< 1 Tarihi 29 >

1 Sa’an nan Sarki Dawuda ya ce wa dukan taron, “Ɗana Solomon, wanda Allah ya zaɓa, matashi ne, kuma bai gogu ba. Aikin yana da yawa, domin wannan ƙasaitaccen ginin ba na mutum ba ne, na Ubangiji Allah ne.
And kyng Dauid spak to al the chirche, God hath chose Salomon, my sone, yit a child and tendre; forsothe the werk is greet, and a dwellyng is not maad redi to man but to God.
2 Na riga na tara dukan kayayyakin da na tanada saboda haikalin Allahna, zinariya saboda dukan ayyukan zinariya, azurfa saboda ayyukan azurfa, tagulla saboda ayyukan tagulla, ƙarfe saboda ayyukan ƙarfe da kuma katako saboda ayyukan katako, da onis don ado, turkuwoyis, duwatsu masu launi dabam-dabam, da kuma dukan duwatsu masu kyau da mabul, dukan waɗannan suna nan jingim.
Sotheli Y in alle my myytis haue maad redi the costis of the hows of my God; gold to goldun vessels, siluer in to siluerne vessels, bras in to brasun vessels, irun in to irun vessels, tre in to trenun vessels, onychyn stonys, and stonys as of the colour of wymmens oynement, and ech precious stoon of dyuerse colouris, and marbil of dyuerse colouris, most plenteuously.
3 Ban da haka ma, cikin sa zuciyata ga haikalin Allahna, yanzu na ba da ma’ajina na zinariya da azurfa saboda haikalin Allahna, fiye da kome na tanada saboda wannan haikali,
And ouer these thingis Y yyue gold and siluer in to the temple of my God, whiche Y offride of my propir catel in to the hows of my God, outakun these thingis whiche Y made redi in to the hooli hows,
4 talenti dubu uku na zinariya (zinariyar Ofir) da tacecciyar azurfa dubu bakwai; don adon bangon gine-ginen,
thre thousynde talentis of gold, of the gold of Ophir, and seuene thousynde of talentis of siluer most preuyd, to ouergilde the wallis of the temple;
5 don aikin zinariya da kuma aikin azurfa, don kuma dukan aikin da gwanaye za su yi. Yanzu fa wa yake da niyya yă miƙa kansa a yau don Ubangiji?”
and werkis be maad bi the hondis of crafti men, where euere gold is nedeful, of gold, and where euere siluer is nedeful, of siluer; and if ony man offrith bi his fre wille, fille he his hond to dai, and offre he that that he wole to the Lord.
6 Sai shugabannin iyalai, shugabannin kabilan Isra’ila, manyan hafsoshin mayaƙa dubu-dubu da manyan hafsoshi mayaƙa ɗari-ɗari, da shugabannin lura da ayyukan sarki suka yi bayarwa da yardar rai.
Therfor the princes of meynees, and the duykis of the lynagis of Israel, and the tribunes, and the centuriouns, and the princes of the possessiouns of the kyng, bihiyten;
7 Suka bayar talenti dubu biyar na zinariya, talenti dubu goma na azurfa, talenti dubu goma sha takwas na tagulla da talenti dubu ɗari na ƙarfe don aiki a haikalin Allah.
and thei yauen in to the werkis of the hows of the Lord, fyue thousynde talentis of gold, and ten thousynde schyllyngis; ten thousynde talentis of siluer, and eiytene thousynde talentis of bras, and an hundrid thousynde of talentis of irun.
8 Duk waɗanda suke da duwatsu masu daraja suka ba da su ga Yehiyel mutumin Gershon ma’ajin haikalin Ubangiji.
And at whom euere stoonys were foundun, thei yauen in to the tresour of the hows of the Lord, bi the hond of Jehiel Gersonyte.
9 Mutane suka yi farin ciki ganin yadda shugabanninsu suke bayarwa da yardar rai, gama sun bayar hannu sake da kuma dukan zuciya ga Ubangiji. Dawuda sarki shi ma ya yi farin ciki ƙwarai.
