< 1 Tarihi 22 >

1 Sai Dawuda ya ce, “Gidan Ubangiji Allah zai kasance a nan, haka kuma bagaden hadaya ta ƙonawa don Isra’ila.”
Then David said, “Here, [at the edge of Jerusalem, ] is where [we will build] the temple for our God Yahweh, and where [we will make] the altar for burning the offerings that the Israeli [people will bring].”
2 Dawuda kuwa ya umarta a tattara baƙin da suke zama a Isra’ila, daga cikinsu ya sa masu farfasa duwatsu don su shirya duwatsun da aka sassaƙa saboda ginin gidan Allah.
So David commanded that the foreigners who lived in Israel must gather together. [When they did that, ] he appointed [some of those] men to [cut huge] stones [from the quarries] and to smooth their surfaces, to be used to build the temple of God.
3 Ya tanada ƙarfe mai yawa don ƙusoshi saboda ƙyamaren hanyoyin shiga da kuma saboda mahaɗai, da ƙarin tagulla fiye da ƙirge.
David provided a large amount of iron for making nails and hinges for the doors in the gates of the temple. He also provided so much bronze [for making the altar and various utensils], that no one could weigh it all.
4 Ya kuma tanada gumaguman al’ul masu yawa fiye da ƙirge, gama Sidoniyawa da mutanen Taya sun kawo su wa Dawuda da yawa.
He also provided [money for buying] a large amount of cedar logs. Because there was a huge number of them, no one was able to count them. Those were logs that men from Tyre and Sidon [cities] sent to David.
5 Dawuda ya ce, “Ɗana Solomon matashi ne kuma bai gogu ba, kuma gidan da za a gina wa Ubangiji zai zama mai ƙayatarwa ƙwarai, sananne da kuma mai daraja a idon dukan al’ummai. Saboda haka zan yi shirye-shirye saboda shi.” Sai Dawuda ya yi ɗumbun shirye-shirye kafin mutuwarsa.
David [provided all those things because he] thought, “My son Solomon is still young and he does not know what he needs to know [about building], and the temple of Yahweh must be (magnificent/very beautiful). It must be a glorious building that will become famous, and people throughout the world must consider it to be glorious/splendid. So now I will begin to prepare for it to be built, [and Solomon will be responsible for building it].” So David collected a great amount of building materials before he died.
6 Sa’an nan ya kira ɗansa Solomon ya umarce shi yă gina gida domin Ubangiji, Allah na Isra’ila.
[When] David [was old, he] summoned his son Solomon, and told him that he should arrange for a temple to be built for Yahweh, the God whom the Israelis [worshiped].
7 Dawuda ya ce wa Solomon, “Ɗana, na yi niyya a zuciyata in gina gida saboda Sunan Ubangiji Allahna.
He said to him, “I wanted [IDM] to build a temple to honor [MTY] Yahweh, my God.
8 Amma wannan maganar Ubangiji ta zo mini, ‘Ka zub da jini mai yawa ka kuma yi yaƙe-yaƙe masu yawa. Ba za ka gina gida domin Sunana ba, domin ka zub da jini da yawa a duniya a idona.
But Yahweh told [a prophet to tell] me, ‘You have killed many men [MTY] in the battles that you have fought. I have seen the blood of all the people whom you killed, so you will not be the one who will arrange for a temple to be built to honor me [MTY].
9 Amma za ka haifi ɗa wanda zai zama mutumin salama da kuma hutu, zan kuma ba shi hutu daga dukan abokan gābansa a kowane gefe. Za a kira shi Solomon, zai kuma kawo wa Isra’ila salama da natsuwa a zamanin mulkinsa.
But you will have a son [who will be king of Israel after you die]. He will be a man who is peaceful and quiet, [not a man who kills others]. And I will cause that there will be peace between him and his enemies who are in all the nearby lands. His name will be Solomon, [which sounds like the word for peace]. During the time that he is king, people in Israel will be peaceful and safe.
