< 1 Tarihi 23 >

1 Sa’ad da Dawuda ya tsufa yana kuma da cikakken shekaru, ya sa ɗansa Solomon sarki bisa Isra’ila.
And David was old and full of days; and he made Solomon his son king over Israel in his stead.
2 Ya kuma tattara dukan shugabannin Isra’ila a wuri ɗaya, haka kuma ya yi da firistoci da Lawiyawa.
And he assembled all the chief men of Israel, and the priests, and the Levites.
3 Aka ƙidaya Lawiyawan da suke’yan shekaru talatin da haihuwa ko fiye, suka kai wajen mutum dubu talatin da takwas.
And the Levites numbered [themselves] from thirty years old and upward; and their number by their polls amounted to thirty and eight thousand men.
4 Dawuda ya ce, “Cikin waɗannan, dubu ashirin da huɗu za su lura da aikin haikalin Ubangiji, dubu shida su zama manyan na ma’aikata da alƙalai.
Of the overseers over the works of the house of the Lord [there were] twenty-four thousand, and [there were] six thousand scribes and judges;
5 Dubu huɗu su zama matsaran ƙofofi, dubu huɗu kuma su yabi Ubangiji da kayayyakin bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe waɗanda na tanada saboda wannan manufa.”
and four thousand doorkeepers, and four thousand to praise the Lord with instruments which he made to praise the Lord.
6 Dawuda ya rarraba Lawiyawa ƙungiya-ƙungiya bisa ga’ya’yan Lawi maza. Gershon, Kohat da Merari.
And David divided them [into] daily courses, for the sons of Levi, for Gedson, Caath, and Merari.
7 Na Gershonawa, Ladan da Shimeyi.
And for [the family of] Gedson, Edan, and Semei.
8 ’Ya’yan Ladan maza su ne, Yehiyel na farko, Zetam da Yowel, su uku ne duka.
The sons of Edan [were] Jeiel, the chief, and Zethan, and Joel, three.
9 ’Ya’yan Shimeyi maza su ne, Shelomot, Haziyel da Haran, su uku ne duka. Waɗannan su ne kawunan iyalan Ladan.
The sons of Semei; Salomith, Jeiel, and Dan, three: these [were] the chiefs of the families of Edan.
10 ’Ya’yan Shimeyi maza kuwa su ne, Yahat, Zina, Yewush da Beriya. Waɗannan su ne’ya’yan Shimeyi maza, su huɗu ne duka.
And to the sons of Semei, Jeth, and Ziza, and Joas, and Beria: these [were] the four sons of Semei.
11 Yahat shi ne na fari, Ziza kuma na biyu, amma Yewush da Beriya ba su haifi’ya’ya maza da yawa ba; saboda haka aka ƙidaya su kamar iyali ɗaya a wurin rabon aiki.
And Jeth was the chief, and Ziza the second: and Joas and Beria did not multiply sons, and they became [only] one reckoning according to the house of their father.
12 ’Ya’yan Kohat maza su ne, Amram, Izhar, Hebron da Uzziyel, su huɗu ne duka.
The sons of Caath; Ambram, Isaar, Chebron, Oziel, four.
13 ’Ya’yan Amram maza su ne, Haruna da Musa. Haruna shi ne aka keɓe, shi da zuriyarsa har abada, don su tsarkake kayayyakin mafi tsarki, su miƙa hadayu a gaban Ubangiji, su yi hidima a gabansa su kuma furta albarku a cikin sunansa har abada.
The sons of Ambram; Aaron and Moses: and Aaron was appointed for the consecration of the most holy things, he and his sons for ever, to burn incense before the Lord, to minister and bless in his name for ever.
14 An ƙidaya aka kuma haɗa’ya’yan Musa maza mutumin Allah a sashen kabilar Lawi.
And [as for] Moses the man of God, his sons were reckoned to the tribe of Levi.
15 ’Ya’yan Musa maza su ne, Gershom da Eliyezer.
The sons of Moses; Gersam, and Eliezer.
16 Zuriyar Gershom su ne, Shebuwel ne ɗan fari.
The sons of Gersam; Subael the chief.
17 Zuriyar Eliyezer su ne, Rehabiya ne ɗan fari. Eliyezer ba shi da waɗansu’ya’ya maza, amma’ya’yan Rehabiya maza sun yi yawa.
And the sons of Eliezer were, Rabia the chief: and Eliezer had no other sons; but the sons of Rabia were very greatly multiplied.
