< 1 Tarihi 28 >

1 Dawuda ya sa aka kira dukan shugabannin Isra’ila su taru a Urushalima, shugabannin kabilu, manyan hafsoshin ɓangarorin hidimar sarki, manyan hafsoshin dubu-dubu da manyan hafsoshin ɗari-ɗari, da kuma shugabanni masu lura da dukan mallaka da dabbobin da suke na sarki da kuma’ya’yansa maza, tare da fadawa, jarumawa da kuma dukan mayaƙa masu kwarjini.
Or David assembla à Jérusalem tous les Chefs d'Israël, les Chefs des Tribus, et les Chefs des départements qui servaient le Roi; et les Gouverneurs de milliers et de centaines, et ceux qui avaient la charge de tous les biens du Roi, et de tout ce qu il possédait, ses fils avec ses Eunuques, et les hommes puissants, et tous les hommes forts et vaillants;
2 Sarki Dawuda ya miƙe tsaye ya ce, “Ku saurare ni,’yan’uwana da kuma mutanena. Na yi niyya in gina gida a matsayin wurin hutu domin akwatin alkawarin Ubangiji, domin zatin Allahnmu, na kuma yi shiri don in gina shi.
Puis le Roi David se leva sur ses pieds, et dit: Mes frères, et mon peuple, écoutez-moi: J'ai désiré de bâtir une maison de repos à l'Arche de l'alliance de l'Eternel, et au marchepied de notre Dieu, et j'ai fait les préparatifs pour la bâtir.
3 Amma Allah ya ce mini, ‘Ba za ka gina gida domin Sunana ba, saboda kai mayaƙi ne ka kuma zub da jini.’
Mais Dieu m'a dit: Tu ne bâtiras point de maison à mon Nom, parce que tu es un homme de guerre, et que tu as répandu beaucoup de sang.
4 “Duk da haka Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya zaɓe ni daga dukan iyalina don in zama sarki bisa Isra’ila har abada. Ya zaɓi Yahuda a matsayin shugaba, kuma daga gidan Yahuda ya zaɓi iyalina, daga’ya’yan mahaifina maza kuwa ya gamsu ya mai da ni sarki bisa dukan Isra’ila.
Or comme l'Eternel le Dieu d'Israël m'a choisi de toute la maison de mon père pour être Roi sur Israël à toujours; car il a choisi Juda pour Conducteur, et de la maison de Juda la maison de mon père, et d'entre les fils de mon père il a pris son plaisir en moi, pour me faire régner sur tout Israël.
5 Cikin dukan’ya’yana maza, Ubangiji kuwa ya ba ni su da yawa, ya zaɓi ɗana Solomon yă zauna a kujerar mulkin Ubangiji a bisa Isra’ila.
Aussi d'entre tous mes fils ( car l'Eternel m'a donné plusieurs fils ) il a choisi Salomon mon fils, pour s'asseoir sur le trône du Royaume de l'Eternel sur Israël.
6 Ya ce mini, ‘Solomon ɗanka shi ne wanda zai gina gidana da filayen da suke kewaye da shi, gama na zaɓe shi yă zama ɗana, ni kuma zan zama mahaifinsa.
Et il m'a dit: Salomon ton fils est celui qui bâtira ma maison et mes parvis; : car je me le suis choisi pour fils et je lui serai père.
7 Zan kafa mulkinsa har abada in bai kauce ga kiyaye umarnaina da dokokina ba, yadda ake yi a wannan lokaci.’
Et j'affermirai son règne à toujours, s'il s'applique à faire mes commandements [et à observer] mes ordonnances, comme [il le fait] aujourd'hui.
8 “Saboda haka yanzu ina umartanku a gaban dukan Isra’ila da na taron jama’ar Ubangiji, da kuma a kunnuwan Allahnmu. Ku yi hankali ku kiyaye dukan umarnan Ubangiji Allahnku don ku mallaki wannan kyakkyawar ƙasa ku kuma bar wa zuriyarku gādo har abada.
Maintenant donc [je vous somme] en la présence de tout Israël, qui est l'assemblée de l'Eternel, et devant notre Dieu qui l'entend, que vous ayez à garder et à rechercher diligemment tous les commandements de l'Eternel votre Dieu, afin que vous possédiez ce bon pays, et que vous le fassiez hériter à vos enfants après vous, à jamais.
9 “Kai kuma ɗana Solomon, ka san Allah na mahaifinka, ka kuma yi masa hidima da dukan zuciya da kuma yardar rai, gama Ubangiji yana binciken zuciya, yana kuma gane dukan aniyar tunani. In ka neme shi, za ka same shi; amma in ka yashe shi, zai ƙi ka har abada.
Et toi Salomon mon fils, connais le Dieu de ton père, et sers-le avec un cœur droit, et une bonne volonté; car l'Eternel sonde tous les cœurs, et connaît toutes les imaginations des pensées. Si tu le cherches, il se fera trouver à toi; mais si tu l'abandonnes, il te rejettera pour toujours.
10 Ka lura fa, gama Ubangiji ya zaɓe ka don ka gina haikali a matsayin wuri mai tsarki. Ka yi ƙarfin hali ka kuma yi aiki.”
Considère maintenant, que l'Eternel t'a choisi pour bâtir une maison pour son sanctuaire; fortifie-toi donc, et applique-toi à y travailler.
