< 1 Tarihi 21 >

1 Sai Shaiɗan ya tashi gāba da Isra’ila, ya zuga Dawuda ya ƙidaya Isra’ila.
Or Satan s’éleva contre Israël, et excita David à dénombrer Israël.
2 Saboda haka Dawuda ya ce wa Yowab da shugabannin mayaƙa, “Ku tafi ku ƙidaya Isra’ilawa daga Beyersheba zuwa Dan. Ku kawo mini labarin saboda in san su nawa ne.”
Et David dit à Joab et aux princes du peuple: Allez, et dénombrez Israël, depuis Bersabée jusqu’à Dan, et apportez-moi le nombre, afin que je le sache.
3 Amma Yowab ya amsa ya ce, “Ubangiji ya riɓaɓɓanya mayaƙansa fiye da sau ɗari. Ranka yă daɗe sarki, dukansu ba bayin shugabana ba ne? Me ya sa ranka yă daɗe yake so yă yi haka? Me zai sa ka kawo laifi a kan Isra’ila?”
Et Joab répondit: Que le Seigneur accroisse son peuple au centuple de ce qu’il est: est-ce, mon seigneur roi, que tous ne sont pas vos serviteurs? Pourquoi mon seigneur recherche-t-il ce qui sera imputé à péché à Israël?
4 Amma sarki ya nace a kan maganar da ya yi wa Yowab. Sai Yowab ya tashi ya tafi cikin dukan Isra’ila, ya kewaye sa’an nan ya dawo Urushalima.
Mais la parole du roi prévalut, et Joab sortit et parcourut tout Israël, et il revint à Jérusalem.
5 Yowab ya ba labarin yawan mayaƙan wa Dawuda. A cikin Isra’ila akwai mutum miliyon da dubu ɗari ɗaya waɗanda za su iya riƙe takobi, haɗe da dubu ɗari huɗu da saba’in a Yahuda.
Et il donna à David le nombre de tous ceux qu’il avait visités, et le nombre total d’Israël se trouva onze cent mille hommes d’Israël, tous tirant le glaive; mais de Juda, quatre cent soixante-dix mille guerriers.
6 Amma Yowab bai haɗa da mutanen Lawi da na Benyamin a ƙidayar ba, domin bai ji daɗin umarnin sarki ba.
Car, pour Lévi et Benjamin, Joab ne les dénombra point, parce que c’était à regret qu’il exécutait l’ordre du roi.
7 Wannan umarnin mugu ne a gaban Allah; saboda haka ya hukunta Isra’ila.
En effet, ce qui avait été commandé déplut à Dieu, et il frappa Israël.
8 Sai Dawuda ya ce wa Allah, “Na yi zunubi ƙwarai ta wurin yin wannan. Yanzu, na roƙe ka, ka ɗauke laifin bawanka. Na yi wauta sosai.”
Et David dit à Dieu: J’ai péché grièvement en faisant cela. Je vous conjure, effacez l’iniquité de votre serviteur, parce que j’ai agi en insensé.
9 Sai Ubangiji ya ce wa Gad, mai duba na Dawuda,
Alors le Seigneur parla à Gad, le Voyant de David, disant:
10 “Tafi ka faɗa wa Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce ina ba ka abubuwa uku. Ka zaɓi ɗaya daga cikinsu don in aikata a kanka.’”
Va et parle à David, et dis-lui: Voici ce que dit le Seigneur: Je te donne l’option de trois choses; choisis celle que tu voudras, et je te la ferai.
11 Saboda haka Gad ya tafi wurin Dawuda ya ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka yi zaɓi,
Lors donc que Gad fut venu vers David, il lui dit: Voici ce que dit le Seigneur: Choisis ce que tu voudras:
12 shekara uku na yunwa, wata uku na shan ɗibga a gaban abokan gābanka, sa’ad da za su bi suna kakkashe ku, ko kuwa kwana uku na takobin Ubangiji, ranakun annoba a cikin ƙasar, mala’ikan Ubangiji zai hallaka kowane sashe na Isra’ila.’ Yanzu sai ka yanke shawara yadda zan amsa wa wanda ya aiko ni.”
