< 1 Tarihi 28 >

1 Dawuda ya sa aka kira dukan shugabannin Isra’ila su taru a Urushalima, shugabannin kabilu, manyan hafsoshin ɓangarorin hidimar sarki, manyan hafsoshin dubu-dubu da manyan hafsoshin ɗari-ɗari, da kuma shugabanni masu lura da dukan mallaka da dabbobin da suke na sarki da kuma’ya’yansa maza, tare da fadawa, jarumawa da kuma dukan mayaƙa masu kwarjini.
David summoned all the leaders of Israel to come to Jerusalem. He summoned the leaders of the tribes, the leaders/commanders of the groups that worked for the king, the commanders of 100 soldiers, the commanders of 1,000 soldiers, those who were in charge of the property and livestock that belonged to the king and his sons, all the palace officials, and his mighty soldiers and bravest warriors.
2 Sarki Dawuda ya miƙe tsaye ya ce, “Ku saurare ni,’yan’uwana da kuma mutanena. Na yi niyya in gina gida a matsayin wurin hutu domin akwatin alkawarin Ubangiji, domin zatin Allahnmu, na kuma yi shiri don in gina shi.
David stood up and said, “My fellow Israelis, listen to me. I wanted [IDM] to build a temple to be a place where we would put the Sacred Chest of Yahweh, where it would stay permanently. And I made plans to build it.
3 Amma Allah ya ce mini, ‘Ba za ka gina gida domin Sunana ba, saboda kai mayaƙi ne ka kuma zub da jini.’
But God said to me, ‘You are not the one who will [arrange to] build a temple for me [MTY], because you are a warrior and you have killed many people [MTY] [in battles].’
4 “Duk da haka Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya zaɓe ni daga dukan iyalina don in zama sarki bisa Isra’ila har abada. Ya zaɓi Yahuda a matsayin shugaba, kuma daga gidan Yahuda ya zaɓi iyalina, daga’ya’yan mahaifina maza kuwa ya gamsu ya mai da ni sarki bisa dukan Isra’ila.
“But Yahweh, the God to whom we Israelis belong, had chosen me and my descendants to be the kings of Israel forever. [First] he chose the tribe of Judah, and from the people [MTY] of Judah he chose my family, and from my father’s sons he chose me to be the king over all of Israel.
5 Cikin dukan’ya’yana maza, Ubangiji kuwa ya ba ni su da yawa, ya zaɓi ɗana Solomon yă zauna a kujerar mulkin Ubangiji a bisa Isra’ila.
Yahweh has given me many sons, but from them he chose my son Solomon to be the next king to rule [MTY] the kingdom of Israel.
6 Ya ce mini, ‘Solomon ɗanka shi ne wanda zai gina gidana da filayen da suke kewaye da shi, gama na zaɓe shi yă zama ɗana, ni kuma zan zama mahaifinsa.
He said to me, ‘Solomon your son is the one who will [arrange to] build my temple and the courtyards around it, because I have chosen him to be [like] my son and I will be [like] [MET] his father.
7 Zan kafa mulkinsa har abada in bai kauce ga kiyaye umarnaina da dokokina ba, yadda ake yi a wannan lokaci.’
I will enable his kingdom to endure forever if he continues to obey my laws and commands, like you are doing now.’
8 “Saboda haka yanzu ina umartanku a gaban dukan Isra’ila da na taron jama’ar Ubangiji, da kuma a kunnuwan Allahnmu. Ku yi hankali ku kiyaye dukan umarnan Ubangiji Allahnku don ku mallaki wannan kyakkyawar ƙasa ku kuma bar wa zuriyarku gādo har abada.
“So now, while all [you people of] Israel, all of you who belong to Yahweh, are watching, and while God is listening, I command you [leaders] to carefully obey all the commands of Yahweh our God, in order that you may continue to possess this good land and enable your descendants to inherit it forever.
9 “Kai kuma ɗana Solomon, ka san Allah na mahaifinka, ka kuma yi masa hidima da dukan zuciya da kuma yardar rai, gama Ubangiji yana binciken zuciya, yana kuma gane dukan aniyar tunani. In ka neme shi, za ka same shi; amma in ka yashe shi, zai ƙi ka har abada.
“And you, my son Solomon, must know God like I know him, and you must serve him faithfully and because you want to. You must do that because he knows what everyone is thinking and he understands the reasons that people do what they do. If you seek [to know] him, he will heed your prayers. But if you abandon/reject him, he will abandon/reject you forever.
10 Ka lura fa, gama Ubangiji ya zaɓe ka don ka gina haikali a matsayin wuri mai tsarki. Ka yi ƙarfin hali ka kuma yi aiki.”
