< 1 Tarihi 24 >
1 Waɗannan su ne sassan’ya’yan Haruna maza.’Ya’yan Haruna maza su ne Nadab, Abihu, Eleyazar da Itamar.
Quant aux enfants d'Aaron, voici leurs classes: Fils d'Aaron: Nadab, Abihu, Éléazar et Ithamar.
2 Amma Nadab da Abihu sun mutu kafin mahaifinsu, ba su kuma haifi’ya’ya maza ba; saboda haka Eleyazar da Itamar suka yi hidimar firistoci.
Mais Nadab et Abihu moururent avant leur père, et ils n'eurent point de fils; et Éléazar et Ithamar exercèrent la sacrificature.
3 Tare da taimakon Zadok zuriyar Eleyazar da Ahimelek wani zuriyar Itamar. Dawuda ya karkasa su zuwa ɓangarori don aikinsu bisa ga hidima.
Or David les distribua, selon leur classement dans leur service, Tsadok d'entre les enfants d'Éléazar, et Achimélec d'entre les enfants d'Ithamar.
4 Akwai ɗumbun shugabanni a cikin zuriyar Eleyazar fiye da zuriyar Itamar, aka kuma karkasa su haka, kawuna goma sha shida daga zuriyar Eleyazar da kuma kawuna iyalai takwas daga zuriyar Itamar.
Il se trouva parmi les enfants d'Éléazar plus de chefs que parmi les enfants d'Ithamar, et on les partagea ainsi: pour les enfants d'Éléazar seize chefs de maisons de pères, et pour les enfants d'Ithamar, huit chefs de maisons de pères.
5 Aka karkasa su babu sonkai ta wurin jifa ƙuri’a, gama akwai manyan ma’aikatan wuri mai tsarki da manyan ma’aikatan Allah a cikin zuriyar Eleyazar da Itamar.
On les classa par le sort, les uns avec les autres; car les chefs du sanctuaire et les chefs de la maison de Dieu étaient des enfants d'Éléazar et des enfants d'Ithamar.
6 Shemahiya ɗan Netanel, wani Balawe ne marubuci, ya rubuta sunayensu a gaban sarki da kuma a gaban manyan ma’aikata. Zadok firist, Ahimelek ɗan Abiyatar da kuma kawunan iyalan firistoci da na Lawiyawa, iyali guda daga Eleyazar, guda kuma daga Itamar.
Shémaja, le scribe, fils de Nathanael, de la tribu de Lévi, les inscrivit devant le roi et les princes, devant Tsadok, le sacrificateur, et Achimélec, fils d'Abiathar, et devant les chefs des pères des sacrificateurs et des Lévites. Une maison de père était tirée pour Éléazar, et une était tirée ensuite pour Ithamar.
7 Ƙuri’a ta farko ta faɗa a kan Yehoyarib, na biyu a kan Yedahiya,
Le premier sort échut à Jéhojarib; le second, à Jédaeja;
8 na uku a kan Harim, na huɗu a kan Seyorim,
Le troisième, à Harim; le quatrième, à Séorim;
9 na biyar a kan Malkiya, na shida a kan Miyamin,
Le cinquième, à Malkija; le sixième, à Mijamin;
10 na bakwai a kan Hakkoz, na takwas a kan Abiya,
Le septième, à Kots; le huitième, à Abija;
11 na tara a kan Yeshuwa, na goma a kan Shekaniya,
Le neuvième, à Jeshua; le dixième, à Shécania;
12 na goma sha ɗaya a kan Eliyashib, na goma sha biyu a kan Yakim,
Le onzième, à Éliashib; le douzième, à Jakim;
13 na goma sha uku a kan Huffa, na goma sha huɗu a kan Yeshebeyab,
Le treizième, à Huppa; le quatorzième, à Jéshébeab;
14 na goma sha biyar a kan Bilga, na goma sha shida a kan Immer,
Le quinzième, à Bilga; le seizième, à Immer;
15 na goma sha shida a kan Hezir, na goma sha takwas a kan Haffizzez,
Le dix-septième, à Hézir; le dix-huitième, à Pitsets;
16 na goma sha tara a kan Fetahahiya, na ashirin a kan Ezekiyel,
Le dix-neuvième, à Péthachia; le vingtième, à Ézéchiel;
17 na ashirin da ɗaya wa Yakin, na ashirin da biyu a kan Gamul,
Le vingt et unième, à Jakin; le vingt-deuxième, à Gamul;
18 na ashirin da uku wa Delahiya da kuma na ashirin da huɗu a kan Ma’aziya.
