< 1 Tarihi 29 >

1 Sa’an nan Sarki Dawuda ya ce wa dukan taron, “Ɗana Solomon, wanda Allah ya zaɓa, matashi ne, kuma bai gogu ba. Aikin yana da yawa, domin wannan ƙasaitaccen ginin ba na mutum ba ne, na Ubangiji Allah ne.
Puis le Roi David dit à toute l'assemblée: Dieu a choisi un seul de mes fils, [savoir] Salomon, qui est encore jeune et délicat, et l'ouvrage est grand; car ce palais n'est point pour un homme, mais pour l'Eternel Dieu.
2 Na riga na tara dukan kayayyakin da na tanada saboda haikalin Allahna, zinariya saboda dukan ayyukan zinariya, azurfa saboda ayyukan azurfa, tagulla saboda ayyukan tagulla, ƙarfe saboda ayyukan ƙarfe da kuma katako saboda ayyukan katako, da onis don ado, turkuwoyis, duwatsu masu launi dabam-dabam, da kuma dukan duwatsu masu kyau da mabul, dukan waɗannan suna nan jingim.
Et moi, j'ai préparé de toutes mes forces pour la maison de mon Dieu, de l'or pour les choses [qui doivent être] d'or, de l'argent pour celles [qui doivent être] d'argent; de l'airain pour celles d'airain, du fer pour celles de fer, du bois pour celles de bois, des pierres d'onyx, et [des pierres] pour être enchâssées, des pierres d'escarboucle, et [des pierres] de diverses couleurs; des pierres précieuses de toutes sortes, et du marbre en abondance.
3 Ban da haka ma, cikin sa zuciyata ga haikalin Allahna, yanzu na ba da ma’ajina na zinariya da azurfa saboda haikalin Allahna, fiye da kome na tanada saboda wannan haikali,
Et outre cela, parce que j'ai une grande affection pour la maison de mon Dieu, je donne pour la maison de mon Dieu, outre toutes les choses que j'ai préparées pour la maison du Sanctuaire, l'or et l'argent que j'ai entre mes plus précieux joyaux;
4 talenti dubu uku na zinariya (zinariyar Ofir) da tacecciyar azurfa dubu bakwai; don adon bangon gine-ginen,
[Savoir], trois mille talents d'or, de l'or d'Ophir, et sept mille talents d'argent affiné, pour revêtir les murailles de la maison.
5 don aikin zinariya da kuma aikin azurfa, don kuma dukan aikin da gwanaye za su yi. Yanzu fa wa yake da niyya yă miƙa kansa a yau don Ubangiji?”
Afin qu'il y ait de l'or partout où il faut de l'or, et de l'argent partout où il faut de l'argent; et pour tout l'ouvrage [qui se fera] par main d'ouvriers. Or qui est celui d'entre vous qui se disposera volontairement à offrir aujourd'hui libéralement à l'Eternel?
6 Sai shugabannin iyalai, shugabannin kabilan Isra’ila, manyan hafsoshin mayaƙa dubu-dubu da manyan hafsoshi mayaƙa ɗari-ɗari, da shugabannin lura da ayyukan sarki suka yi bayarwa da yardar rai.
Alors les Chefs des pères, et les Chefs des Tribus d'Israël, et les Gouverneurs de milliers et de centaines, et ceux qui avaient la charge des affaires du Roi offrirent volontairement.
7 Suka bayar talenti dubu biyar na zinariya, talenti dubu goma na azurfa, talenti dubu goma sha takwas na tagulla da talenti dubu ɗari na ƙarfe don aiki a haikalin Allah.
Et ils donnèrent pour le service de la maison de Dieu cinq mille talents et dix mille drachmes d'or, dix mille talents d'argent, dix-huit mille talents d'airain, et cent mille talents de fer.
8 Duk waɗanda suke da duwatsu masu daraja suka ba da su ga Yehiyel mutumin Gershon ma’ajin haikalin Ubangiji.
Ils mirent aussi les pierreries que chacun avait, au trésor de la maison de l'Eternel, entre les mains de Jéhiël Guersonite.
9 Mutane suka yi farin ciki ganin yadda shugabanninsu suke bayarwa da yardar rai, gama sun bayar hannu sake da kuma dukan zuciya ga Ubangiji. Dawuda sarki shi ma ya yi farin ciki ƙwarai.
