< 1 Tarihi 24 >
1 Waɗannan su ne sassan’ya’yan Haruna maza.’Ya’yan Haruna maza su ne Nadab, Abihu, Eleyazar da Itamar.
Folgendes sind die Abteilungen der Söhne Aarons: Die Söhne Aarons waren: Nadab und Abihu, Eleasar und Itamar.
2 Amma Nadab da Abihu sun mutu kafin mahaifinsu, ba su kuma haifi’ya’ya maza ba; saboda haka Eleyazar da Itamar suka yi hidimar firistoci.
Aber Nadab und Abihu starben vor dem Angesicht ihres Vaters und hatten keine Kinder; und Eleasar und Itamar wurden Priester.
3 Tare da taimakon Zadok zuriyar Eleyazar da Ahimelek wani zuriyar Itamar. Dawuda ya karkasa su zuwa ɓangarori don aikinsu bisa ga hidima.
Und David teilte sie, zusammen mit Zadok, aus den Söhnen Eleasars, und mit Achimelech, aus den Söhnen Itamars, in ihre Dienstklassen ein.
4 Akwai ɗumbun shugabanni a cikin zuriyar Eleyazar fiye da zuriyar Itamar, aka kuma karkasa su haka, kawuna goma sha shida daga zuriyar Eleyazar da kuma kawuna iyalai takwas daga zuriyar Itamar.
Es fand sich aber, daß die Söhne Eleasars an Familienhäuptern zahlreicher waren als die Söhne Itamars. Daher teilte man sie so ein, daß sechzehn Familienhäupter auf die Söhne Eleasars, und acht auf die Söhne Itamars kamen.
5 Aka karkasa su babu sonkai ta wurin jifa ƙuri’a, gama akwai manyan ma’aikatan wuri mai tsarki da manyan ma’aikatan Allah a cikin zuriyar Eleyazar da Itamar.
Und zwar teilte man sie durchs Los ein, die einen wie die andern, denn es gab sowohl unter den Söhnen Eleasars als auch unter den Söhnen Itamars «Fürsten des Heiligtums» und «Fürsten Gottes».
6 Shemahiya ɗan Netanel, wani Balawe ne marubuci, ya rubuta sunayensu a gaban sarki da kuma a gaban manyan ma’aikata. Zadok firist, Ahimelek ɗan Abiyatar da kuma kawunan iyalan firistoci da na Lawiyawa, iyali guda daga Eleyazar, guda kuma daga Itamar.
Und Semaja, der Schreiber, der Sohn Nataneels, aus den Leviten, schrieb sie auf vor dem König und vor den Obersten und vor Zadok, dem Priester, und vor Achimelech, dem Sohn Abjatars, und vor den Familienhäuptern unter den Priestern und Leviten; je ein Vaterhaus ward ausgelost von Eleasar und je eines ward ausgelost von Itamar.
7 Ƙuri’a ta farko ta faɗa a kan Yehoyarib, na biyu a kan Yedahiya,
Und das erste Los fiel auf Jojarib, das zweite auf Jedaja,
8 na uku a kan Harim, na huɗu a kan Seyorim,
das dritte auf Harim, das vierte auf Seorim,
9 na biyar a kan Malkiya, na shida a kan Miyamin,
das fünfte auf Malchija, das sechste auf Mijamin,
10 na bakwai a kan Hakkoz, na takwas a kan Abiya,
das siebente auf Hakkoz, das achte auf Abija,
11 na tara a kan Yeshuwa, na goma a kan Shekaniya,
das neunte auf Jesua, das zehnte auf Sechanja,
12 na goma sha ɗaya a kan Eliyashib, na goma sha biyu a kan Yakim,
das elfte auf Eljaschib, das zwölfte auf Jakim,
13 na goma sha uku a kan Huffa, na goma sha huɗu a kan Yeshebeyab,
das dreizehnte auf Huppa, das vierzehnte auf Jeschebab,
14 na goma sha biyar a kan Bilga, na goma sha shida a kan Immer,
das fünfzehnte auf Bilga, das sechzehnte auf Immer,
15 na goma sha shida a kan Hezir, na goma sha takwas a kan Haffizzez,
das siebzehnte auf Hesir, das achtzehnte auf Happizaz.