11 Sa’an nan Dawuda ya ba ɗansa Solomon tsari domin shirayin haikalin, gine-ginensa, ɗakunan ajiyarsa, ɓangarorin bisansa, ɗakunan cikinsa da kuma wurin kafara.
Et David donna à Salomon son fils le modèle du portique, de ses maisons, de ses cabinets, de ses chambres hautes, de ses cabinets de dedans, et du lieu du Propitiatoire.
12 Ya ba shi tsarin dukan abin da Ruhu ya sa a zuciyarsa saboda filayen haikalin Ubangiji da ɗakunan kewaye, da ma’ajin haikalin Allah da kuma baitulmali na kayayyakin da aka keɓe.
Et le modèle de toutes les choses qui lui avaient été inspirées par l'Esprit qui était avec lui, pour les parvis de la maison de l'Eternel, pour les chambres d'alentour, pour les trésors de la maison de l'Eternel, et pour les trésors des choses saintes;
13 Ya ba shi tsari game ɓangarori na firistoci da Lawiyawa, da game dukan aikin hidima a cikin haikalin Ubangiji, da kuma game da dukan kayayyakin da za a yi amfani da su a hidima.
Et pour les départements des Sacrificateurs et des Lévites, et pour toute l'œuvre du service de la maison de l'Eternel, et pour tous les ustensiles du service de la maison de l'Eternel.
14 Ya kimanta yawan zinariya don dukan kayayyakin zinariyar da za a yi amfani a kowane irin hidima, da yawan azurfa don dukan kayayyakin azurfan da za a yi amfani a kowace irin hidima.
[Il lui donna aussi] de l'or à certain poids, pour les choses qui devaient être d'or, [savoir] pour tous les ustensiles de chaque service; [et de l'argent] à certain poids, pour tous les ustensiles d'argent, [savoir] pour tous les ustensiles de chaque service.
15 Da yawan zinariya don wurin ajiye fitilan fitilu da fitilunsu, da yawan zinariyan da za a yi amfani don kowace fitila da wurin ajiye fitilanta; da kuma yawan azurfa don kowane wurin ajiye fitila da fitilunsa bisa ga yadda za a yi amfani da kowane wurin ajiye fitila;
Le poids des chandeliers d'or, et de leurs lampes d'or, selon le poids de chaque chandelier et de ses lampes; et [le poids] des chandeliers d'argent, selon le poids de chaque chandelier et de ses lampes, selon le service de chaque chandelier.
16 yawan zinariya don kowane tebur saboda burodi mai tsaki; da kuma yawan azurfa saboda teburin azurfa;
Et le poids de l'or pesant ce qu'il fallait pour chaque table des pains de proposition; et de l'argent pour les tables d'argent.
17 yawan zinariya zalla, don cokula masu yatsu, kwanonin yayyafawa ruwa da kuma tuluna; yawan zinariya don kowane kwanon zinariya; yawan azurfa don kowane kwanon azurfa;
Et de l'or pur pour les fourchettes, pour les bassins, pour les gobelets, et pour les plats d'or, selon le poids de chaque plat; et [de l'argent] pour les plats d'argent, selon le poids de chaque plat.
18 da kuma yawan tacecciyar zinariya don bagaden turare. Ya kuma ba shi tsari don keken yaƙi, wato, kerubobin zinariyar da suka miƙe fikafikansu suka inuwantar da akwatin alkawarin Ubangiji.
Et de l'or affiné à certain poids pour l'autel des parfums; et de l'or pour le modèle du chariot des Chérubins qui étendaient [les ailes], et qui couvraient l'Arche de l'alliance de l'Eternel.
19 Dawuda ya ce, “Dukan wannan, ina da shi a rubuce daga hannun Ubangiji zuwa gare ni, ya kuma ba ni ganewa cikin dukan tsarin fasalin, filla-filla.”
Toutes ces choses, [dit-il], m'ont été données par écrit, de la part de l'Eternel, afin que j'eusse l'intelligence de tous les ouvrages de ce modèle.
20 Dawuda ya kuma ce wa Solomon ɗansa, “Ka yi ƙarfin hali, ka kuma yi aikin. Kada ka ji tsoro ko ka fid da zuciya, gama Ubangiji Allah, Allahna, yana tare da kai. Ba zai bari ka ji kunya ko yă yashe ka ba, sai an gama dukan aikin saboda hidimar haikalin Ubangiji.
C'est pourquoi David dit à Salomon son fils: Fortifie-toi, et prends courage, et travaille; ne crains point, et ne t'effraie de rien; car l'Eternel Dieu, mon Dieu, [sera] avec toi, il ne te délaissera point, et il ne t'abandonnera point, que tu n'aies achevé tout l'ouvrage du service de la maison de l'Eternel.
21 Sassan firistoci da na Lawiyawa suna a shirye domin dukan aiki a haikalin Allah, kuma kowane gwani mai niyya a kowace sana’a, zai taimake ka a cikin dukan aikin. Shugabanni da dukan mutane za su yi biyayya da kowane umarninka.”
Et voici, [j'ai fait] les départements des Sacrificateurs et des Lévites pour tout le service de la maison de Dieu; et il y a avec toi pour tout cet ouvrage toutes sortes de gens prompts et experts, pour toute sorte de service; et les Chefs avec tout le peuple [seront prêts] pour exécuter tout ce que tu diras.

< 1 Tarihi 28 >