Le vingt-troisième, à Délaja; le vingt-quatrième, à Maazia.
19 Ga tsarin aikinsu na hidima sa’ad da suka shiga haikalin Ubangiji, bisa ga ƙa’idar da kakansu Haruna ya kafa, yadda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya umarce shi.
Tel fut leur classement pour leur service, pour entrer dans la maison de l'Éternel, selon leur règle, établie par Aaron, leur père, comme l'Éternel, le Dieu d'Israël, le lui avait ordonné.
20 Game da sauran zuriyar Lawi kuwa, Daga’ya’yan Amram maza. Shubayel; daga’ya’yan Shubayel maza. Yedehiya.
Quant au reste des enfants de Lévi, voici leurs chefs: Des fils d'Amram: Shubaël; et des fils de Shubaël: Jechdéja;
21 Game da Rehabiya kuwa, daga’ya’yansa maza. Isshiya shi ne na fari.
De Réchabia, des fils de Réchabia: le chef Jishija.
22 Daga mutanen Izhar, Shelomot; daga’ya’yan Shelomot maza, Yahat.
Des Jitseharites: Shélomoth; des fils de Shélomoth: Jachath.
23 ’Ya’yan Hebron maza su ne, Yeriya na fari, Amariya na biyu, Yahaziyel na uku da Yekameyam na huɗu.
Fils de Hébron: Jérija, Amaria le second, Jachaziel le troisième, Jékameam le quatrième.
24 Ɗan Uzziyel shi ne, Mika; daga’ya’yan Mika maza, Shamir.
Fils d'Uziel: Mica; des fils de Mica: Shamir.
25 Ɗan’uwan Mika shi ne, Isshiya; daga’ya’yan Isshiya maza, Zakariya.
Frère de Mica: Jishija; des fils de Jishija: Zacharie.
26 ’Ya’yan Merari su ne, Mali da Mushi. Ɗan Ya’aziya shi ne, Beno.
Fils de Mérari: Machli et Mushi, et les fils de Jaazija, son fils.
27 ’Ya’yan Merari su ne, daga Ya’aziya, Beno, Shoham, Zakkur da Ibri.
Fils de Mérari, de Jaazija, son fils: Shoham, Zaccur et Ibri.
28 Daga Mali, Eleyazar, wanda ba shi da’ya’ya maza.
De Machli: Éléazar qui n'eut point de fils;
29 Daga Kish, ɗan Kish shi ne, Yerameyel.
De Kis, les fils de Kis: Jérachméel.
30 Kuma’ya’yan Mushi maza su ne, Mali, Eder da Yerimot. Waɗannan su ne Lawiyawa bisa ga iyalansu.
Fils de Mushi: Machli, Éder et Jérimoth. Ce sont là les fils des Lévites, selon les maisons de leurs pères.
31 Suka kuma jifa ƙuri’a, kamar dai yadda’yan’uwansu zuriyar Haruna suka yi, a gaban Sarki Dawuda da gaban Zadok, Ahimelek, da kuma a gaban kawunan iyalan firistoci da na Lawiyawa. Aka yi da iyalan wa daidai da iyalan ƙane.
Eux aussi, comme leurs frères, les enfants d'Aaron, ils tirèrent au sort devant le roi David, Tsadok et Achimélec, et les chefs des pères des sacrificateurs et des Lévites. Le chef de maison de pères tira tout comme le moindre de ses frères.