< 1 Tarihi 24 >
1 Waɗannan su ne sassan’ya’yan Haruna maza.’Ya’yan Haruna maza su ne Nadab, Abihu, Eleyazar da Itamar.
Forsothe to the sones of Aaron these porciouns schulen be; the sones of Aaron weren Nadab, and Abyud, Eleazar, and Ythamar;
2 Amma Nadab da Abihu sun mutu kafin mahaifinsu, ba su kuma haifi’ya’ya maza ba; saboda haka Eleyazar da Itamar suka yi hidimar firistoci.
but Nadab and Abyud weren deed with out fre children bifor her fadir, and Eleazar and Ythamar weren set in presthod.
3 Tare da taimakon Zadok zuriyar Eleyazar da Ahimelek wani zuriyar Itamar. Dawuda ya karkasa su zuwa ɓangarori don aikinsu bisa ga hidima.
And Dauith departide hem, that is, Sadoch, of the sones of Eleazar, and Achymelech, of the sones of Ithamar, by her whiles and seruyce;
4 Akwai ɗumbun shugabanni a cikin zuriyar Eleyazar fiye da zuriyar Itamar, aka kuma karkasa su haka, kawuna goma sha shida daga zuriyar Eleyazar da kuma kawuna iyalai takwas daga zuriyar Itamar.
and the sones of Eleazar weren founden many mo in the men princes, than the sones of Ythamar. Forsothe he departide to hem, that is, to the sones of Eleazar, sixtene prynces bi meynees; and to the sones of Ythamar eiyte prynces bi her meynees and howsis.
5 Aka karkasa su babu sonkai ta wurin jifa ƙuri’a, gama akwai manyan ma’aikatan wuri mai tsarki da manyan ma’aikatan Allah a cikin zuriyar Eleyazar da Itamar.
Sotheli he departide euer eithir meynees among hem silf bi lottis; for there weren princes of the seyntuarye, and princes of the hows of God, as wel of the sones of Eleazar as of the sones of Ithamar.
6 Shemahiya ɗan Netanel, wani Balawe ne marubuci, ya rubuta sunayensu a gaban sarki da kuma a gaban manyan ma’aikata. Zadok firist, Ahimelek ɗan Abiyatar da kuma kawunan iyalan firistoci da na Lawiyawa, iyali guda daga Eleyazar, guda kuma daga Itamar.
And Semeye, the sone of Nathanael, a scribe of the lynage of Leuy, discriuede hem bifore the king and pryncis, and bifor Sadoch, the preest, and Achymelech, the sone of Abiathar, and to the prynces of meynees of the preestis and of the dekenes; he discriuyde oon hows of Eleazar, that was souereyn to othere, and `the tother hows of Ithamar, that hadde othere vndir hym.
7 Ƙuri’a ta farko ta faɗa a kan Yehoyarib, na biyu a kan Yedahiya,
Forsothe the firste lot yede out to Joiarib, the secounde to Jedeie,
8 na uku a kan Harim, na huɗu a kan Seyorim,
the thridde to Aharym, the fourthe to Seorym,
9 na biyar a kan Malkiya, na shida a kan Miyamin,
the fyuethe to Melchie,
10 na bakwai a kan Hakkoz, na takwas a kan Abiya,
the sixte to Maynan, the seuenthe to Accos,
11 na tara a kan Yeshuwa, na goma a kan Shekaniya,
the eiythe to Abia, the nynthe to Hieusu, the tenthe to Sechema, the elleuenthe to Eliasib,
12 na goma sha ɗaya a kan Eliyashib, na goma sha biyu a kan Yakim,
the tweluethe to Jacyn,
13 na goma sha uku a kan Huffa, na goma sha huɗu a kan Yeshebeyab,
the thrittenthe to Opha, the fourtenthe to Isbaal,
14 na goma sha biyar a kan Bilga, na goma sha shida a kan Immer,
the fiftenthe to Abelga, the sixtenthe to Emmer,
15 na goma sha shida a kan Hezir, na goma sha takwas a kan Haffizzez,
the seuententhe to Ezir, the eiytenthe to Ahapses, the nyntenthe to Pheseye,
16 na goma sha tara a kan Fetahahiya, na ashirin a kan Ezekiyel,
the twentithe to Jezechel,
17 na ashirin da ɗaya wa Yakin, na ashirin da biyu a kan Gamul,
the oon and twentithe to Jachym, the two and twentithe to Gamul, the thre and twentithe to Dalayam,
18 na ashirin da uku wa Delahiya da kuma na ashirin da huɗu a kan Ma’aziya.
