Seraya ne. Serahiya kuma ɗan Asiyel ne.
Joel, Jehu son of Joshibiah son of Seraiah son of Asiel,
36 Akwai Eliyohenai da Ya’akoba, da Yeshohahiya, da Asahiya, da Adiyel, da Yesimiyel, da Benahiya.
Elioenai, Jaakobah, Jeshohaiah, Asaiah, Adiel, Jesimiel, Benaiah,
37 Akwai Ziza ɗan Shifi. Shifi ɗan Allon ne. Allon ɗan Yedahiya ne. Yedahiya ɗan Shimri ne. Shimri kuma ɗan Shemahiya ne.
and Ziza son of Shiphi son of Allon son of Jedaiah son of Shimri son of Shemaiah.
38 Mutanen da aka jera sunayensu a bisa, shugabannin gidajensu ne. Iyalansu sun ƙaru sosai,
These mentioned by name were leaders in their clans, and their clans increased greatly.
39 suka tafi bayan garin Gedor wajajen gabashin kwari suna neman makiyaya domin garkunansu.
They went near Gedor, on the east side of the valley, to seek pasture for their flocks.
40 Suka sami makiyaya mai ciyawa mai kyau, ƙasar kuma tana da fāɗi, da salama, kuma zaman lafiya. A dā waɗansu mutanen Ham sun zauna a can.
They found abundant and good pasture. The land was broad, quiet, and peaceable. The Hamites had formerly lived there.
41 Mutanen da aka jera sunayensu sun zo ne a zamanin Hezekiya sarkin Yahuda. Suka yaƙi mutanen Ham a wuraren zamansu, haka kuma suka yi da Meyunawa da suke can, suka hallaka su ƙaƙaf, yadda yake har yă zuwa yau. Sa’an nan suka zauna a wurin, gama akwai makiyaya domin garkunansu.
These just listed by name came in the days of Hezekiah king of Judah, and attacked the Hamite settlements and the Meunites, who were there also. They destroyed them completely and lived there because they found pasture for their flocks.
42 Mutum ɗari biyar na waɗannan mutane Simeyon, waɗanda Felatiya, Neyariya, Refahiya da Uzziyel,’ya’yan Ishi maza suka jagorance, sun mamaye ƙasar tudu ta Seyir.
From them, from the sons of Simeon, five hundred men went to Mount Seir with Pelatiah, Neariah, Rephaiah, and Uzziel, the sons of Ishi, as their leader.
43 Suka karkashe raguwar Amalekawan da suka tsere, suka kuma zauna a can har yă zuwa yau.
They defeated the rest of the Amalekite refugees, and have lived there to this day.

< 1 Tarihi 4 >