18 ’Ya’yan Izhar maza su ne, Shelomit ne ɗan fari.
The sons of Isaar; Salomoth the chief.
19 ’Ya’yan Hebron maza su ne, Yeriya na fari, Amariya na biyu, Yahaziyel na uku da Yekameyam na huɗu.
The sons of Chebron; Jeria the chief, Amaria the second, Jeziel the third, Jekemias the fourth.
20 ’Ya’yan Uzziyel maza su ne, Mika na fari da Isshiya na biyu.
The sons of Oziel; Micha the chief, and Isia the second.
21 ’Ya’yan Merari maza su ne, Mali da Mushi.’Ya’yan Mali maza su ne, Eleyazar da Kish.
The sons of Merari; Mooli, and Musi: the sons of Mooli; Eleazar, and Kis.
22 Eleyazar ya mutu ba’ya’yan maza, yana da’ya’ya mata ne kawai.’Yan’uwansu,’ya’yan Kish maza, suka aure su.
And Eleazar died, and he had no sons, but daughters: and the sons of Kis, their brethren, took them.
23 ’Ya’yan Mushi maza su ne, Mali, Eder da Yeremot, su uku ne duka.
The sons of Musi; Mooli, and Eder, and Jarimoth, three.
24 Waɗannan ne zuriyar Lawi bisa ga iyalansu, kawunan iyalai kamar yadda aka rubuta su a ƙarƙashin sunayensu aka kuma ƙirga kowa, wato, masu aikin da suke’yan shekara ashirin da haihuwa ko fiye waɗanda suka yi hidima a cikin haikalin Ubangiji.
These [are] the sons of Levi according to the houses of their fathers; chiefs of their families according to their numbering, according to the number of their names, according to their polls, doing the works of service of the house of the Lord, from twenty years old and upward.
25 Gama Dawuda ya ce, “Tun da Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya ba da hutu ga mutanensa, ya kuma zo ya zauna a Urushalima har abada,
For David said, The Lord God of Israel has given rest to his people, and has taken up his abode in Jerusalem for ever.
26 Lawiyawa ba sa ƙara bukata su ɗauki tabanakul ko kuwa waɗansu kayayyakin da ake amfani da su a hidima.”
And the Levites bore not the tabernacle, and all the vessels of it for its service.
27 Bisa ga umarnin ƙarshe na Dawuda, za a ƙidaya Lawiyawa daga’yan shekara ashirin ko fiye.
For by the last words of David was the number of the Levites [taken] from twenty years old and upward.
28 Aikin Lawiyawa shi ne su taimaki zuriyar Haruna a hidimar haikalin Ubangiji; su lura da filaye da kuma ɗakunan da suke gefe, su tsarkake dukan kayayyaki masu tsarki, su kuma yi waɗansu ayyuka a gidan Allah.
For he appointed them to wait on Aaron, to minister in the house of the Lord, over the courts, and over the chambers, and over the purification of all the holy things, and over the works of the service of the house of God;
29 Su ne za su lura da burodin da aka ajiye a tebur, lallausan gari don hadaya ta gari, waina marar yisti, toyawa da kwaɓawa, da kuma dukan awon yawa da kuma girman abubuwa.
and for the show-bread, and for the fine flour of the meat-offering, and for the unleavened cakes, and for the fried cake, and for the dough, and for every measure;
30 Su ne kuma za su tsaya kowace safiya su yi godiya, su kuma yabi Ubangiji. Za su kuma yi haka da yamma
and to stand in the morning to praise and give thanks to the Lord, and so in the evening;
31 da kuma a duk sa’ad da aka miƙa hadayun ƙonawa ga Ubangiji a Asabbatai da bukukkuwan Sabon Wata da kuma a ƙayyadaddun bukukkuwa, za su yi hidima a gaban Ubangiji kullum bisa ga yawan da aka tsara da kuma a hanyar da aka tsara musu.
and [to be] over all the whole burnt offerings that were offered up to the Lord on the sabbaths, and at the new moons, and at the feasts, by number, according to the order [given] to them, continually before the Lord.
32 A haka kuwa Lawiyawa suka yi ayyukansu don Tentin Sujada, don Wuri Mai Tsarki da kuma a ƙarƙashin’yan’uwansu zuriyar Haruna, saboda hidimar haikalin Ubangiji.
And they are to keep the charge of the tabernacle of witness, and the charge of the holy place, and the charges of the sons of Aaron their brethren, to minister in the house of the Lord.

< 1 Tarihi 23 >