< 1 Tarihi 23 >
1 Sa’ad da Dawuda ya tsufa yana kuma da cikakken shekaru, ya sa ɗansa Solomon sarki bisa Isra’ila.
Et David était vieux et rassasié de jours, et il établit Salomon, son fils, roi sur Israël.
2 Ya kuma tattara dukan shugabannin Isra’ila a wuri ɗaya, haka kuma ya yi da firistoci da Lawiyawa.
Et il assembla tous les chefs d’Israël, et les sacrificateurs, et les Lévites.
3 Aka ƙidaya Lawiyawan da suke’yan shekaru talatin da haihuwa ko fiye, suka kai wajen mutum dubu talatin da takwas.
Et on dénombra les Lévites, depuis l’âge de 30 ans et au-dessus; et leur nombre, par tête, par homme, fut de 38 000.
4 Dawuda ya ce, “Cikin waɗannan, dubu ashirin da huɗu za su lura da aikin haikalin Ubangiji, dubu shida su zama manyan na ma’aikata da alƙalai.
Il y en eut d’entre eux 24 000 pour diriger l’œuvre de la maison de l’Éternel, et 6 000 intendants et juges,
5 Dubu huɗu su zama matsaran ƙofofi, dubu huɗu kuma su yabi Ubangiji da kayayyakin bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe waɗanda na tanada saboda wannan manufa.”
et 4 000 portiers, et 4 000 qui louaient l’Éternel avec les instruments, que j’ai faits, [dit David, ] pour louer.
6 Dawuda ya rarraba Lawiyawa ƙungiya-ƙungiya bisa ga’ya’yan Lawi maza. Gershon, Kohat da Merari.
Et David les distribua en classes d’après les fils de Lévi, Guershon, Kehath, et Merari.
7 Na Gershonawa, Ladan da Shimeyi.
Des Guershonites: Lahdan et Shimhi.
8 ’Ya’yan Ladan maza su ne, Yehiyel na farko, Zetam da Yowel, su uku ne duka.
Les fils de Lahdan: Jekhiel, le premier, et Zétham, et Joël, trois.
9 ’Ya’yan Shimeyi maza su ne, Shelomot, Haziyel da Haran, su uku ne duka. Waɗannan su ne kawunan iyalan Ladan.
Les fils de Shimhi: Shelomith, et Haziel, et Haran, trois. Ce sont les chefs des pères de Lahdan.
10 ’Ya’yan Shimeyi maza kuwa su ne, Yahat, Zina, Yewush da Beriya. Waɗannan su ne’ya’yan Shimeyi maza, su huɗu ne duka.
Et les fils de Shimhi: Jakhath, Ziza, et Jehush, et Beriha: ce sont les quatre fils de Shimhi.
11 Yahat shi ne na fari, Ziza kuma na biyu, amma Yewush da Beriya ba su haifi’ya’ya maza da yawa ba; saboda haka aka ƙidaya su kamar iyali ɗaya a wurin rabon aiki.
Et Jakhath était le chef, et Ziza, le second. Mais Jehush et Beriha n’eurent pas beaucoup de fils; et, par maison de père, ils furent comptés pour une seule classe.
12 ’Ya’yan Kohat maza su ne, Amram, Izhar, Hebron da Uzziyel, su huɗu ne duka.
Les fils de Kehath: Amram, Jitsehar, Hébron, et Uziel, quatre.
13 ’Ya’yan Amram maza su ne, Haruna da Musa. Haruna shi ne aka keɓe, shi da zuriyarsa har abada, don su tsarkake kayayyakin mafi tsarki, su miƙa hadayu a gaban Ubangiji, su yi hidima a gabansa su kuma furta albarku a cikin sunansa har abada.
Les fils d’Amram: Aaron et Moïse; et Aaron fut séparé pour qu’il soit sanctifié comme très saint, lui et ses fils, à toujours, pour faire fumer [ce qui se brûle] devant l’Éternel, pour faire son service, et pour bénir en son nom, à toujours.
14 An ƙidaya aka kuma haɗa’ya’yan Musa maza mutumin Allah a sashen kabilar Lawi.
– Et quant à Moïse, homme de Dieu, ses fils furent attribués à la tribu de Lévi.
15 ’Ya’yan Musa maza su ne, Gershom da Eliyezer.
Fils de Moïse: Guershom et Éliézer.
16 Zuriyar Gershom su ne, Shebuwel ne ɗan fari.
Fils de Guershom: Shebuel, le chef.
17 Zuriyar Eliyezer su ne, Rehabiya ne ɗan fari. Eliyezer ba shi da waɗansu’ya’ya maza, amma’ya’yan Rehabiya maza sun yi yawa.
Et les fils d’Éliézer étaient: Rekhabia, le chef; et Éliézer n’eut pas d’autres fils; mais les fils de Rekhabia furent très nombreux.
18 ’Ya’yan Izhar maza su ne, Shelomit ne ɗan fari.
– Fils de Jitsehar: Shelomith, le chef.