10 Shi ne wanda zai gina gida saboda Sunana. Zai zama ɗana, ni kuma zan zama mahaifinsa. Zan kafa kujerar sarautarsa a bisa Isra’ila har abada.’
He is the one who will arrange for a temple to be built to honor me [MTY]. He will be [like] a son to me, and I will cause some of his descendants to rule [MTY] over Israel forever [HYP].’
11 “Yanzu, ɗana, Ubangiji ya kasance tare da kai, bari kuma ka yi nasara ka kuma gina gidan Ubangiji Allahnka, kamar yadda ya ce za ka yi.
“So now, my son, I hope/wish that Yahweh will help you, and enable you to be successful in arranging for building the temple of Yahweh, your God, which is what he said that you would do.
12 Bari Ubangiji ya ba ka basira da fahimi sa’ad da ya sa ka shugaba a bisa Isra’ila, saboda ka kiyaye dokar Ubangiji Allahnka.
I also hope/wish that he will enable you to be wise and to understand what you need to know, and enable you to obey his laws while you rule over Israel.
13 Ta haka za ka yi nasara in ka mai da hankali ga kiyaye ƙa’idodi da dokokin da Ubangiji ya ba wa Musa saboda Isra’ila. Ka yi ƙarfin hali ka kuma ƙarfafa. Kada ka ji tsoro ko ka fid da zuciya.
If you carefully obey all the laws and regulations/commands that Yahweh gave to Moses to give to us Israeli people, you will be successful. So be steadfast/strong and courageous. Do not be afraid of anything, and do not become discouraged!
14 “Na sha wahala da yawa don in yi tanadi talentin dubu ɗari na zinariya, talenti miliyon na azurfa, ɗumbun tagulla da ƙarfe da suka wuce ƙirge da katako da dutse saboda haikalin Ubangiji. Za ka iya ƙara su.
“I have tried hard to provide [materials] for [building] the temple of Yahweh. I have provided nearly 4,000 tons of gold, and nearly 40,000 tons of silver. I have also provided a very large amount of iron and bronze; no one has been able to weigh it all. I have also gathered/provided lumber and stone [for the walls of the temple], but you may need to get some more of those things.
15 Kana da ma’aikata masu yawa, masu fafarshe duwatsu, masu gini da masu aikin katako, da kuma gwanaye a kowane irin aikin
There are many men [in Israel] who have good ability to cut big stones for making stone walls, and carpenters, and men who are very skilled at making various kinds of things.
16 zinariya da azurfa, tagulla da ƙarfe, masu sana’a waɗanda suka wuce ƙirge. Yanzu ka fara aiki, Ubangiji kuma ya kasance tare da kai.”
There are many men who know how to make things from gold and silver and bronze and iron. So now [I say to you], begin the work [of building the temple], and I hope/wish that Yahweh will help/be with you.”
17 Sai Dawuda ya umarta dukan shugabannin Isra’ila su taimake ɗansa Solomon.
Then David commanded that all the Israeli leaders must assist Solomon. He said to them,
18 Ya ce musu, “Ba Ubangiji Allahnku yana tare da ku ba? Bai kuma ba ku hutu a kowane gefe ba? Gama ya ba da mazaunan ƙasar gare ni, ƙasar kuma ta Ubangiji ce da mutanensa.
“Yahweh our God is certainly with/helping you [RHQ]. He has allowed you to have peace with all the nearby nations [RHQ]. He has enabled my [army] to conquer [IDM] them, so now Yahweh and my people control them.
19 Yanzu fa sai ku sa zuciyarku da ranku ga neman Ubangiji Allahnku. Ku fara ginin wuri mai tsarki na Ubangiji Allah, don ku kawo akwatin alkawarin Ubangiji da kayayyaki masu tsarki na Allah a cikin haikalin da za a gina saboda Sunan Ubangiji.”
Now you must obey Yahweh completely. Help Solomon to arrange for building the temple for Yahweh God, in order that you can bring the Sacred Chest that contains the Ten Commandments and the other sacred items that belong to God into the temple that you will build to honor Yahweh.”

< 1 Tarihi 22 >