Et le peuple offrait avec joie volontairement; car ils offraient de tout leur cœur leurs offrandes volontaires à l'Eternel; et David en eut une fort grande joie.
10 Dawuda ya yabi Ubangiji a gaban dukan taron, yana cewa, “Yabo gare ka, ya Ubangiji, Allah na mahaifinmu Isra’ila, har abada abadin.
Puis David bénit l'Eternel en la présence de toute l'assemblée, et dit: Ô Eternel Dieu d'Israël notre père! tu [es] béni de tout temps et à toujours.
11 Girma da iko da ɗaukaka, da daraja da kuma nasara naka ne, ya Ubangiji, gama kome a sama da ƙasa naka ne. Mulki kuma naka ne, ya Ubangiji; an kuma ɗaukaka ka a matsayin kai a bisa duka.
Ô Eternel! c'est à toi qu'appartient la magnificence, la puissance, la gloire, l'éternité, et la majesté; car tout ce qui est aux cieux et en la terre est à toi; ô Eternel! le Royaume est à toi, et tu es le Prince de toutes choses.
12 Wadata da girma daga gare ka suke; kai ne mai mulkin dukan abubuwa. A hannuwanka ne ƙarfi da iko suke don ka ɗaukaka da kuma ba da ƙarfi ga duka.
Les richesses et les honneurs viennent de toi, et tu as la domination sur toutes choses; la force et la puissance est en ta main, et il est aussi en ta main d'agrandir et de fortifier toutes choses.
13 Yanzu fa, Allahnmu, muna gode maka, muna kuma yabon ɗaukakar sunanka.
Maintenant donc, ô notre Dieu! nous te célébrons, et nous louons ton Nom glorieux.
14 “Amma wane ni, kuma wace ce jama’ata da za mu iya ba ka a yalwace kamar haka? Kome daga gare ka suka fito, kuma mun ba ka abin da kawai ya fito daga hannunka ne.
Mais qui suis-je, et qui est mon peuple, que nous ayons assez de pouvoir pour offrir ces choses volontairement? car toutes choses viennent de toi, et [les ayant reçues] de ta main, nous te les présentons.
15 Mu bare ne kuma baƙi a gabanka, kamar yadda dukan kakanninmu suke. Kwanakinmu a duniya suna kamar inuwa ne, ba sa zuciya.
Et même nous sommes étrangers et forains chez toi, comme [ont été] tous nos pères; [et] nos jours sont comme l'ombre sur la terre, et il n'y a nulle espérance.
16 Ya Ubangiji Allahnmu, game da dukan wannan yalwar da ka tanada saboda ginin haikali saboda Sunanka Mai Tsarki, sun fito daga hannunka ne, kuma dukan naka ne.
Eternel notre Dieu! toute cette abondance, que nous avons préparée pour bâtir une maison à ton saint Nom, est de ta main, et toutes ces choses sont à toi.
17 Na sani, Allahna, cewa kakan gwada zuciya, kakan kuma gamsu da mutunci. Dukan waɗannan abubuwa na bayar da yardar rai da kuma kyakkyawar niyya. Yanzu kuma da farin ciki na ga yadda mutanenka waɗanda suke a nan da yardar rai suka ba ka.
Et je sais, ô mon Dieu! que c'est toi qui sondes les cœurs, et que tu prends plaisir à la droiture; c'est pourquoi j'ai volontairement offert d'un cœur droit toutes ces choses, et j'ai vu maintenant avec joie que ton peuple, qui s'est trouvé ici, t'a fait son offrande volontairement.
18 Ya Ubangiji Allah na kakanninmu Ibrahim, Ishaku da Isra’ila, ka sa wannan sha’awa a cikin zukatan mutanenka har abada, ka kuma bar zukatansu su yi maka biyayya.
Ô Eternel! Dieu d'Abraham, d'Isaac, et d'Israël nos pères, entretiens ceci à toujours, [savoir] l'inclination des pensées du cœur de ton peuple, et tourne leurs cœurs vers toi.
19 Ka kuma ba ɗana Solomon cikakkiyar zuciya don yă kiyaye umarnanka, farillanka da ƙa’idodinka yă kuma yi kome don yă gina ƙasaitaccen gini wanda na riga na yi tanadi dominsa.”
Donne aussi un cœur droit à Salomon mon fils, afin qu'il garde tes commandements, tes témoignages, et tes statuts, et qu'il fasse tout [ce qui est nécessaire] et qu'il bâtisse le palais que j'ai préparé.
