< 1 Tarihi 26 >
1 Ɓangarorin Matsaran Ƙofofi su ne, Daga Korayawa, Meshelemiya ɗan Kore, ɗaya daga cikin’ya’yan Asaf maza.
En ce qui concerne les subdivisions des portiers, les Korahites étaient représentés par Mechélémiahou, fils de Korê, des enfants d’Assaph.
2 Meshelemiya yana da’ya’ya maza. Zakariya ɗan fari, Yediyayel na biyu, Zebadiya na uku, Yatniyel na huɗu,
Mechélémiahou avait pour fils Zekhariahou, l’aîné, Yediaël, le second, Zebadiahou, le troisième, Yatniël, le quatrième,
3 Elam na biyar, Yehohanan na shida da Eliyehoyenai na bakwai.
Elam, le cinquième, Johanan, le sixième, Elyehoênaï, le septième.
4 Obed-Edom shi ma yana da’ya’ya maza. Shemahiya ɗan fari, Yehozabad na biyu, Yowa na uku, Sakar na huɗu Netanel na biyar,
Obed-Edom avait pour fils Chemaeya, rainé, Yozabad, le second, Yoah, le troisième, Sakhar, le quatrième, Netanel, le cinquième,
5 Ammiyel na shida, Issakar na bakwai da Feyuletai na takwas. (Gama Allah ya albarkace Obed-Edom.)
Ammiël, le sixième, Issachar, le septième, Peoultaï, le huitième; car Dieu l’avait béni.
6 Ɗan Obed-Edom, wato, Shemahiya shi ma yana da’ya’ya maza, waɗanda suke shugabanni a cikin iyalin mahaifinsu, gama su jarumawa ne ƙwarai.
A son fils Chemaeya il naquit des fils, qui eurent la direction de leur maison paternelle, car c’étaient des gens vaillants.
7 ’Ya’yan Shemahiya maza su ne, Otni, Rafayel, Obed da Elzabad; danginsa Elihu da Shemahiya su ma jarumawa ne.
Les fils de Chemaeya furent: Otni, Raphaël, Obed, Elzabad et ses frères des hommes vaillants Elihou et Semakhiahou.
8 Ɗaukan waɗannan zuriyar Obed-Edom ne; su da’ya’yansu maza da danginsu, jarumawa ne masu ƙarfin yin aiki. Zuriyar Obed-Edom, mutum 62 ne duka.
Tous ceux-ci, de la progéniture d’Obed-Edom, eux, leurs fils et leurs frères étaient des hommes vaillants
9 Meshelemiya yana da’ya’ya maza da kuma’yan’uwa, waɗanda jarumawa ne, su 18 ne duka.
Mechélémiahou avait des fils et des frères hommes vaillants au nombre de dix-huit.
10 Hosa dangin Merari yana da’ya’ya maza. Shimri na fari (ko da yake ba shi ne ɗan fari ba, mahaifinsa ya sa shi na fari),
Hossa, descendant de Merari, avait des fils, dont Chimri était le chef; car à défaut d’un fils aîné son père l’avait établi chef.
11 Hilkiya ne na biyu, Tabaliya ne na uku sai kuma Zakariya na huɗu.’Ya’ya da dangin Hosa su 13 ne duka.
Hilkiyahou était le second, Tebaliahou le troisième, Zekhariahou le quatrième: fils et frères de Hossa étaient ensemble treize.
12 Waɗannan ɓangarori na matsaran ƙofofi, ta wurin manyansu, suna da ayyukan yin hidima a haikalin Ubangiji, kamar yadda danginsu suke da shi.
A ces sections de portiers, à ces chefs de groupes d’hommes incombait la tâche de faire le service dans le temple de l’Eternel, concurremment avec leurs frères.
13 Aka jefa ƙuri’u don kowace ƙofa bisa ga iyalansu, ƙarami da babba.
On désigna, par la voie du sort, petits et grands, d’après leurs familles, pour la garde de chacune des portes.
14 Ƙuri’a don Ƙofar Gabas ta fāɗo a kan Shelemiya. Sai aka jefa ƙuri’u don ɗansa Zakariya, mai ba da shawara mai ma’ana, sai ƙuri’a ta ƙofar arewa ta fāɗo a kansa.
Le sort attribua à Chélémiahou le côté Est; quant à son fils Zekhariahou, conseiller avisé, on consulta le sort, qui le désigna pour le côté Nord.
15 Ƙuri’a don Ƙofar Kudu ta fāɗo a kan Obed-Edom, ƙuri’a don ɗakin ajiya kuwa ta fāɗo a kan’ya’yansa maza.
Obed-Edom eut la garde du côté Sud, ses fils celle du dépôt des magasins.
16 Ƙuri’u don Ƙofar Yamma da kuma Ƙofar Shalleket a hanyar bisa suka fāɗo a kan Shuffim da Hosa. Aikin tsaro bisa ga mai tsaro.
Chouppim et Hossa eurent le côté Ouest, ainsi que la porte de Challékhet, sur la chaussée montante: un poste faisait face à l’autre.
17 Akwai Lawiyawa shida da suke tsaron ƙofar gabas, huɗu a ƙofar kudu, huɗu kuma a ƙofar arewa, biyu-biyu suke tsaron ɗakunan ajiya.
