< 1 Tarihi 29 >
1 Sa’an nan Sarki Dawuda ya ce wa dukan taron, “Ɗana Solomon, wanda Allah ya zaɓa, matashi ne, kuma bai gogu ba. Aikin yana da yawa, domin wannan ƙasaitaccen ginin ba na mutum ba ne, na Ubangiji Allah ne.
And king David said to all the assembly: Solomon my son, whom alone God hath chosen, is as yet young and tender: and the work is great, for a house is prepared not for man, but for God.
2 Na riga na tara dukan kayayyakin da na tanada saboda haikalin Allahna, zinariya saboda dukan ayyukan zinariya, azurfa saboda ayyukan azurfa, tagulla saboda ayyukan tagulla, ƙarfe saboda ayyukan ƙarfe da kuma katako saboda ayyukan katako, da onis don ado, turkuwoyis, duwatsu masu launi dabam-dabam, da kuma dukan duwatsu masu kyau da mabul, dukan waɗannan suna nan jingim.
And I with all my ability have prepared the expenses for the house of my God. Gold for vessels of gold, and silver for vessels of silver, brass for things of brass, iron for things of iron, wood for things of wood: and onyx stones, and stones like alabaster, and of divers colours, and all manner of precious stones, and marble of Paros in great abundance.
3 Ban da haka ma, cikin sa zuciyata ga haikalin Allahna, yanzu na ba da ma’ajina na zinariya da azurfa saboda haikalin Allahna, fiye da kome na tanada saboda wannan haikali,
Now over and above the things which I have offered into the house of my God I give of my own proper goods, gold and silver for the temple of my God, beside what things I have prepared for the holy house.
4 talenti dubu uku na zinariya (zinariyar Ofir) da tacecciyar azurfa dubu bakwai; don adon bangon gine-ginen,
Three thousand talents of gold of the gold of Ophir: and seven thousand talents of refined silver, to overlay the walls of the temple.
5 don aikin zinariya da kuma aikin azurfa, don kuma dukan aikin da gwanaye za su yi. Yanzu fa wa yake da niyya yă miƙa kansa a yau don Ubangiji?”
And gold for wheresoever there is need of gold: and silver for wheresoever there is need of silver, for the works to be made by the hands of the artificers: now if any man is willing to offer, let him fill his hand today, and offer what he pleaseth to the Lord.
6 Sai shugabannin iyalai, shugabannin kabilan Isra’ila, manyan hafsoshin mayaƙa dubu-dubu da manyan hafsoshi mayaƙa ɗari-ɗari, da shugabannin lura da ayyukan sarki suka yi bayarwa da yardar rai.
Then the heads of the families, and the princes of the tribes of Israel, and the captains of thousands, and of hundreds, and the overseers of the king’s possessions promised,
7 Suka bayar talenti dubu biyar na zinariya, talenti dubu goma na azurfa, talenti dubu goma sha takwas na tagulla da talenti dubu ɗari na ƙarfe don aiki a haikalin Allah.
And they gave for the works of the house of the Lord, of gold, five thousand talents, and ten thousand solids: of silver ten thousand talents: and of brass eighteen thousand talents: and of iron a hundred thousand talents.
8 Duk waɗanda suke da duwatsu masu daraja suka ba da su ga Yehiyel mutumin Gershon ma’ajin haikalin Ubangiji.
And all they that had stones, gave them to the treasures of the house of the Lord, by the hand of Jahiel the Gersonite.
9 Mutane suka yi farin ciki ganin yadda shugabanninsu suke bayarwa da yardar rai, gama sun bayar hannu sake da kuma dukan zuciya ga Ubangiji. Dawuda sarki shi ma ya yi farin ciki ƙwarai.
And the people rejoiced, when they promised their offerings willingly: because they offered them to the Lord with all their heart: and David the king rejoiced also with a great joy.
10 Dawuda ya yabi Ubangiji a gaban dukan taron, yana cewa, “Yabo gare ka, ya Ubangiji, Allah na mahaifinmu Isra’ila, har abada abadin.
And he blessed the Lord before all the multitude, and he said: Blessed art thou, O Lord the God of Israel, our father from eternity to eternity.
11 Girma da iko da ɗaukaka, da daraja da kuma nasara naka ne, ya Ubangiji, gama kome a sama da ƙasa naka ne. Mulki kuma naka ne, ya Ubangiji; an kuma ɗaukaka ka a matsayin kai a bisa duka.
Thine, O Lord, is magnificence, and power, and glory, and victory: and to thee is praise: for all that is in heaven, and in earth, is thine: thine is the kingdom, O Lord, and thou art above all princes.
12 Wadata da girma daga gare ka suke; kai ne mai mulkin dukan abubuwa. A hannuwanka ne ƙarfi da iko suke don ka ɗaukaka da kuma ba da ƙarfi ga duka.
Thine are riches, and thine is glory, thou hast dominion over all, in thy hand is power and might: in thy hand greatness, and the empire of all things.
13 Yanzu fa, Allahnmu, muna gode maka, muna kuma yabon ɗaukakar sunanka.
Now therefore our God we give thanks to thee, and we praise thy glorious name.
14 “Amma wane ni, kuma wace ce jama’ata da za mu iya ba ka a yalwace kamar haka? Kome daga gare ka suka fito, kuma mun ba ka abin da kawai ya fito daga hannunka ne.
Who am I, and what is my people, that we should be able to promise thee all these things? all things are thine: and we have given thee what we received of thy hand.
