< 1 Tarihi 24 >

1 Waɗannan su ne sassan’ya’yan Haruna maza.’Ya’yan Haruna maza su ne Nadab, Abihu, Eleyazar da Itamar.
Or voici quelle fut la classification des fils d’Aaron. Les fils d’Aaron étaient Nadab, Abiu, Eléazar et Ithamar.
2 Amma Nadab da Abihu sun mutu kafin mahaifinsu, ba su kuma haifi’ya’ya maza ba; saboda haka Eleyazar da Itamar suka yi hidimar firistoci.
Mais Nadab et Abiu moururent avant leur père, sans enfants; et Eléazar et Ithamar exercèrent les fonctions du sacerdoce.
3 Tare da taimakon Zadok zuriyar Eleyazar da Ahimelek wani zuriyar Itamar. Dawuda ya karkasa su zuwa ɓangarori don aikinsu bisa ga hidima.
David les divisa donc, c’est-à-dire Sadoc, d’entre les fils d’Eléazar, et Ahimélech, d’entre les fils d’Ithamar, selon leurs classes et leur ministère.
4 Akwai ɗumbun shugabanni a cikin zuriyar Eleyazar fiye da zuriyar Itamar, aka kuma karkasa su haka, kawuna goma sha shida daga zuriyar Eleyazar da kuma kawuna iyalai takwas daga zuriyar Itamar.
Mais il se trouva beaucoup plus de fils d’Eléazar parmi les princes, que de fils d’Ithamar. Il leur répartit donc, savoir: aux fils d’Eléazar, seize princes, selon leurs familles, et aux fils d’Ithamar, selon leurs familles et leurs maisons, huit.
5 Aka karkasa su babu sonkai ta wurin jifa ƙuri’a, gama akwai manyan ma’aikatan wuri mai tsarki da manyan ma’aikatan Allah a cikin zuriyar Eleyazar da Itamar.
Il partagea encore l’une et l’autre famille au sort; car il y avait des princes du sanctuaire, et des princes de Dieu, tant d’entre les fils d’Eléazar, que d’entre les fils d’Ithamar.
6 Shemahiya ɗan Netanel, wani Balawe ne marubuci, ya rubuta sunayensu a gaban sarki da kuma a gaban manyan ma’aikata. Zadok firist, Ahimelek ɗan Abiyatar da kuma kawunan iyalan firistoci da na Lawiyawa, iyali guda daga Eleyazar, guda kuma daga Itamar.
Séméias, fils de Nathanaël, le scribe de la tribu de Lévi, les enregistra devant le roi, les princes, Sadoc, le prêtre, Ahimélech, fils d’Abiathar, et devant les princes des familles sacerdotales et lévitiques, prenant une maison qui était à la tête des autres, celle d’Eléazar, et une autre maison qui avait sous elle les autres, celle d’Ithamar.
7 Ƙuri’a ta farko ta faɗa a kan Yehoyarib, na biyu a kan Yedahiya,
Ainsi le premier sort sortit pour Joïarib; le second, pour Jédéi;
8 na uku a kan Harim, na huɗu a kan Seyorim,
Le troisième, pour Harim; le quatrième, pour Séorim;
9 na biyar a kan Malkiya, na shida a kan Miyamin,
Le cinquième, pour Melchia; le sixième, pour Maïman;
10 na bakwai a kan Hakkoz, na takwas a kan Abiya,
Le septième, pour Accos; le huitième, pour Abia;
11 na tara a kan Yeshuwa, na goma a kan Shekaniya,
Le neuvième, pour Jésua; le dixième, pour Séchénia;
12 na goma sha ɗaya a kan Eliyashib, na goma sha biyu a kan Yakim,
Le onzième, pour Eliasib; le douzième, pour Jacim;
13 na goma sha uku a kan Huffa, na goma sha huɗu a kan Yeshebeyab,
Le treizième, pour Hoppha; le quatorzième, pour Isbaab;
14 na goma sha biyar a kan Bilga, na goma sha shida a kan Immer,
Le quinzième, pour Belga; le seizième, pour Emmer;
15 na goma sha shida a kan Hezir, na goma sha takwas a kan Haffizzez,
Le dix-septième, pour Hézir; le dix-huitième, pour Aphsès;
16 na goma sha tara a kan Fetahahiya, na ashirin a kan Ezekiyel,
Le dix-neuvième, pour Phétéia; le vingtième, pour Hézéchiel;
17 na ashirin da ɗaya wa Yakin, na ashirin da biyu a kan Gamul,
Le vingt-unième, pour Jachin; le vingt-deuxième, pour Gamul;
18 na ashirin da uku wa Delahiya da kuma na ashirin da huɗu a kan Ma’aziya.
