< 1 Tarihi 4 >

1 Zuriyoyin Yahuda su ne, Ferez, Hezron, Karmi, Hur da Shobal.
The sons of Juda: Phares, Hesron, and Charmi, and Hur, and Sobal.
2 Reyahiya ɗan Shobal shi ne mahaifin Yahat, Yahat shi ne mahaifin Ahumai da Lahad. Waɗannan su ne gidajen Zoratiyawa.
And Raia the son of Sobal beget Jahath, of whom were born Ahumai, and Laad. These are the families of Sarathi.
3 Waɗannan su ne’ya’yan Etam. Yezireyel, Ishma da Idbash.’Yar’uwarsu ita ce Hazzelelfoni.
And this is the posterity of Etam: Jezrahel, and Jesema, and Jedebos: and the name of their sister was Asalelphuni.
4 Fenuwel shi ne mahaifin Gedor, kuma Ezer shi ne mahaifin Husha. Waɗannan su ne zuriyar Hur, ɗan farin Efrata da mahaifin Betlehem.
And Phanuel the father of Gedor, and Ezar the father of Hosa, these are the sons of Hur the firstborn of Ephratha the father of Bethlehem.
5 Asshur mahaifin Tekowa yana da mata biyu, Hela da Na’ara.
And Assur the father of Thecua had two wives, Halaa and Naara:
6 Na’ara ta haifi Ahuzzam, Hefer, Temeni da Hawahashtari. Waɗannan su ne zuriyar Na’ara.
And Naara bore him Ozam, and Hepher, and Themani, and Ahasthari: these are the sons of Naara.
7 ’Ya’yan Hela maza su ne, Zeret, Zohar, Etnan,
And the sons of Halaa, Sereth, Isaar, and Ethnan.
8 da Koz. Koz ne mahaifin Anub da Hazzobeba, shi ne kuma kakan iyalin da suka fito daga zuriyar Aharhel ɗan Harum.
And Cos begot Anob, and Soboba, the kindred of Aharehel the son of Arum.
9 Yabez ya fi’yan’uwansa martaba. Mahaifiyarsa ta sa masa suna Yabez, tana cewa, “Na haife shi da azaba.”
And Jabes was more honourable than any of his brethren, and his mother called his name Jabes, saying: Because I bore him with sorrow.
10 Yabez ya yi kuka ga Allah na Isra’ila ya ce, “Ka yi mini albarka ka fadada yankina! Bari hannunka yă kasance tare da ni, yă kuma kiyaye ni daga abin da zai cuce ni, don kada in shiga wahala.” Sai Allah ya ji roƙonsa.
And Jabes called upon the God of Israel, saying: If blessing thou wilt bless me, and wilt enlarge my borders, and thy hand be with me, and thou save me from being oppressed by evil. And God granted him the things he prayed for.
11 Kelub, ɗan’uwan Shuha, shi ne mahaifin Mehir, wanda shi ne mahaifin Eshton.
And Caleb the brother of Sua beget Mahir, who was the father of Esthon.
12 Eshton shi ne mahaifin Bet-Rafa, Faseya da Tehinna wanda ya haifi Ir Nahash. Waɗannan su ne mutanen Reka.
And Esthon beget Bethrapha, and Phesse, and Tehinna father of the city of Naas: these are the men of Recha.
13 ’Ya’yan Kenaz maza su ne, Otniyel da Serahiya.’Ya’yan Otniyel maza su ne, Hatat da Meyonotai.
And the sons of Cenez were Othoniel, and Saraia. And the sons of Othoniel, Hathath, and Maonathi.
14 Meyonotai shi ne mahaifin Ofra. Serahiya shi ne mahaifin Yowab, mahaifin Ge-Harashim. An kira shi haka domin mutanensa masu sana’ar hannu ne.
Maonathi beget Ophra, and Saraia begot Joab the father of the Valley of artificers: for artificers were there.
15 ’Ya’yan Kaleb ɗan Yefunne maza su ne, Iru, Ela da Na’am. Ɗan Ela shi ne, Kenaz.
