< 1 Tarihi 22 >

1 Sai Dawuda ya ce, “Gidan Ubangiji Allah zai kasance a nan, haka kuma bagaden hadaya ta ƙonawa don Isra’ila.”
Zato David reče: “Ovo je Dom Jahve i ovo je žrtvenik za paljenice Izraelu!”
2 Dawuda kuwa ya umarta a tattara baƙin da suke zama a Isra’ila, daga cikinsu ya sa masu farfasa duwatsu don su shirya duwatsun da aka sassaƙa saboda ginin gidan Allah.
David zapovjedi da se skupe stranci koji su bili u izraelskoj zemlji i odredi klesare da propisno klešu kamenje za gradnju Doma Božjeg.
3 Ya tanada ƙarfe mai yawa don ƙusoshi saboda ƙyamaren hanyoyin shiga da kuma saboda mahaɗai, da ƙarin tagulla fiye da ƙirge.
David je pripravio mnogo željeza za čavle na vratnim krilima i za kvačice; i bez mjere mnogo tuča.
4 Ya kuma tanada gumaguman al’ul masu yawa fiye da ƙirge, gama Sidoniyawa da mutanen Taya sun kawo su wa Dawuda da yawa.
Mnogo cedrovine, jer su Sidonci i Tirci dovozili mnogo cedrovih drva Davidu.
5 Dawuda ya ce, “Ɗana Solomon matashi ne kuma bai gogu ba, kuma gidan da za a gina wa Ubangiji zai zama mai ƙayatarwa ƙwarai, sananne da kuma mai daraja a idon dukan al’ummai. Saboda haka zan yi shirye-shirye saboda shi.” Sai Dawuda ya yi ɗumbun shirye-shirye kafin mutuwarsa.
Jer David mišljaše: “Moj je sin Salomon mlad i nježan, a Dom koji treba graditi Jahvi mora biti veličanstven, na slavu i čast po svim zemljama. Hajde da mu sve pripravim.” I David je pripravio mnogo toga prije svoje smrti.
6 Sa’an nan ya kira ɗansa Solomon ya umarce shi yă gina gida domin Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Potom dozva sina Salomona i zapovjedi mu da sagradi Dom Jahvi, Bogu Izraelovu.
7 Dawuda ya ce wa Solomon, “Ɗana, na yi niyya a zuciyata in gina gida saboda Sunan Ubangiji Allahna.
Još David reče Salomonu: “Sine! Bio sam nakanio u srcu da sagradim Dom imenu Jahve, svoga Boga.
8 Amma wannan maganar Ubangiji ta zo mini, ‘Ka zub da jini mai yawa ka kuma yi yaƙe-yaƙe masu yawa. Ba za ka gina gida domin Sunana ba, domin ka zub da jini da yawa a duniya a idona.
Ali mi je došla Jahvina riječ: 'Mnogo si krvi prolio i velike si ratove vodio; nećeš ti graditi Doma mome imenu jer si mnogo krvi prolio na zemlju preda mnom.
9 Amma za ka haifi ɗa wanda zai zama mutumin salama da kuma hutu, zan kuma ba shi hutu daga dukan abokan gābansa a kowane gefe. Za a kira shi Solomon, zai kuma kawo wa Isra’ila salama da natsuwa a zamanin mulkinsa.
Gle, rodit će ti se sin; on će biti miroljubac i dat ću mu mir od svih njegovih neprijatelja odasvud unaokolo; ime će mu biti Salomon. Mir i pokoj dat ću Izraelu za njegova vremena.
10 Shi ne wanda zai gina gida saboda Sunana. Zai zama ɗana, ni kuma zan zama mahaifinsa. Zan kafa kujerar sarautarsa a bisa Isra’ila har abada.’
On će sagraditi Dom mome imenu, on će mi biti sin, a ja ću njemu biti otac i utvrdit ću njegovo kraljevsko prijestolje nad Izraelom zauvijek.'
11 “Yanzu, ɗana, Ubangiji ya kasance tare da kai, bari kuma ka yi nasara ka kuma gina gidan Ubangiji Allahnka, kamar yadda ya ce za ka yi.
Sada, moj sine, neka bude Jahve s tobom da izvršiš i sagradiš Dom Jahve, svoga Boga, kao što je rekao za te.
12 Bari Ubangiji ya ba ka basira da fahimi sa’ad da ya sa ka shugaba a bisa Isra’ila, saboda ka kiyaye dokar Ubangiji Allahnka.
Samo neka ti Jahve poda razum i mudrost kad te postavi nad Izraelom zato da se držiš Zakona Jahve, svoga Boga!
13 Ta haka za ka yi nasara in ka mai da hankali ga kiyaye ƙa’idodi da dokokin da Ubangiji ya ba wa Musa saboda Isra’ila. Ka yi ƙarfin hali ka kuma ƙarfafa. Kada ka ji tsoro ko ka fid da zuciya.
Bit ćeš sretan budeš li brižno vršio uredbe i zakone koje je Jahve preko Mojsija dao Izraelu. Budi junak i hrabar, ne boj se i ne plaši se!
14 “Na sha wahala da yawa don in yi tanadi talentin dubu ɗari na zinariya, talenti miliyon na azurfa, ɗumbun tagulla da ƙarfe da suka wuce ƙirge da katako da dutse saboda haikalin Ubangiji. Za ka iya ƙara su.
Ja sam, evo, svojim trudom pripravio za Dom Jahvin sto tisuća zlatnih talenata i milijun srebrnih talenata, a tuča i željeza bez mjere, jer ga je tako mnogo. Pripravio sam i drva i kamenja, a i ti dodaj nešto k tomu.
15 Kana da ma’aikata masu yawa, masu fafarshe duwatsu, masu gini da masu aikin katako, da kuma gwanaye a kowane irin aikin
Imaš mnogo valjanih radnika, klesara, zidara, tesara i svakovrsnih vještaka u svakom umijeću;
16 zinariya da azurfa, tagulla da ƙarfe, masu sana’a waɗanda suka wuce ƙirge. Yanzu ka fara aiki, Ubangiji kuma ya kasance tare da kai.”
zlatu, srebru, tuču i željezu nema mjere; idi, dakle, i gradi, i neka Jahve bude s tobom!”
17 Sai Dawuda ya umarta dukan shugabannin Isra’ila su taimake ɗansa Solomon.
Tada David zapovjedi svim izraelskim knezovima da pomažu njegovu sinu Salomonu:
18 Ya ce musu, “Ba Ubangiji Allahnku yana tare da ku ba? Bai kuma ba ku hutu a kowane gefe ba? Gama ya ba da mazaunan ƙasar gare ni, ƙasar kuma ta Ubangiji ce da mutanensa.
“Nije li s vama Jahve, Bog vaš, koji vam je dao mir odasvud unaokolo jer je predao u moje ruke stanovnike ove zemlje i zemlja je pokorena pred Jahvom i pred njegovim narodom.
19 Yanzu fa sai ku sa zuciyarku da ranku ga neman Ubangiji Allahnku. Ku fara ginin wuri mai tsarki na Ubangiji Allah, don ku kawo akwatin alkawarin Ubangiji da kayayyaki masu tsarki na Allah a cikin haikalin da za a gina saboda Sunan Ubangiji.”
Sada, dakle, pregnite svojim srcem i svojom dušom da tražite Jahvu, svoga Boga; idite i gradite Svetište Bogu Jahvi, unesite Kovčeg saveza Jahvina i Božje sveto posuđe u Dom koji će se sagraditi Jahvinu imenu!”

< 1 Tarihi 22 >