15 Mu bare ne kuma baƙi a gabanka, kamar yadda dukan kakanninmu suke. Kwanakinmu a duniya suna kamar inuwa ne, ba sa zuciya.
For we are sojourners before thee, and strangers, as were all our fathers. Our days upon earth are as a shadow, and there is no stay.
16 Ya Ubangiji Allahnmu, game da dukan wannan yalwar da ka tanada saboda ginin haikali saboda Sunanka Mai Tsarki, sun fito daga hannunka ne, kuma dukan naka ne.
O Lord our God, all this store that we have prepared to build thee a house for thy holy name, is from thy hand, and all things are thine.
17 Na sani, Allahna, cewa kakan gwada zuciya, kakan kuma gamsu da mutunci. Dukan waɗannan abubuwa na bayar da yardar rai da kuma kyakkyawar niyya. Yanzu kuma da farin ciki na ga yadda mutanenka waɗanda suke a nan da yardar rai suka ba ka.
I know my God that thou provest hearts, and lovest simplicity, wherefore I also in the simplicity of my heart, have joyfully offered all these things: and I have seen with great joy thy people, which are here present, offer thee their offerings.
18 Ya Ubangiji Allah na kakanninmu Ibrahim, Ishaku da Isra’ila, ka sa wannan sha’awa a cikin zukatan mutanenka har abada, ka kuma bar zukatansu su yi maka biyayya.
O Lord God of Abraham, and of Isaac, and of Israel our fathers, keep for ever this will of their heart, and let this mind remain always for the worship of thee.
19 Ka kuma ba ɗana Solomon cikakkiyar zuciya don yă kiyaye umarnanka, farillanka da ƙa’idodinka yă kuma yi kome don yă gina ƙasaitaccen gini wanda na riga na yi tanadi dominsa.”
And give to Solomon my son a perfect heart, that he may keep thy commandments, thy testimonies, and thy ceremonies, and do all things: and build the house, for which I have provided the charges.
20 Sa’an nan Dawuda ya ce wa dukan taron, “Ku yabi Ubangiji Allahnku.” Saboda haka suka yabi Ubangiji Allah na kakanninsu; suka rusuna suka kuma fāɗi rubda ciki a gaban Ubangiji da kuma sarki.
And David commanded all the assembly: Bless ye the Lord our God. And all the assembly blessed the Lord the God of their fathers: and they bowed themselves and worshipped God, and then the king.
21 Kashegari suka miƙa hadayu ga Ubangiji suka kuma miƙa hadayu bijimai dubu, raguna dubu da kuma’yan raguna dubu na ƙonawa gare shi, tare da hadayunsu na sha da sauran hadayu a yalwace saboda dukan Isra’ila.
And they sacrificed victims to the Lord: and they offered holocausts the next day, a thousand bullocks, a thousand rams, a thousand lambs, with their libations, and with every thing prescribed most abundantly for all Israel.
22 Suka ci suka sha da farin ciki mai girma a gaban Ubangiji a wannan rana. Sa’an nan suka yarda da Solomon ɗan Dawuda a matsayin sarki sau na biyu, suka shafe shi a gaban Ubangiji don yă zama mai mulki, Zadok kuwa ya zama firist.
And they ate, and drank before the Lord that day with great joy. And they anointed the second time Solomon the son of David. And they anointed him to the Lord to be prince, and Sadoc to be high priest.
23 Saboda haka Solomon ya zauna a kujerar sarautar Ubangiji a matsayin sarki a maimakon mahaifinsa Dawuda. Ya yi nasara, dukan Isra’ila kuwa suka yi masa biyayya.
And Solomon sat on the throne of the Lord as king instead of David his father, and he pleased all: and all Israel obeyed him.
24 Dukan shugabanni da jarumawa, har ma da dukan’ya’yan Sarki Dawuda maza, suka yi alkawari za su yi wa Sarki Solomon biyayya.
And all the princes, and men of power, and all the sons of king David gave their hand, and were subject to Solomon the king.
25 Ubangiji ya ɗaukaka Solomon sosai a idon dukan Isra’ila, ya kuma ba shi darajar sarauta yadda babu sarki a Isra’ilan da ya taɓa samu.
And the Lord magnified Solomon over all Israel: and gave him the glory of a reign, such as no king of Israel had before him.
26 Dawuda ɗan Yesse ya zama sarki a bisa dukan Isra’ila.
So David the son of Isai reigned over all Israel.
27 Ya yi mulki a bisa Isra’ila shekaru arba’in, shekaru bakwai a Hebron da kuma shekaru talatin da uku a Urushalima.
And the days that he reigned over Israel, were forty years: in Hebron he reigned seven years, and in Jerusalem three and thirty years.
28 Ya mutu a kyakkyawar tsufa, bayan ya more dogon rai, wadata da girma. Ɗansa Solomon ya gāje shi a matsayin sarki.
And he died in a good age, full of days, and riches, and glory. And Solomon his son reigned in his stead.
29 Game da ayyukan mulkin Sarki Dawuda, daga farko har ƙarshe, an rubuta su a cikin tarihin Sama’ila mai duba, tarihin annabi Natan da kuma tarihin Gad mai duba,
Now the acts of king David first and last are written in the book of Samuel the seer, and in the book of Nathan the prophet, and in the book of Gad the seer:
30 tare da yadda mulkinsa da ikonsa da yanayin da suka kewaye shi da Isra’ila da kuma dukan masarautai na dukan sauran ƙasashe.
And of all his reign, and his valour, and of the times that passed under him, either in Israel, or in all the kingdoms of the countries.