And the sons of Caleb the son of Jephone, were Hir, and Ela, and Naham. And the sons of Ela: Cenez.
16 ’Ya’yan Yahallelel su ne, Zif, Zifa, Tiriya da Asarel.
The sons also of Jaleleel: Ziph, and Zipha, Thiria, and Asrael.
17 ’Ya’yan Ezra maza su ne, Yeter, Mered, Efer da Yalon. Ɗaya daga cikin matan Mered ta haifi Miriyam, Shammai da Ishba wanda ya haifi Eshtemowa.
And the sons of Esra, Jether, and Mered, and Epher, and Jalon, and he beget Mariam, and Sammai, and Jesba the father of Esthamo.
18 (Matarsa mutuniyar Yahuda kuwa ta haifi Yared mahaifin Gedor, Heber mahaifin Soko, da kuma Yekutiyel mahaifin Zanowa.) Waɗannan su ne’ya’yan Bitiya’yar Fir’auna, wadda Mered ya aura.
And his wife Judaia, bore Jared the father of Gedor, and Heber the father of Socho, and Icuthiel the father of Zanoe. And these are the sons of Bethia the daughter of Pharao, whom Mered took to wife.
19 ’Ya’yan matar Hodiya,’yar’uwar Naham su ne, suka haifi Keyila Bagarme, da Eshtemowa mutumin Ma’aka.
And the sons of his wife Odaia the sister of Naham the father of Celia, Garmi, and Esthamo, who was of Machathi.
20 ’Ya’yan Shimon maza su ne, Amnon, Rinna, Ben-Hanan da Tilon. Zuriyar Ishi su ne, Zohet da Ben-Zohet.
The sons also of Simon, Amnon, and Rinna the son of Hanan, and Thilon. And the sons of Jesi Zoheth, and Benzoheth.
21 ’Ya’yan Shela ɗan Yahuda maza su ne, Er mahaifin Leka, La’ada mahaifin Maresha da kuma gidajen masu aikin lilin a Bet-Ashbeya,
The sons of Sela the son of Juda: Her the father of Lecha, and Laada the father of Maresa, and the families of the house of them that wrought fine linen in the House of oath.
22 da Yokim, mutanen Kozeba, da Yowash da Saraf wanda ya yi mulkin Mowab da kuma Yashubi Lehem (Waɗannan rubutattun tarihi ne na tun dā.)
And he that made the sun to stand, and the men of Lying, and Secure, and Burning, who were princes in Moab, and who returned into Lahem. Now these are things of old.
23 Su ne maginan tukwane waɗanda suka zauna a Netayim da Gedera; sun zauna a can suka kuma yi wa sarki aiki.
These are the potters, and they dwelt in Plantations, and Hedges, with the king for his works, and they abode there.
24 Zuriyar Simeyon su ne, Nemuwel, Yamin, Yarib, Zera da Shawulu;
The sons of Simeon: Namuel, and Jamin, Jarib, Zara, Saul:
25 Shawulu ya haifi Shallum, Shallum ya haifi Mibsam. Mibsam ya haifi Mishma.
Sellum his son, Mapsam his son, Masma his son.
26 Zuriyar Mishma su ne, Hammuwel ɗansa, wanda ya haifi Zakkur, shi Zakkur kuma ya haifi Shimeyi.
The sons of Masma: Hamuel his son, Zachur his son, Semei his son.
27 Shimeyi yana da’ya’ya maza goma sha shida da’ya’ya mata shida, amma’yan’uwansa ba su da’ya’ya da yawa; saboda haka gidansu gaba ɗaya ba tă zama mai mutane da yawa kamar mutanen Yahuda ba.
The sons of Semei were sixteen, and six daughters: but his brethren had not many sons, and the whole kindred could not reach to the sum of the children of Juda.