Ou, durant trois ans, une famine; ou, durant trois mois, fuir devant les ennemis et ne pouvoir pas éviter leur glaive; ou que, pendant trois jours, le glaive du Seigneur et une peste règnent dans le pays, et qu’un ange du Seigneur tue dans tous les confins d’Israël. Maintenant donc, vois ce que je dois répondre à celui qui m’a envoyé.
13 Dawuda ya ce wa Gad, “Na shiga uku. Bari in fāɗa a hannuwan Ubangiji, gama jinƙansa yana da girma sosai; amma kada ka bari in fāɗa a hannuwan mutane.”
Et David dit à Gad: De toutes parts les angoisses me pressent; mais il vaut mieux pour moi que je tombe dans les mains du Seigneur (parce que ses miséricordes sont sans nombre), que dans les mains des hommes,
14 Sai Ubangiji ya aiko da annoba a kan Isra’ila, mutane duba saba’in na Isra’ila suka mutu.
Le Seigneur envoya donc une peste en Israël, et il mourut d’Israël soixante-dix mille hommes.
15 Allah kuwa ya aiki mala’ika yă hallaka Urushalima. Amma yayinda mala’ikan yana gab da yin haka, sai Ubangiji ya gani ya kuma yi nadama saboda masifar, sai ya ce wa mala’ikan wanda yake hallaka mutane, “Ya isa! Janye hannunka.” Mala’ikan Ubangiji kuwa yana tsaye a masussukar Ornan mutumin Yebus.
Il envoya aussi un ange à Jérusalem pour la frapper; et, lorsqu’elle était frappée, le Seigneur le vit, et fut touché de compassion à cause de la grandeur du mal; il commanda donc à l’ange qui frappait: Il suffit; qu’à l’instant ta main s’arrête. Or l’ange du Seigneur se tenait alors près de l’aire d’Ornan, le Jébuséen.
16 Sai Dawuda ya ɗaga ido ya ga mala’ikan Ubangiji tsaye tsakanin sama da duniya, da takobi a zāre a hannunsa ya miƙa a kan Urushalima. Sai Dawuda da dattawa, saye da rigunan makoki suka fāɗi rubda jiki.
Et David, levant ses yeux, vit l’ange du Seigneur debout entre le ciel et la terre, et un glaive nu en sa main, et tourné contre Jérusalem; alors lui aussi bien que les anciens, revêtus de cilices, tombèrent inclinés vers la terre.
17 Dawuda ya ce wa Allah, “Ba ni ba ne na umarta a ƙidaya mayaƙan? Ni ne wanda ya yi zunubin da kuma abin da ba daidai ba. Waɗannan dai tumaki ne. Me suka yi? Ya Ubangiji Allahna, bari hannunka ya fāɗi a kaina da kuma iyalina, amma kada ka bar wannan annoba ya kasance a kan mutanenka.”
Et David dit à Dieu: N’est-ce pas moi qui ai commandé de dénombrer le peuple? C’est moi qui ai péché; c’est moi qui ai fait le mal; mais ce troupeau, qu’a-t-il mérité? Seigneur mon Dieu, je vous conjure, que votre main se tourne contre moi et contre la maison de mon père; mais que votre peuple ne soit pas frappé.
18 Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya umarci Gad yă faɗa wa Dawuda yă haura yă gina bagade wa Ubangiji a masussukar Ornan mutumin Yebus.
Or l’ange du Seigneur ordonna à Gad de dire à David qu’il montât et dressât un autel au Seigneur Dieu dans l’aire d’Ornan, le Jébuséen.
19 Saboda haka Dawuda ya haura cikin biyayya ga maganar da Allah ya yi da sunan Ubangiji.
David monta donc, suivant la parole que Gad lui avait dite au nom du Seigneur.
20 Yayinda Ornan yake sussukar alkama, sai ya juya ya ga mala’ika;’ya’yansa maza guda huɗu da suke tare da shi suka ɓuya.
