< 1 Tarihi 24 >
1 Waɗannan su ne sassan’ya’yan Haruna maza.’Ya’yan Haruna maza su ne Nadab, Abihu, Eleyazar da Itamar.
Et quant aux fils d’Aaron, [voici] leurs classes: Fils d’Aaron: Nadab et Abihu, Éléazar et Ithamar.
2 Amma Nadab da Abihu sun mutu kafin mahaifinsu, ba su kuma haifi’ya’ya maza ba; saboda haka Eleyazar da Itamar suka yi hidimar firistoci.
Et Nadab et Abihu moururent avant leur père, et n’eurent point de fils. Et Éléazar et Ithamar exercèrent la sacrificature.
3 Tare da taimakon Zadok zuriyar Eleyazar da Ahimelek wani zuriyar Itamar. Dawuda ya karkasa su zuwa ɓangarori don aikinsu bisa ga hidima.
Et Tsadok, des fils d’Éléazar, et Akhimélec, des fils d’Ithamar, David les distribua en classes, selon leur office dans leur service:
4 Akwai ɗumbun shugabanni a cikin zuriyar Eleyazar fiye da zuriyar Itamar, aka kuma karkasa su haka, kawuna goma sha shida daga zuriyar Eleyazar da kuma kawuna iyalai takwas daga zuriyar Itamar.
et des fils d’Éléazar on trouva un plus grand nombre de chefs de famille que des fils d’Ithamar, et on les distribua en classes: des fils d’Éléazar, 16 chefs de maisons de pères; et des fils d’Ithamar, huit, selon leurs maisons de pères.
5 Aka karkasa su babu sonkai ta wurin jifa ƙuri’a, gama akwai manyan ma’aikatan wuri mai tsarki da manyan ma’aikatan Allah a cikin zuriyar Eleyazar da Itamar.
Et on les distribua en classes par le sort, les uns avec les autres; car les chefs du lieu saint et les chefs de Dieu furent d’entre les fils d’Éléazar et parmi les fils d’Ithamar.
6 Shemahiya ɗan Netanel, wani Balawe ne marubuci, ya rubuta sunayensu a gaban sarki da kuma a gaban manyan ma’aikata. Zadok firist, Ahimelek ɗan Abiyatar da kuma kawunan iyalan firistoci da na Lawiyawa, iyali guda daga Eleyazar, guda kuma daga Itamar.
Et Shemahia, fils de Nethaneël, le scribe, d’entre les Lévites, les inscrivit en la présence du roi, et des chefs, et de Tsadok, le sacrificateur, et d’Akhimélec, fils d’Abiathar, et des chefs des pères des sacrificateurs et des Lévites: une maison de père était tirée pour Éléazar, et une était tirée pour Ithamar.
7 Ƙuri’a ta farko ta faɗa a kan Yehoyarib, na biyu a kan Yedahiya,
Et le premier sort échut à Jehoïarib; le second, à Jedahia;
8 na uku a kan Harim, na huɗu a kan Seyorim,
le troisième, à Harim; le quatrième, à Seorim;
9 na biyar a kan Malkiya, na shida a kan Miyamin,
le cinquième, à Malkija; le sixième, à Mijamin;
10 na bakwai a kan Hakkoz, na takwas a kan Abiya,
le septième, à Kots; le huitième, à Abija;
11 na tara a kan Yeshuwa, na goma a kan Shekaniya,
le neuvième, à Jéshua; le dixième, à Shecania;
12 na goma sha ɗaya a kan Eliyashib, na goma sha biyu a kan Yakim,
le onzième, à Éliashib; le douzième, à Jakim;
13 na goma sha uku a kan Huffa, na goma sha huɗu a kan Yeshebeyab,
le treizième, à Huppa; le quatorzième, à Jéshébeab;
14 na goma sha biyar a kan Bilga, na goma sha shida a kan Immer,
le quinzième, à Bilga; le seizième, à Immer;
15 na goma sha shida a kan Hezir, na goma sha takwas a kan Haffizzez,
le dix-septième, à Hézir; le dix-huitième, à Pitsets;
16 na goma sha tara a kan Fetahahiya, na ashirin a kan Ezekiyel,
le dix-neuvième, à Pethakhia; le vingtième, à Ézéchiel;
17 na ashirin da ɗaya wa Yakin, na ashirin da biyu a kan Gamul,
le vingt et unième, à Jakin; le vingt-deuxième, à Gamul;
18 na ashirin da uku wa Delahiya da kuma na ashirin da huɗu a kan Ma’aziya.