20 Sa’an nan Dawuda ya ce wa dukan taron, “Ku yabi Ubangiji Allahnku.” Saboda haka suka yabi Ubangiji Allah na kakanninsu; suka rusuna suka kuma fāɗi rubda ciki a gaban Ubangiji da kuma sarki.
Après cela David dit à toute l'assemblée: Bénissez maintenant l'Eternel votre Dieu. Et toute l'assemblée bénit l'Eternel, le Dieu de leurs pères, et s'inclinant, ils se prosternèrent devant l'Eternel, et devant le Roi.
21 Kashegari suka miƙa hadayu ga Ubangiji suka kuma miƙa hadayu bijimai dubu, raguna dubu da kuma’yan raguna dubu na ƙonawa gare shi, tare da hadayunsu na sha da sauran hadayu a yalwace saboda dukan Isra’ila.
Et le lendemain ils sacrifièrent des sacrifices à l'Eternel, et lui offrirent des holocaustes, [savoir] mille veaux, mille moutons, et mille agneaux, avec leurs aspersions; et des sacrifices en grand nombre pour tous ceux d'Israël.
22 Suka ci suka sha da farin ciki mai girma a gaban Ubangiji a wannan rana. Sa’an nan suka yarda da Solomon ɗan Dawuda a matsayin sarki sau na biyu, suka shafe shi a gaban Ubangiji don yă zama mai mulki, Zadok kuwa ya zama firist.
Et ils mangèrent et burent ce jour-là devant l'Eternel avec une grande joie; et ils établirent Roi pour la seconde fois Salomon fils de David, et l'oignirent en l'honneur de l'Eternel pour être leur Conducteur, et Tsadoc pour Sacrificateur.
23 Saboda haka Solomon ya zauna a kujerar sarautar Ubangiji a matsayin sarki a maimakon mahaifinsa Dawuda. Ya yi nasara, dukan Isra’ila kuwa suka yi masa biyayya.
Salomon donc s'assit sur le trône de l'Eternel pour être Roi en la place de David son père, et il prospéra; car tout Israël lui obéit.
24 Dukan shugabanni da jarumawa, har ma da dukan’ya’yan Sarki Dawuda maza, suka yi alkawari za su yi wa Sarki Solomon biyayya.
Et tous les principaux et les puissants, et même tous les fils du Roi David consentirent d'être les sujets du Roi Salomon.
25 Ubangiji ya ɗaukaka Solomon sosai a idon dukan Isra’ila, ya kuma ba shi darajar sarauta yadda babu sarki a Isra’ilan da ya taɓa samu.
Ainsi l'Eternel éleva souverainement Salomon, à la vue de tout Israël; et lui donna une majesté Royale, telle qu'aucun Roi avant lui n'en avait eue en Israël.
26 Dawuda ɗan Yesse ya zama sarki a bisa dukan Isra’ila.
David donc fils d'Isaï régna sur tout Israël.
27 Ya yi mulki a bisa Isra’ila shekaru arba’in, shekaru bakwai a Hebron da kuma shekaru talatin da uku a Urushalima.
Et les jours qu'il régna sur Israël furent quarante ans; il régna sept ans à Hébron, et trente-trois ans à Jérusalem.
28 Ya mutu a kyakkyawar tsufa, bayan ya more dogon rai, wadata da girma. Ɗansa Solomon ya gāje shi a matsayin sarki.
Puis il mourut en bonne vieillesse, rassasié de jours, de richesses, et de gloire; et Salomon son fils régna en sa place.
29 Game da ayyukan mulkin Sarki Dawuda, daga farko har ƙarshe, an rubuta su a cikin tarihin Sama’ila mai duba, tarihin annabi Natan da kuma tarihin Gad mai duba,
Or quant aux faits du Roi David, tant les premiers que les derniers, voilà, ils sont écrits au Livre de Samuël le Voyant, et aux Livres de Nathan le Prophète, et aux Livres de Gad le Voyant,
30 tare da yadda mulkinsa da ikonsa da yanayin da suka kewaye shi da Isra’ila da kuma dukan masarautai na dukan sauran ƙasashe.
Avec tout son règne, et sa force, et les temps qui passèrent sur lui, et sur Israël, et sur tous les Royaumes des pays.

< 1 Tarihi 29 >