16 na goma sha tara a kan Fetahahiya, na ashirin a kan Ezekiyel,
Das neunzehnte auf Petachja, das zwanzigste auf Jecheskel,
17 na ashirin da ɗaya wa Yakin, na ashirin da biyu a kan Gamul,
das einundzwanzigste auf Jachin, das zweiundzwanzigste auf Gamul,
18 na ashirin da uku wa Delahiya da kuma na ashirin da huɗu a kan Ma’aziya.
das dreiundzwanzigste auf Delaja, das vierundzwanzigste auf Maasja.
19 Ga tsarin aikinsu na hidima sa’ad da suka shiga haikalin Ubangiji, bisa ga ƙa’idar da kakansu Haruna ya kafa, yadda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya umarce shi.
Das ist die Reihenfolge ihres Dienstes, nach welcher sie in das Haus des HERRN zu gehen haben nach ihrer Ordnung, [gegeben] durch ihren Vater Aaron, wie ihm der HERR, der Gott Israels, geboten hatte.
20 Game da sauran zuriyar Lawi kuwa, Daga’ya’yan Amram maza. Shubayel; daga’ya’yan Shubayel maza. Yedehiya.
Aber betreffs der übrigen Söhne Levis war unter den Söhnen Amrams Schubael. Unter den Söhnen Schubaels war Jechdeja.
21 Game da Rehabiya kuwa, daga’ya’yansa maza. Isshiya shi ne na fari.
Von Rechabja: Unter den Söhnen Rechabjas war Jischia das Oberhaupt.
22 Daga mutanen Izhar, Shelomot; daga’ya’yan Shelomot maza, Yahat.
Unter den Jizharitern war Selomot. Unter den Söhnen Selomots war Jachat.
23 ’Ya’yan Hebron maza su ne, Yeriya na fari, Amariya na biyu, Yahaziyel na uku da Yekameyam na huɗu.
Die Söhne [Hebrons] waren: Jeria, das Oberhaupt; Amarja, der zweite; Jahasiel, der dritte; Jekameam, der vierte.
24 Ɗan Uzziyel shi ne, Mika; daga’ya’yan Mika maza, Shamir.
Die Söhne Ussiels waren: Micha. Unter den Söhnen Michas war Samir.
25 Ɗan’uwan Mika shi ne, Isshiya; daga’ya’yan Isshiya maza, Zakariya.
Der Bruder Michas war Jischia. Unter den Söhnen Jischias war Sacharja.
26 ’Ya’yan Merari su ne, Mali da Mushi. Ɗan Ya’aziya shi ne, Beno.
Die Söhne Meraris waren: Machli und Muschi.
27 ’Ya’yan Merari su ne, daga Ya’aziya, Beno, Shoham, Zakkur da Ibri.
Die Söhne Jaasias: Beno, die Söhne Meraris von Jaasia waren: Beno, Soham, Sakkur und Ibri.
28 Daga Mali, Eleyazar, wanda ba shi da’ya’ya maza.
Von Machli aber war Eleasar; und dieser hatte keine Söhne;
29 Daga Kish, ɗan Kish shi ne, Yerameyel.
von Kis: unter den Söhnen des Kis war Jerachmeel.
30 Kuma’ya’yan Mushi maza su ne, Mali, Eder da Yerimot. Waɗannan su ne Lawiyawa bisa ga iyalansu.
Die Söhne Muschis waren: Machli, Eder und Jerimot. Das sind die Söhne der Leviten nach ihren Vaterhäusern.
31 Suka kuma jifa ƙuri’a, kamar dai yadda’yan’uwansu zuriyar Haruna suka yi, a gaban Sarki Dawuda da gaban Zadok, Ahimelek, da kuma a gaban kawunan iyalan firistoci da na Lawiyawa. Aka yi da iyalan wa daidai da iyalan ƙane.
Und auch sie warfen Lose gleich wie ihre Brüder, die Söhne Aarons, vor dem König David und vor Zadok und Achimelech und vor den Familienhäuptern der Priester und Leviten, und zwar die Familienhäupter ganz gleich wie ihre jüngeren Brüder.