the foure and twentithe to Mazzian.
19 Ga tsarin aikinsu na hidima sa’ad da suka shiga haikalin Ubangiji, bisa ga ƙa’idar da kakansu Haruna ya kafa, yadda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya umarce shi.
These weren the whilis of hem bi her mynysteries, that thei entre in to the hows of God, and bi her custom vndur the hond of Aaron, her fadir, as the Lord God of Israel comaundide.
20 Game da sauran zuriyar Lawi kuwa, Daga’ya’yan Amram maza. Shubayel; daga’ya’yan Shubayel maza. Yedehiya.
Forsothe Sebahel was prince of the sones of Leuy that weren resydue, of the sones of Amram; and the sone of Sebahel was Jedeie;
21 Game da Rehabiya kuwa, daga’ya’yansa maza. Isshiya shi ne na fari.
also Jesie was prince of the sones of Roobie.
22 Daga mutanen Izhar, Shelomot; daga’ya’yan Shelomot maza, Yahat.
Sotheli Salomoth was prince of Isaaris; and the sone of Salamoth was Janadiath;
23 ’Ya’yan Hebron maza su ne, Yeriya na fari, Amariya na biyu, Yahaziyel na uku da Yekameyam na huɗu.
and his firste sone was Jeriuans, `Amarie the secounde, Azihel the thridde, `Jethmoan the fourthe.
24 Ɗan Uzziyel shi ne, Mika; daga’ya’yan Mika maza, Shamir.
The sone of Ozihel was Mycha; the sone of Mycha was Samyr;
25 Ɗan’uwan Mika shi ne, Isshiya; daga’ya’yan Isshiya maza, Zakariya.
the brother of Mycha was Jesia; and the sone of Jesia was Zacharie.
26 ’Ya’yan Merari su ne, Mali da Mushi. Ɗan Ya’aziya shi ne, Beno.
The sones of Merary weren Mooli and Musi; the sone of Josyan was Bennon;
27 ’Ya’yan Merari su ne, daga Ya’aziya, Beno, Shoham, Zakkur da Ibri.
and the sone of Merarie was Ozian, and Soen, and Zaccur, and Hebri.
28 Daga Mali, Eleyazar, wanda ba shi da’ya’ya maza.
Sotheli the sone of Mooli was Eleazar, that hadde not fre sones; forsothe the sone of Cys was Jeremyhel;
29 Daga Kish, ɗan Kish shi ne, Yerameyel.
the sones of Musy weren Mooli,
30 Kuma’ya’yan Mushi maza su ne, Mali, Eder da Yerimot. Waɗannan su ne Lawiyawa bisa ga iyalansu.
Eder, Jerymuth. These weren the sones of Leuy, bi the housis of her meynees.
31 Suka kuma jifa ƙuri’a, kamar dai yadda’yan’uwansu zuriyar Haruna suka yi, a gaban Sarki Dawuda da gaban Zadok, Ahimelek, da kuma a gaban kawunan iyalan firistoci da na Lawiyawa. Aka yi da iyalan wa daidai da iyalan ƙane.
Also and thei senten lottis ayens her britheren, the sones of Aaron, bifor Dauid the kyng, and bifor Sadoch, and Achymelech, and the princes of meynees of preestis and of dekenes; lot departide euenli alle, bothe the gretter and the lesse.