< 1 Tarihi 24 >

1 Waɗannan su ne sassan’ya’yan Haruna maza.’Ya’yan Haruna maza su ne Nadab, Abihu, Eleyazar da Itamar.
Now the divisions into which the sons of Aaron were grouped were these: the sons of Aaron, Nadab and Abihu, Eleazar and Ithamar.
2 Amma Nadab da Abihu sun mutu kafin mahaifinsu, ba su kuma haifi’ya’ya maza ba; saboda haka Eleyazar da Itamar suka yi hidimar firistoci.
But Nadab and Abihu came to their end before their father, and had no children; so Eleazar and Ithamar did the work of priests.
3 Tare da taimakon Zadok zuriyar Eleyazar da Ahimelek wani zuriyar Itamar. Dawuda ya karkasa su zuwa ɓangarori don aikinsu bisa ga hidima.
And David, with Zadok of the sons of Eleazar, and Ahimelech of the sons of Ithamar, made distribution of them into their positions for their work.
4 Akwai ɗumbun shugabanni a cikin zuriyar Eleyazar fiye da zuriyar Itamar, aka kuma karkasa su haka, kawuna goma sha shida daga zuriyar Eleyazar da kuma kawuna iyalai takwas daga zuriyar Itamar.
And there were more chiefs among the sons of Eleazar than among the sons of Ithamar; and this is how they were grouped: of the sons of Eleazar there were sixteen, all heads of families; and of the sons of Ithamar, heads of families, there were eight.
5 Aka karkasa su babu sonkai ta wurin jifa ƙuri’a, gama akwai manyan ma’aikatan wuri mai tsarki da manyan ma’aikatan Allah a cikin zuriyar Eleyazar da Itamar.
So they were put into groups, by the Lord's decision, one with another; for there were rulers of the holy place and rulers of the house of God among the sons of Eleazar and the sons of Ithamar.
6 Shemahiya ɗan Netanel, wani Balawe ne marubuci, ya rubuta sunayensu a gaban sarki da kuma a gaban manyan ma’aikata. Zadok firist, Ahimelek ɗan Abiyatar da kuma kawunan iyalan firistoci da na Lawiyawa, iyali guda daga Eleyazar, guda kuma daga Itamar.
And Shemaiah, the son of Nethanel the scribe, who was a Levite, put down their names in writing, the king being present with the rulers, and Zadok the priest, and Ahimelech, the son of Abiathar, and the heads of families of the priests and the Levites; one family being taken for Eleazar and then one for Ithamar, and so on.
7 Ƙuri’a ta farko ta faɗa a kan Yehoyarib, na biyu a kan Yedahiya,
Now the first name to come out was that of Jehoiarib; the second Jedaiah,
8 na uku a kan Harim, na huɗu a kan Seyorim,
The third Harim, the fourth Seorim,
9 na biyar a kan Malkiya, na shida a kan Miyamin,
The fifth Malchijah, the sixth Mijamin,
10 na bakwai a kan Hakkoz, na takwas a kan Abiya,
The seventh Hakkoz, the eighth Abijah,
11 na tara a kan Yeshuwa, na goma a kan Shekaniya,
The ninth Jeshua, the tenth Shecaniah,
12 na goma sha ɗaya a kan Eliyashib, na goma sha biyu a kan Yakim,
The eleventh Eliashib, the twelfth Jakim,
13 na goma sha uku a kan Huffa, na goma sha huɗu a kan Yeshebeyab,
The thirteenth Huppah, the fourteenth Jeshebeab,
14 na goma sha biyar a kan Bilga, na goma sha shida a kan Immer,
The fifteenth Bilgah, the sixteenth Immer,
15 na goma sha shida a kan Hezir, na goma sha takwas a kan Haffizzez,
The seventeenth Hezir, the eighteenth Happizzez,
16 na goma sha tara a kan Fetahahiya, na ashirin a kan Ezekiyel,
The nineteenth Pethahiah, the twentieth Jehezkel,
17 na ashirin da ɗaya wa Yakin, na ashirin da biyu a kan Gamul,
The twenty-first Jachin, the twenty-second Gamul,
18 na ashirin da uku wa Delahiya da kuma na ashirin da huɗu a kan Ma’aziya.
The twenty-third Delaiah, the twenty-fourth Maaziah.
19 Ga tsarin aikinsu na hidima sa’ad da suka shiga haikalin Ubangiji, bisa ga ƙa’idar da kakansu Haruna ya kafa, yadda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya umarce shi.
So they were put into their different groups, to take their places in the house of the Lord, in agreement with the rules made by Aaron their father, as the Lord, the God of Israel, had given him orders.
20 Game da sauran zuriyar Lawi kuwa, Daga’ya’yan Amram maza. Shubayel; daga’ya’yan Shubayel maza. Yedehiya.
And of the rest of the sons of Levi: of the sons of Amram, Shubael; of the sons of Shubael, Jehdeiah.
21 Game da Rehabiya kuwa, daga’ya’yansa maza. Isshiya shi ne na fari.
Of Rehabiah; of the sons of Rehabiah, Isshiah the chief.
22 Daga mutanen Izhar, Shelomot; daga’ya’yan Shelomot maza, Yahat.
Of the Izharites, Shelomoth; of the sons of Shelomoth, Jahath.
23 ’Ya’yan Hebron maza su ne, Yeriya na fari, Amariya na biyu, Yahaziyel na uku da Yekameyam na huɗu.
And the sons of Hebron: Jeriah the chief, Amariah the second, Jahaziel the third, Jekameam the fourth.
24 Ɗan Uzziyel shi ne, Mika; daga’ya’yan Mika maza, Shamir.
The sons of Uzziel, Micah; of the sons of Micah, Shamir.
25 Ɗan’uwan Mika shi ne, Isshiya; daga’ya’yan Isshiya maza, Zakariya.
The brother of Micah, Isshiah; of the sons of Isshiah, Zechariah.
26 ’Ya’yan Merari su ne, Mali da Mushi. Ɗan Ya’aziya shi ne, Beno.
The sons of Merari: Mahli and Mushi; the sons of Jaaziah.
27 ’Ya’yan Merari su ne, daga Ya’aziya, Beno, Shoham, Zakkur da Ibri.
The sons of Merari: of Jaaziah, Shoham and Zaccur and Ibri.
28 Daga Mali, Eleyazar, wanda ba shi da’ya’ya maza.
Of Mahli: Eleazar, who had no sons.
29 Daga Kish, ɗan Kish shi ne, Yerameyel.
Of Kish: the sons of Kish, Jerahmeel.
30 Kuma’ya’yan Mushi maza su ne, Mali, Eder da Yerimot. Waɗannan su ne Lawiyawa bisa ga iyalansu.
And the sons of Mushi: Mahli and Eder and Jerimoth. These were the sons of the Levites by their families.
31 Suka kuma jifa ƙuri’a, kamar dai yadda’yan’uwansu zuriyar Haruna suka yi, a gaban Sarki Dawuda da gaban Zadok, Ahimelek, da kuma a gaban kawunan iyalan firistoci da na Lawiyawa. Aka yi da iyalan wa daidai da iyalan ƙane.
Selection was made of these in the same way as of their brothers the sons of Aaron, David the king being present, with Zadok, and Ahimelech, and the heads of families of the priests and of the Levites; the families of the chief in the same way as those of his younger brother.

< 1 Tarihi 24 >