19 ’Ya’yan Hebron maza su ne, Yeriya na fari, Amariya na biyu, Yahaziyel na uku da Yekameyam na huɗu.
Fils de Hébron: Jerija, le chef; Amaria, le second; Jakhaziel, le troisième; et Jekamham, le quatrième.
20 ’Ya’yan Uzziyel maza su ne, Mika na fari da Isshiya na biyu.
Fils d’Uziel: Michée, le chef, et Jishija, le second.
21 ’Ya’yan Merari maza su ne, Mali da Mushi.’Ya’yan Mali maza su ne, Eleyazar da Kish.
Les fils de Merari: Makhli et Mushi. Fils de Makhli: Éléazar et Kis.
22 Eleyazar ya mutu ba’ya’yan maza, yana da’ya’ya mata ne kawai.’Yan’uwansu,’ya’yan Kish maza, suka aure su.
Et Éléazar mourut, et n’eut point de fils, mais des filles; et les fils de Kis, leurs frères, les prirent [pour femmes].
23 ’Ya’yan Mushi maza su ne, Mali, Eder da Yeremot, su uku ne duka.
Fils de Mushi: Makhli, et Éder, et Jerémoth, trois.
24 Waɗannan ne zuriyar Lawi bisa ga iyalansu, kawunan iyalai kamar yadda aka rubuta su a ƙarƙashin sunayensu aka kuma ƙirga kowa, wato, masu aikin da suke’yan shekara ashirin da haihuwa ko fiye waɗanda suka yi hidima a cikin haikalin Ubangiji.
Ce sont là les fils de Lévi, selon leurs maisons de pères, les chefs des pères, selon qu’ils furent recensés, en comptant les noms par tête; ils faisaient l’œuvre du service de la maison de l’Éternel, depuis l’âge de 20 ans, et au-dessus;
25 Gama Dawuda ya ce, “Tun da Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya ba da hutu ga mutanensa, ya kuma zo ya zauna a Urushalima har abada,
car David dit: L’Éternel, le Dieu d’Israël, a donné du repos à son peuple, et il demeurera à Jérusalem pour toujours;
26 Lawiyawa ba sa ƙara bukata su ɗauki tabanakul ko kuwa waɗansu kayayyakin da ake amfani da su a hidima.”
et les Lévites aussi n’auront plus à porter le tabernacle, ni tous les ustensiles pour son service.
27 Bisa ga umarnin ƙarshe na Dawuda, za a ƙidaya Lawiyawa daga’yan shekara ashirin ko fiye.
Car c’est selon les dernières paroles de David que se fit le dénombrement des fils de Lévi, depuis l’âge de 20 ans et au-dessus.
28 Aikin Lawiyawa shi ne su taimaki zuriyar Haruna a hidimar haikalin Ubangiji; su lura da filaye da kuma ɗakunan da suke gefe, su tsarkake dukan kayayyaki masu tsarki, su kuma yi waɗansu ayyuka a gidan Allah.
Car leur place était à côté des fils d’Aaron pour le service de la maison de l’Éternel, [pour veiller] sur les parvis et les chambres, et sur la purification de toutes les choses saintes, et sur l’œuvre du service de la maison de Dieu:
29 Su ne za su lura da burodin da aka ajiye a tebur, lallausan gari don hadaya ta gari, waina marar yisti, toyawa da kwaɓawa, da kuma dukan awon yawa da kuma girman abubuwa.
pour les pains à placer en rangées, et la fleur de farine pour le gâteau et les galettes sans levain, et [ce qui se cuit sur] la plaque, et ce qui est mêlé [avec de l’huile], et toutes les mesures de capacité et de longueur;
30 Su ne kuma za su tsaya kowace safiya su yi godiya, su kuma yabi Ubangiji. Za su kuma yi haka da yamma
et pour se tenir là chaque matin, afin de célébrer et de louer l’Éternel, et de même chaque soir;
31 da kuma a duk sa’ad da aka miƙa hadayun ƙonawa ga Ubangiji a Asabbatai da bukukkuwan Sabon Wata da kuma a ƙayyadaddun bukukkuwa, za su yi hidima a gaban Ubangiji kullum bisa ga yawan da aka tsara da kuma a hanyar da aka tsara musu.
et [pour être de service] pour tous les holocaustes qu’on offrait à l’Éternel, aux sabbats, aux nouvelles lunes, et aux jours solennels, en nombre, conformément à l’ordonnance à leur égard, continuellement, devant l’Éternel.
32 A haka kuwa Lawiyawa suka yi ayyukansu don Tentin Sujada, don Wuri Mai Tsarki da kuma a ƙarƙashin’yan’uwansu zuriyar Haruna, saboda hidimar haikalin Ubangiji.
Et ils vaquaient à leur charge à l’égard de la tente d’assignation, et à leur charge à l’égard du lieu saint, et à leur charge à l’égard des fils d’Aaron, leurs frères, pour le service de la maison de l’Éternel.