le vingt-troisième, à Delaïa; le vingt-quatrième, à Maazia.
19 Ga tsarin aikinsu na hidima sa’ad da suka shiga haikalin Ubangiji, bisa ga ƙa’idar da kakansu Haruna ya kafa, yadda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya umarce shi.
Ce fut là leur distribution, pour leur service, pour entrer dans la maison de l’Éternel selon leur ordonnance [donnée] par Aaron, leur père, comme l’Éternel, le Dieu d’Israël, le lui avait commandé.
20 Game da sauran zuriyar Lawi kuwa, Daga’ya’yan Amram maza. Shubayel; daga’ya’yan Shubayel maza. Yedehiya.
Et quant au reste des fils de Lévi, [les voici]: Des fils d’Amram, Shubaël; des fils de Shubaël, Jekhdia.
21 Game da Rehabiya kuwa, daga’ya’yansa maza. Isshiya shi ne na fari.
De Rekhabia: des fils de Rekhabia, Jishija était le chef.
22 Daga mutanen Izhar, Shelomot; daga’ya’yan Shelomot maza, Yahat.
Des Jitseharites, Shelomoth; des fils de Shelomoth, Jakhath.
23 ’Ya’yan Hebron maza su ne, Yeriya na fari, Amariya na biyu, Yahaziyel na uku da Yekameyam na huɗu.
Et les fils de [Hébron]: Jerija; Amaria, le second; Jakhaziel, le troisième; Jekamham, le quatrième.
24 Ɗan Uzziyel shi ne, Mika; daga’ya’yan Mika maza, Shamir.
Les fils d’Uziel, Michée; des fils de Michée, Shamir;
25 Ɗan’uwan Mika shi ne, Isshiya; daga’ya’yan Isshiya maza, Zakariya.
le frère de Michée était Jishija; des fils de Jishija, Zacharie.
26 ’Ya’yan Merari su ne, Mali da Mushi. Ɗan Ya’aziya shi ne, Beno.
Les fils de Merari, Makhli et Mushi; les fils de Jaazija, son fils;
27 ’Ya’yan Merari su ne, daga Ya’aziya, Beno, Shoham, Zakkur da Ibri.
les fils de Merari, de Jaazija, son fils: Shoham, et Zaccur, et Ibri;
28 Daga Mali, Eleyazar, wanda ba shi da’ya’ya maza.
de Makhli, Éléazar, et il n’eut point de fils;
29 Daga Kish, ɗan Kish shi ne, Yerameyel.
de Kis, les fils de Kis, Jerakhmeël;
30 Kuma’ya’yan Mushi maza su ne, Mali, Eder da Yerimot. Waɗannan su ne Lawiyawa bisa ga iyalansu.
et les fils de Mushi: Makhli, et Éder, et Jerimoth. Ce sont là les fils des Lévites, selon leurs maisons de pères.
31 Suka kuma jifa ƙuri’a, kamar dai yadda’yan’uwansu zuriyar Haruna suka yi, a gaban Sarki Dawuda da gaban Zadok, Ahimelek, da kuma a gaban kawunan iyalan firistoci da na Lawiyawa. Aka yi da iyalan wa daidai da iyalan ƙane.
Et eux aussi, comme leurs frères, les fils d’Aaron, tirèrent au sort devant le roi David, et Tsadok, et Akhimélec, et les chefs des pères des sacrificateurs et des Lévites, les chefs des pères comme le plus petit d’entre leurs frères.