And the puple was glad, whanne thei bihiyten avowis bi her fre wille, for with al the herte thei offriden tho to the Lord. But also kyng Dauid was glad with greet ioye, and blesside the Lord bifor al the multitude,
10 Dawuda ya yabi Ubangiji a gaban dukan taron, yana cewa, “Yabo gare ka, ya Ubangiji, Allah na mahaifinmu Isra’ila, har abada abadin.
and seide, Lord God of Israel, oure fadir, thou art blessid fro with outen bigynnyng in to with outen ende;
11 Girma da iko da ɗaukaka, da daraja da kuma nasara naka ne, ya Ubangiji, gama kome a sama da ƙasa naka ne. Mulki kuma naka ne, ya Ubangiji; an kuma ɗaukaka ka a matsayin kai a bisa duka.
Lord, worthi doyng is thin, and power, and glorie, and victorie, and heriyng is to thee; for alle thingis that ben in heuene and in erthe ben thine; Lord, the rewme is thin, and thou art ouer alle princes; ritchessis ben thin, and glorie is thin;
12 Wadata da girma daga gare ka suke; kai ne mai mulkin dukan abubuwa. A hannuwanka ne ƙarfi da iko suke don ka ɗaukaka da kuma ba da ƙarfi ga duka.
thou art Lord of alle; in thin hond is vertu, and power, and in thin hond is greetnesse, and lordschipe of alle.
13 Yanzu fa, Allahnmu, muna gode maka, muna kuma yabon ɗaukakar sunanka.
Now therfor, oure God, we knoulechen to thee, and we herien thi noble name.
14 “Amma wane ni, kuma wace ce jama’ata da za mu iya ba ka a yalwace kamar haka? Kome daga gare ka suka fito, kuma mun ba ka abin da kawai ya fito daga hannunka ne.
Who am Y, and who is my puple, that we moun bihete alle these thingis to thee? Alle thingis ben thine, and we han youe to thee tho thingis, whiche we token of thin hond.
15 Mu bare ne kuma baƙi a gabanka, kamar yadda dukan kakanninmu suke. Kwanakinmu a duniya suna kamar inuwa ne, ba sa zuciya.
For we ben pilgrimes and comelyngis bifor thee, as alle oure fadris; oure daies ben as schadewe on the erthe, and `no dwellyng is.
16 Ya Ubangiji Allahnmu, game da dukan wannan yalwar da ka tanada saboda ginin haikali saboda Sunanka Mai Tsarki, sun fito daga hannunka ne, kuma dukan naka ne.
Oure Lord God, al this plentee which we han maad redi, that an hows schulde be byldid to thin hooli name, is of thin hond; and alle thingis ben thin.
17 Na sani, Allahna, cewa kakan gwada zuciya, kakan kuma gamsu da mutunci. Dukan waɗannan abubuwa na bayar da yardar rai da kuma kyakkyawar niyya. Yanzu kuma da farin ciki na ga yadda mutanenka waɗanda suke a nan da yardar rai suka ba ka.
My God, Y woot, that thou preuest hertis, and louest symplenesse of herte; wherfor and Y, in the symplenesse of myn herte, haue offrid gladli alle these thingis; and Y siy with greet ioye thi puple, which is foundun here, offre yiftis to thee.
18 Ya Ubangiji Allah na kakanninmu Ibrahim, Ishaku da Isra’ila, ka sa wannan sha’awa a cikin zukatan mutanenka har abada, ka kuma bar zukatansu su yi maka biyayya.
Lord God of Abraham, and of Ysaac, and of Israel, oure fadris, kepe thou with outen ende this wille of her hertis; and this mynde dwelle euere in to the worschipyng of thee.
19 Ka kuma ba ɗana Solomon cikakkiyar zuciya don yă kiyaye umarnanka, farillanka da ƙa’idodinka yă kuma yi kome don yă gina ƙasaitaccen gini wanda na riga na yi tanadi dominsa.”
Also yyue thou to Salomon, my sone, a perfit herte, that he kepe thin heestis, and witnessyngis, and thi ceremonyes; and do alle thingis, and that he bilde the hows, whose costis Y haue maad redi.
