< 1 Tarihi 24 >

1 Waɗannan su ne sassan’ya’yan Haruna maza.’Ya’yan Haruna maza su ne Nadab, Abihu, Eleyazar da Itamar.
Auch die Aaronssöhne hatten ihre Abteilungen. Die Aaronssöhne waren Nadab, Abihu, Eleazar und Itamar.
2 Amma Nadab da Abihu sun mutu kafin mahaifinsu, ba su kuma haifi’ya’ya maza ba; saboda haka Eleyazar da Itamar suka yi hidimar firistoci.
Nadab und Abihu aber starben vor ihrem Vater, ohne Söhne zu hinterlassen. So wurden Eleazar und Itamar Priester.
3 Tare da taimakon Zadok zuriyar Eleyazar da Ahimelek wani zuriyar Itamar. Dawuda ya karkasa su zuwa ɓangarori don aikinsu bisa ga hidima.
David teilte sie mit Sadok von Eleazars Söhnen und mit Achimelek von den Söhnen Itamars je nach ihrem Amt in ihren Dienst ein.
4 Akwai ɗumbun shugabanni a cikin zuriyar Eleyazar fiye da zuriyar Itamar, aka kuma karkasa su haka, kawuna goma sha shida daga zuriyar Eleyazar da kuma kawuna iyalai takwas daga zuriyar Itamar.
Nun waren Eleazars Söhne in den Sippenhäuptern zahlreicher als Itamars Söhne. Sie teilten sich so, daß auf Eleazars Söhne sechzehn und auf die Itamars acht Familienhäupter kamen.
5 Aka karkasa su babu sonkai ta wurin jifa ƙuri’a, gama akwai manyan ma’aikatan wuri mai tsarki da manyan ma’aikatan Allah a cikin zuriyar Eleyazar da Itamar.
Sie teilten sie durch das Los, die einen wie die anderen. Denn es gab Fürsten des Heiligtums und Fürsten Gottes sowohl bei Eleazars als bei Itamars Söhnen.
6 Shemahiya ɗan Netanel, wani Balawe ne marubuci, ya rubuta sunayensu a gaban sarki da kuma a gaban manyan ma’aikata. Zadok firist, Ahimelek ɗan Abiyatar da kuma kawunan iyalan firistoci da na Lawiyawa, iyali guda daga Eleyazar, guda kuma daga Itamar.
Und Netanels Sohn, Semaja, der Schreiber aus der Levitenzahl, schrieb sie vor dem König, den Fürsten und dem Priester Sadok auf. Je eine Familie wurde dabei von Itamar und je zwei von Eleazar ausgelost.
7 Ƙuri’a ta farko ta faɗa a kan Yehoyarib, na biyu a kan Yedahiya,
Das erste Los fiel auf Jojarib, das zweite auf Jedaja,
8 na uku a kan Harim, na huɗu a kan Seyorim,
das dritte auf Charim, das vierte auf Seorim,
9 na biyar a kan Malkiya, na shida a kan Miyamin,
das fünfte auf Malkia, das sechste auf Mijjamin,
10 na bakwai a kan Hakkoz, na takwas a kan Abiya,
das siebte auf Hakkos, das achte auf Abia,
11 na tara a kan Yeshuwa, na goma a kan Shekaniya,
das neunte auf Jesua, das zehnte auf Sekanjahu,
12 na goma sha ɗaya a kan Eliyashib, na goma sha biyu a kan Yakim,
das elfte auf Eljasib, das zwölfte auf Jakin,
13 na goma sha uku a kan Huffa, na goma sha huɗu a kan Yeshebeyab,
das dreizehnte auf Chuppa, das vierzehnte auf Jeseb,
14 na goma sha biyar a kan Bilga, na goma sha shida a kan Immer,
das fünfzehnte auf Bilga, das sechzehnte auf Immer,
15 na goma sha shida a kan Hezir, na goma sha takwas a kan Haffizzez,
das siebzehnte auf Chezir, das achtzehnte auf Happisses,
16 na goma sha tara a kan Fetahahiya, na ashirin a kan Ezekiyel,
das neunzehnte auf Petachja, das zwanzigste auf Jechezkel,
17 na ashirin da ɗaya wa Yakin, na ashirin da biyu a kan Gamul,
das einundzwanzigste auf Jakin, das zweiundzwanzigste auf Gamul,
18 na ashirin da uku wa Delahiya da kuma na ashirin da huɗu a kan Ma’aziya.
das dreiundzwanzigste auf Delaja und das vierundzwanzigste auf Maazja.