Yahweh has chosen you to [arrange to] build a temple for him. So think about [what I have said], and be strong and do what [he is wanting you to do].”
11 Sa’an nan Dawuda ya ba ɗansa Solomon tsari domin shirayin haikalin, gine-ginensa, ɗakunan ajiyarsa, ɓangarorin bisansa, ɗakunan cikinsa da kuma wurin kafara.
Then David gave to his son Solomon [the scroll on which were written] the plans for the main rooms of the temple, its porch, its storerooms, all the other upper and lower rooms, and the Very Holy Place where God would forgive the sins that people had committed.
12 Ya ba shi tsarin dukan abin da Ruhu ya sa a zuciyarsa saboda filayen haikalin Ubangiji da ɗakunan kewaye, da ma’ajin haikalin Allah da kuma baitulmali na kayayyakin da aka keɓe.
David wrote for him the plans that God’s Spirit had put into his mind for building the courtyards and all the rooms that surrounded the temple, including the room where the money and other valuable things that were dedicated to God would be kept.
13 Ya ba shi tsari game ɓangarori na firistoci da Lawiyawa, da game dukan aikin hidima a cikin haikalin Ubangiji, da kuma game da dukan kayayyakin da za a yi amfani da su a hidima.
He gave Solomon instructions for the groups of priests and other descendants of Levi, about all the work that they must do to serve in Yahweh’s temple, and about taking care of all the things that would be used in the work at the temple.
14 Ya kimanta yawan zinariya don dukan kayayyakin zinariyar da za a yi amfani a kowane irin hidima, da yawan azurfa don dukan kayayyakin azurfan da za a yi amfani a kowace irin hidima.
He wrote down how much gold and how much silver should be used to make all the items in the temple:
15 Da yawan zinariya don wurin ajiye fitilan fitilu da fitilunsu, da yawan zinariyan da za a yi amfani don kowace fitila da wurin ajiye fitilanta; da kuma yawan azurfa don kowane wurin ajiye fitila da fitilunsa bisa ga yadda za a yi amfani da kowane wurin ajiye fitila;
how much gold for making the gold lampstands and the lamps, how much silver to make the silver lamps and lampstands,
16 yawan zinariya don kowane tebur saboda burodi mai tsaki; da kuma yawan azurfa saboda teburin azurfa;
how much gold for making the table on which [the priests would put] the sacred bread, how much silver to use to make the other tables,
17 yawan zinariya zalla, don cokula masu yatsu, kwanonin yayyafawa ruwa da kuma tuluna; yawan zinariya don kowane kwanon zinariya; yawan azurfa don kowane kwanon azurfa;
how much pure gold for the meat forks and the bowls and the cups, how much gold for each gold dish, how much silver for each silver dish,
18 da kuma yawan tacecciyar zinariya don bagaden turare. Ya kuma ba shi tsari don keken yaƙi, wato, kerubobin zinariyar da suka miƙe fikafikansu suka inuwantar da akwatin alkawarin Ubangiji.
and how much pure gold to make the altar for [burning] incense. He also gave to Solomon his plans for making the golden statues of winged creatures that would be above the Sacred Chest of Yahweh, [like] a chariot for him.
19 Dawuda ya ce, “Dukan wannan, ina da shi a rubuce daga hannun Ubangiji zuwa gare ni, ya kuma ba ni ganewa cikin dukan tsarin fasalin, filla-filla.”
Then David said, “I have written [all these plans] while Yahweh was directing [MTY] me. He has enabled me to understand all the details of his plan [for the temple that is to be built].”
20 Dawuda ya kuma ce wa Solomon ɗansa, “Ka yi ƙarfin hali, ka kuma yi aikin. Kada ka ji tsoro ko ka fid da zuciya, gama Ubangiji Allah, Allahna, yana tare da kai. Ba zai bari ka ji kunya ko yă yashe ka ba, sai an gama dukan aikin saboda hidimar haikalin Ubangiji.
David also said to his son Solomon, “Be strong and courageous, and do this work. Do not be afraid or discouraged, because Yahweh our God will be with/helping you. He will not fail [to help] you or abandon you until you finish all the work of making his temple.
21 Sassan firistoci da na Lawiyawa suna a shirye domin dukan aiki a haikalin Allah, kuma kowane gwani mai niyya a kowace sana’a, zai taimake ka a cikin dukan aikin. Shugabanni da dukan mutane za su yi biyayya da kowane umarninka.”
The groups of priests and [other] descendants of Levi are ready to begin their work at the temple, and every man who has a special skill will help you in all the work. And my officials and the other people will obey you, whatever you command them to do.”

< 1 Tarihi 28 >