20 Sa’an nan Dawuda ya ce wa dukan taron, “Ku yabi Ubangiji Allahnku.” Saboda haka suka yabi Ubangiji Allah na kakanninsu; suka rusuna suka kuma fāɗi rubda ciki a gaban Ubangiji da kuma sarki.
Forsothe Dauid comaundide to al the chirche, Blesse ye `oure Lord God. And al the chirche blesside the Lord God of her fadris, and thei bowiden hem silf, and worschipiden God, aftirward the kyng.
21 Kashegari suka miƙa hadayu ga Ubangiji suka kuma miƙa hadayu bijimai dubu, raguna dubu da kuma’yan raguna dubu na ƙonawa gare shi, tare da hadayunsu na sha da sauran hadayu a yalwace saboda dukan Isra’ila.
And thei offriden slayn sacrifices to the Lord, and thei offriden brent sacrifices in the dai suynge; a thousynde boolis, and a thousynde rammes, and a thousynde lambren, with her fletynge sacrifices, and al the custom, most plenteuously, in to al Israel.
22 Suka ci suka sha da farin ciki mai girma a gaban Ubangiji a wannan rana. Sa’an nan suka yarda da Solomon ɗan Dawuda a matsayin sarki sau na biyu, suka shafe shi a gaban Ubangiji don yă zama mai mulki, Zadok kuwa ya zama firist.
And thei eten and drunken bifor the Lord in that dai, with greet gladnesse. And thei anoyntiden the secounde tyme Salomon, the sone of Dauid; and thei anoyntiden hym in to prince to the Lord, and Sadoch in to bischop.
23 Saboda haka Solomon ya zauna a kujerar sarautar Ubangiji a matsayin sarki a maimakon mahaifinsa Dawuda. Ya yi nasara, dukan Isra’ila kuwa suka yi masa biyayya.
And Salomon sat on the trone of the Lord in to kyng, for Dauid, his fadir; and it pleside alle men, and al Israel obeiede to hym.
24 Dukan shugabanni da jarumawa, har ma da dukan’ya’yan Sarki Dawuda maza, suka yi alkawari za su yi wa Sarki Solomon biyayya.
But also alle princes, and myyti men, and alle the sones of kyng Dauid, yauen hond, and weren suget to `Salomon the kyng.
25 Ubangiji ya ɗaukaka Solomon sosai a idon dukan Isra’ila, ya kuma ba shi darajar sarauta yadda babu sarki a Isra’ilan da ya taɓa samu.
Therfor the Lord magnefiede Salomon on al Israel, and yaue to hym glorie of the rewme, what maner glorie no kyng of Israel hadde bifor hym.
26 Dawuda ɗan Yesse ya zama sarki a bisa dukan Isra’ila.
Therfor Dauid, the sone of Ysai, regnede on al Israel;
27 Ya yi mulki a bisa Isra’ila shekaru arba’in, shekaru bakwai a Hebron da kuma shekaru talatin da uku a Urushalima.
and the daies in whiche he regnede on Israel weren fourti yeer; in Ebron he regnede seuene yeer, and in Jerusalem thre and thretti yeer.
28 Ya mutu a kyakkyawar tsufa, bayan ya more dogon rai, wadata da girma. Ɗansa Solomon ya gāje shi a matsayin sarki.
And he diede in good eelde, and was ful of daies, and richessis, and glorie; and Salomon, his sone, regnede for hym.
29 Game da ayyukan mulkin Sarki Dawuda, daga farko har ƙarshe, an rubuta su a cikin tarihin Sama’ila mai duba, tarihin annabi Natan da kuma tarihin Gad mai duba,
Forsothe the formere and the laste dedis of Dauid ben writun in the book of Samuel, the prophete, and in the book of Nathan, prophete, and in the book of Gad, the prophete;
30 tare da yadda mulkinsa da ikonsa da yanayin da suka kewaye shi da Isra’ila da kuma dukan masarautai na dukan sauran ƙasashe.
and of al his rewme, and strengthe, and tymes, that passiden vndur hym, ethir in Israel, ethir in alle rewmes of londis.

< 1 Tarihi 29 >