Six Lévites étaient postés du côté de l’Est, quatre par jour du côté du Nord, quatre par jour du côté du Midi; les magasins étaient gardés par deux groupes de deux.
18 Game da filin waje ta yamma kuwa, akwai masu tsaro huɗu a hanya da kuma biyu a filin kansa.
Quant au Parbar à l’Ouest, quatre gardaient la chaussée montante et deux le Parbar.
19 Waɗannan su ne ɓangarori na matsaran ƙofofi waɗanda suke zuriyar Kora da Merari.
Telles étaient les subdivisions des portiers, pour les Korahites et les Merarites.
20 ’Yan’uwansu Lawiyawa kuwa su ne suke lura da ma’ajin gidan Allah da kuma baitulmali don kayayyakin da aka keɓe.
Quant aux Lévites, leurs frères, préposés aux trésors du temple de Dieu et aux trésors des choses saintes,
21 Ladan ɗan Gershon ne, kuma kaka ga iyalai masu yawa, har ma da iyalin ɗansa Yehiyeli,
c’étaient les fils de Laedân, descendants de Gerson par Laedân, les chefs de famille de Laedân, le Gersonite, les Yehiêlites.
22 ’ya’yan Yehiyeli maza su ne, Zetam da ɗan’uwansa Yowel. Su ne suke kula da ma’ajin haikalin Ubangiji.
Les descendants de Yehiël, Zêtam et Joël étaient commis à la garde des trésors du temple de l’Eternel.
23 Daga zuriyar Amram, Izhar, mutanen Hebron da kuma Uzziyel, su ma aka ba su aiki.
En ce qui concerne les descendants d’Amram, Yiçhar, Hébron et Ouzziel,
24 Shebuwel ɗan Gershom, daga zuriyar Musa, shi ne babban jami’i mai lura da baitulmali.
Chebouël, fils de Gerson, fils de Moïse, était intendant des trésors.
25 Danginsa na wajen Eliyezer su ne, Rehabiya, Yeshahiya, Yoram, Zikri da Shelomit.
Et ses frères, par Eliézer, étaient Rehabiahou, fils de ce dernier, Isaïe, son fils, Joram, son fils, Zikhri, son fils, et Chelomit, son fils.
26 Shelomit da danginsa su ne suke lura da dukan baitulmali don kayayyakin da Sarki Dawuda ya keɓe, ta wajen kawunan iyalai waɗanda suke shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, da kuma wajen sauran shugabannin mayaƙa.
Ce Chelomit et ses frères étaient préposés à tous les trésors d’objets saints qu’avaient consacrés le roi David, les chefs des familles, chiliarques et centurions, les chefs de l’armée.
27 Sun keɓe waɗansu ganimar da aka kwaso a yaƙi don gyaran haikalin Ubangiji.
C’Est sur le butin de guerre qu’ils les avaient consacrés en vue d’édifier le temple de l’Eternel.
28 Shelomit da’yan’uwansa suka lura da dukan abubuwan da annabi Sama’ila da Shawulu ɗan Kish, da Abner ɗan Ner, da Yowab ɗan Zeruhiya suka keɓe.
De même, tout ce qu’avaient consacré Samuel, le voyant, Saül, fils de Kich, Abner, fils de Ner, et Joab, fils de Cerouya, en un mot, tous les consécrateurs, était confié à la garde de Chelomit et de ses frères.
29 Daga mutanen Izhar, Kenaniya da’ya’yansa maza su aka sa a ayyukan da ba na haikali ba, su suka zama manya da kuma alƙalai a bisa Isra’ila.
Dans la famille de Yiçhar, Kenaniahou et ses fils étaient préposés à la besogne extérieure en Israël, comme prévôts et comme juges.
30 Daga zuriyar Hebron, Hashabiya da danginsa, su jarumawa dubu ɗaya da ɗari bakwai ne, su suke lura da Isra’ila yamma da Urdun don dukan aikin Ubangiji da kuma hidimar sarki.
Parmi les Hébronites, Hachabiahou et ses frères, tous hommes vaillants, au nombre de mille sept cents, étaient chargés des affaires d’Israël en deçà du Jourdain, à l’Ouest, en tout ce qui avait trait au service de l’Eternel et au service du roi.
31 Game da zuriyar Hebron kuwa, Yeriya ne babba bisa ga tarihin zuriyar iyalansu. A shekara ta arba’in ta sarautar Dawuda, sai aka yi binciken tarihi, aka tarar jarumawa cikin zuriyar Hebron suna zama a Yazer cikin Gileyad ne.
De ces Hébronites Yeriya était le chef, eu égard à la généalogie par familles de Hébron (ce fut dans la quarantième année du règne de David qu’on fit des recherches sur eux: il se trouva parmi eux des hommes vaillants à Yazer en Galaad).
32 Yeriya yana da’yan’uwa guda dubu biyu da ɗari bakwai, jarumawa da kuma kawunan iyalai, sai Sarki Dawuda ya sa su lura da mutanen Ruben, Gad da rabin kabilar Manasse game da kome da ya shafi Allah da kuma al’amuran sarki.
Et ses frères étaient des hommes de courage, au nombre de deux mille sept cents chefs de famille. Le roi David les mit à la tête des tribus de Ruben, de Gad et de la demi-tribu de Manassé, pour veiller à tous les intérêts de Dieu et aux intérêts du roi.