19 Ga tsarin aikinsu na hidima sa’ad da suka shiga haikalin Ubangiji, bisa ga ƙa’idar da kakansu Haruna ya kafa, yadda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya umarce shi.
Das war ihre Amtsordnung für ihren Dienst, der darin bestand, daß sie des Herrn Haus nach der ihnen von ihrem Vater Aaron gegebenen Vorschrift betraten, wie es ihm der Herr, Israels Gott, geboten hatte.
20 Game da sauran zuriyar Lawi kuwa, Daga’ya’yan Amram maza. Shubayel; daga’ya’yan Shubayel maza. Yedehiya.
Was die übrigen Levisöhne betrifft, so stammte von Amrams Söhnen Subael her, von Subaels Söhnen Iechdejahu,
21 Game da Rehabiya kuwa, daga’ya’yansa maza. Isshiya shi ne na fari.
von Rechabjahu, und zwar den Rechabjahusöhnen, das Oberhaupt Issia,
22 Daga mutanen Izhar, Shelomot; daga’ya’yan Shelomot maza, Yahat.
von den Ishariten Selomot, von Selomots Söhnen Jachat.
23 ’Ya’yan Hebron maza su ne, Yeriya na fari, Amariya na biyu, Yahaziyel na uku da Yekameyam na huɗu.
Jerias Söhne sind Amarja, der zweite, Jachaziel, der dritte, und Jekaman, der vierte.
24 Ɗan Uzziyel shi ne, Mika; daga’ya’yan Mika maza, Shamir.
Uzziels Söhne sind: Mika, von Mikas Söhnen Samir.
25 Ɗan’uwan Mika shi ne, Isshiya; daga’ya’yan Isshiya maza, Zakariya.
Mikas Bruder ist Issia; von den Söhnen Issias Zakarja.
26 ’Ya’yan Merari su ne, Mali da Mushi. Ɗan Ya’aziya shi ne, Beno.
Meraris Söhne sind Machli und Musi, die Söhne seines Sohnes Jaazia.
27 ’Ya’yan Merari su ne, daga Ya’aziya, Beno, Shoham, Zakkur da Ibri.
Meraris Söhne von seinem Sohn Jaaziahu sind Soham, Zakkur und Ibri.
28 Daga Mali, Eleyazar, wanda ba shi da’ya’ya maza.
Von Machli stammte Eleazar. Dieser hatte keine Söhne.
29 Daga Kish, ɗan Kish shi ne, Yerameyel.
Von Kis: die Söhne des Kis: Jerachmeel.
30 Kuma’ya’yan Mushi maza su ne, Mali, Eder da Yerimot. Waɗannan su ne Lawiyawa bisa ga iyalansu.
Des Musi Söhne sind Machli, Eder und Jerimot. Dies sind die Levitensöhne nach ihren Familien.
31 Suka kuma jifa ƙuri’a, kamar dai yadda’yan’uwansu zuriyar Haruna suka yi, a gaban Sarki Dawuda da gaban Zadok, Ahimelek, da kuma a gaban kawunan iyalan firistoci da na Lawiyawa. Aka yi da iyalan wa daidai da iyalan ƙane.
Auch sie warfen Lose, wie ihre Brüder, die Söhne Aarons, vor König David, vor Sadok und Achimelek sowie vor den Familienhäuptern der Priester und Leviten, die Familienhäupter ebenso wie ihre jüngeren Brüder.

< 1 Tarihi 24 >