28 Sun zauna a Beyersheba, Molada, Hazar Shuwal,
And they dwelt in Bersabee, and Molada, and Hasarsuhal,
29 Bilha, Ezem, Tolad
And in Bala, and in Asom, and in Tholad,
30 Betuwel, Horma, Ziklag,
And in Bathuel, and in Horma, and in Siceleg,
31 Bet-Markabot, Hazar-Susim, Bet-Biri da Sha’arayim. Waɗannan su ne garuruwansu har lokacin mulkin Dawuda.
And in Bethmarchaboth, and in Hasarsusim, and in Bethberai, and in Saarim. These were their cities unto the reign of David.
32 Ƙauyukan da suke kewayensu su ne Etam, Ayin, Rimmon, Token da Ashan, garuruwa biyar;
Their towns also were Etam, and Aen, Remmon, and Thochen, and Asan, five cities.
33 da kuma dukan ƙauyuka kewaye da waɗannan garuruwa har zuwa Ba’al. Waɗannan ne wuraren zamansu. Suka kuma ajiye tarihin zuriya.
And all their villages round about these cities as far as Baal. This was their habitation, and the distribution of their dwellings.
34 Zuriyar Simeyon ta ƙunshi Meshobab, da Yamlek, da Yosha ɗan Amaziya.
And Mosabab and Jemlech, and Josa, the son of Amasias,
35 Akwai Yowel, da Yehu ɗan Yoshibiya. Yoshibiya ɗan Seraya ne. Serahiya kuma ɗan Asiyel ne.
And Joel, and Jehu the son of Josabia the son of Saraia, the son of Asiel,
36 Akwai Eliyohenai da Ya’akoba, da Yeshohahiya, da Asahiya, da Adiyel, da Yesimiyel, da Benahiya.
And Elioenai, and Jacoba, and Isuhaia, and Asaia, and Adiel, and Ismiel, and Banaia,
37 Akwai Ziza ɗan Shifi. Shifi ɗan Allon ne. Allon ɗan Yedahiya ne. Yedahiya ɗan Shimri ne. Shimri kuma ɗan Shemahiya ne.
Ziza also the son of Sephei the son of Allon the son of Idaia the son of Semri the son of Samaia.
38 Mutanen da aka jera sunayensu a bisa, shugabannin gidajensu ne. Iyalansu sun ƙaru sosai,
These were named princes in their kindreds, and in the houses of their families were multiplied exceedingly.
39 suka tafi bayan garin Gedor wajajen gabashin kwari suna neman makiyaya domin garkunansu.
And they went forth to enter into Gador as far as to the east side of the valley, to seek pastures for their flocks.
40 Suka sami makiyaya mai ciyawa mai kyau, ƙasar kuma tana da fāɗi, da salama, kuma zaman lafiya. A dā waɗansu mutanen Ham sun zauna a can.
And they found fat pastures, and very good, and a country spacious, and quiet, and fruitful, in which some of the race of Cham had dwelt before.
41 Mutanen da aka jera sunayensu sun zo ne a zamanin Hezekiya sarkin Yahuda. Suka yaƙi mutanen Ham a wuraren zamansu, haka kuma suka yi da Meyunawa da suke can, suka hallaka su ƙaƙaf, yadda yake har yă zuwa yau. Sa’an nan suka zauna a wurin, gama akwai makiyaya domin garkunansu.
And these whose names are written above, came in the days of Ezechias king of Juda: and they beat down their tents, and slew the inhabitants that were found there, and utterly destroyed them unto this day: and they dwelt in their place, because they found there fat pastures.
42 Mutum ɗari biyar na waɗannan mutane Simeyon, waɗanda Felatiya, Neyariya, Refahiya da Uzziyel,’ya’yan Ishi maza suka jagorance, sun mamaye ƙasar tudu ta Seyir.
Some also of the children of Simeon, five hundred men, went into mount Seir, having for their captains Phaltias and Naaria and Raphaia and Oziel the sons of Jesi:
43 Suka karkashe raguwar Amalekawan da suka tsere, suka kuma zauna a can har yă zuwa yau.
And they slew the remnant of the Amalecites, who had been able to escape, and they dwelt there in their stead unto this day.

< 1 Tarihi 4 >