Mais lorsqu’Ornan eut levé les yeux, et qu’il eut vu l’ange du Seigneur, ainsi que ses quatre fils, ils se cachèrent; car, en ce moment-là, il battait du blé dans son aire.
21 Sai Dawuda ya kusato, sa’ad da Ornan ya duba sai ya gan shi, ya bar masussukar ya rusuna a gaban Dawuda da fuskarsa har ƙasa.
Lors donc que David venait vers Ornan, Ornan l’aperçut, et s’avança de l’aire au-devant de lui, puis se prosterna devant lui, incliné vers la terre.
22 Dawuda ya ce wa Ornan, “Ka ba ni masussukarka saboda in gina bagade wa Ubangiji, don annobar da take kan mutane tă daina. Ka sayar mini ita a cikakken kuɗinta.”
Et David lui dit: Donne-moi la place de ton aire, afin que j’y bâtisse un autel au Seigneur; en sorte que tu reçoives autant d’argent qu’elle vaut, et que la plaie soit détournée du peuple.
23 Ornan ya ce wa Dawuda, “Ka karɓa! Bari ranka yă daɗe, sarki yă yi duk abin da ya ga ya yi masa kyau. Duba, zan ba da shanu domin hadaya ta ƙonawa, da itacen sussuka, da kuma alkama domin hadaya ta gari. Zan ba da dukan wannan.”
Or Ornan répondit à David: Prenez, et que mon seigneur le roi fasse ce qui lui plaît: et je lui donne aussi les bœufs pour l’holocauste, les herses pour le bois, et le blé pour le sacrifice; je lui donne tout cela avec plaisir.
24 Amma Sarki Dawuda ya amsa wa Ornan ya ce, “A’a, na nace zan biya cikakken kuɗinta. Ba zan karɓi abinka kawai don Ubangiji ba, ko in miƙa hadaya ta ƙonawar da ba tă ci mini wani abu ba.”
Et le roi David lui dit: Pas du tout, la chose ne se fera point ainsi, mais je donnerai autant d’argent qu’elle en vaut; car je ne dois pas te l’ôter, et offrir ainsi au Seigneur des holocaustes qui ne me coûtent rien.
25 Saboda haka Dawuda ya biya Ornan shekel ɗari shida na zinariya saboda wurin.
David donna donc à Ornan, pour la place de l’aire, six cents sicles d’or d’un poids très juste.
26 Dawuda ya gina bagade wa Ubangiji a can ya kuma miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama, Ubangiji kuwa ya amsa masa ta wurin wuta daga sama a kan bagaden hadaya ta ƙonawa.
Et il bâtit là un autel au Seigneur, et il offrit des holocaustes et des sacrifices pacifiques; et il invoqua le Seigneur, qui l’exauça par le moyen du feu descendu du ciel sur l’autel de l’holocauste.
27 Sa’an nan Ubangiji ya yi magana ga mala’ikan, ya kuma mayar da takobinsa a kube.
Et le Seigneur ordonna à l’ange, et il remit son glaive dans le fourreau.
28 A lokacin, sa’ad da Dawuda ya ga cewa Ubangiji ya amsa masa a masussukar Ornan mutumin Yebus, sai ya miƙa hadayu a can.
Aussitôt donc David, voyant que le Seigneur l’avait exaucé dans l’aire d’Ornan, le Jébuséen, immola dans ce lieu des victimes.
29 Tabanakul na Ubangiji da Musa ya yi a hamada, da kuma bagaden hadaya ta ƙonawa a lokacin suna a tudun Gibeyon.
Mais le tabernacle du Seigneur que Moïse avait fait dans le désert, et l’autel des holocaustes, étaient à cette époque au haut lieu de Gabaon.
30 Amma Dawuda bai iya zuwa gabansa don yă yi tambaya ga Allah ba, gama yana jin tsoron takobin mala’ikan Ubangiji.
Et David n’eut pas la force d’aller jusqu’à l’autel pour y prier Dieu, parce qu’il avait été frappé d’une trop grande crainte en voyant le glaive de l’ange du Seigneur.

< 1 Tarihi 21 >