Le vingt-troisième, pour Dalaïau; le vingt-quatrième, pour Maaziaü.
19 Ga tsarin aikinsu na hidima sa’ad da suka shiga haikalin Ubangiji, bisa ga ƙa’idar da kakansu Haruna ya kafa, yadda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya umarce shi.
Telles sont leurs classes, selon leurs fonctions, afin qu’ils entrent dans la maison du Seigneur suivant le rite qui leur est prescrit, sous la main d’Aaron leur père, comme avait ordonné le Seigneur Dieu d’Israël.
20 Game da sauran zuriyar Lawi kuwa, Daga’ya’yan Amram maza. Shubayel; daga’ya’yan Shubayel maza. Yedehiya.
Quant aux autres fils de Lévi, d’entre les fils d’Amram, était Subaël, et d’entre les fils de Subaël, Jéhédéia.
21 Game da Rehabiya kuwa, daga’ya’yansa maza. Isshiya shi ne na fari.
De plus, d’entre les fils de Rohobia, le prince Jésias.
22 Daga mutanen Izhar, Shelomot; daga’ya’yan Shelomot maza, Yahat.
Or le fils d’Isaar était Salémoth, et le fils de Salémoth, Jaath,
23 ’Ya’yan Hebron maza su ne, Yeriya na fari, Amariya na biyu, Yahaziyel na uku da Yekameyam na huɗu.
Dont le fils Jériaü fut le premier; Amarias, le second; Jahaziel, le troisième; Jecmaan, le quatrième.
24 Ɗan Uzziyel shi ne, Mika; daga’ya’yan Mika maza, Shamir.
Le fils d’Oziel, Micha; le fils de Micha, Samir.
25 Ɗan’uwan Mika shi ne, Isshiya; daga’ya’yan Isshiya maza, Zakariya.
Le frère de Micha était Jésia, et le fils de Jésia, Zacharie;
26 ’Ya’yan Merari su ne, Mali da Mushi. Ɗan Ya’aziya shi ne, Beno.
Les fils de Mérari, Moholi et Musi; le fils d’Osiaü, Benno.
27 ’Ya’yan Merari su ne, daga Ya’aziya, Beno, Shoham, Zakkur da Ibri.
Le fils de Mérari fut encore Oziaü, ainsi que Soam, Zachur et Hébri;
28 Daga Mali, Eleyazar, wanda ba shi da’ya’ya maza.
Mais le fils de Moholi fut Eléazar, qui n’eut point d’enfants;
29 Daga Kish, ɗan Kish shi ne, Yerameyel.
Et le fils de Cis, Jéraméel.
30 Kuma’ya’yan Mushi maza su ne, Mali, Eder da Yerimot. Waɗannan su ne Lawiyawa bisa ga iyalansu.
Les fils de Musi furent Moholi, Eder et Jérimoth. Ce sont là les fils de Lévi, selon les maisons de leurs familles.
31 Suka kuma jifa ƙuri’a, kamar dai yadda’yan’uwansu zuriyar Haruna suka yi, a gaban Sarki Dawuda da gaban Zadok, Ahimelek, da kuma a gaban kawunan iyalan firistoci da na Lawiyawa. Aka yi da iyalan wa daidai da iyalan ƙane.
Or ceux-ci aussi, tant les grands que les petits, jetèrent les sorts, comme leurs frères, les fils d’Aaron, devant David, le roi, et devant Sadoc, Ahimélech, et les princes des familles sacerdotales et lévitiques: le sort les partagea tous également.

< 1 Tarihi 24 >