< 1 Tarihi 21 >

1 Sai Shaiɗan ya tashi gāba da Isra’ila, ya zuga Dawuda ya ƙidaya Isra’ila.
Et le diable se leva contre Israël; il excita le roi David à faire le dénombrement du peuple.
2 Saboda haka Dawuda ya ce wa Yowab da shugabannin mayaƙa, “Ku tafi ku ƙidaya Isra’ilawa daga Beyersheba zuwa Dan. Ku kawo mini labarin saboda in san su nawa ne.”
Le roi dit donc à Joab et aux chefs de l'armée: Allez et faites le dénombrement d'Israël, depuis Dan jusqu'à Bersabée; puis, rapportez-le-moi, et je saurai leur nombre.
3 Amma Yowab ya amsa ya ce, “Ubangiji ya riɓaɓɓanya mayaƙansa fiye da sau ɗari. Ranka yă daɗe sarki, dukansu ba bayin shugabana ba ne? Me ya sa ranka yă daɗe yake so yă yi haka? Me zai sa ka kawo laifi a kan Isra’ila?”
Joab répondit: Puisse le Seigneur ajouter à son peuple et le rendre cent fois aussi nombreux qu'il l'est, et puisse le roi mon maître le voir de ses yeux; puissent le voir aussi les serviteurs de mon maître; mais pourquoi mon maître a-t-il formé ce dessein? Est-ce pour qu'il soit imputé à péché au peuple d'Israël?
4 Amma sarki ya nace a kan maganar da ya yi wa Yowab. Sai Yowab ya tashi ya tafi cikin dukan Isra’ila, ya kewaye sa’an nan ya dawo Urushalima.
Mais, la volonté du roi prévalut sur Joab, et Joab partit, et il parcourut tout Israël, et il revint à Jérusalem.
5 Yowab ya ba labarin yawan mayaƙan wa Dawuda. A cikin Isra’ila akwai mutum miliyon da dubu ɗari ɗaya waɗanda za su iya riƙe takobi, haɗe da dubu ɗari huɗu da saba’in a Yahuda.
Et Joab remit à David le dénombrement du peuple qu'il avait recensé: il y avait en tout Israël onze cent mille hommes tirant l'épée, et en Juda étaient quatre cent soixante-dix mille hommes tirant l'épée.
6 Amma Yowab bai haɗa da mutanen Lawi da na Benyamin a ƙidayar ba, domin bai ji daɗin umarnin sarki ba.
Et Joab n'avait compté ni Lévi, ni Benjamin, parce qu'il avait cédé à contre-cœur au roi.
7 Wannan umarnin mugu ne a gaban Allah; saboda haka ya hukunta Isra’ila.
Et la chose fut mauvaise devant Dieu, et il frappa Israël.
8 Sai Dawuda ya ce wa Allah, “Na yi zunubi ƙwarai ta wurin yin wannan. Yanzu, na roƙe ka, ka ɗauke laifin bawanka. Na yi wauta sosai.”
Et David dit à Dieu: J'ai gravement péché en ce que je viens de faire, et maintenant remettez à votre serviteur son iniquité, car j'ai commis une insigne folie.
9 Sai Ubangiji ya ce wa Gad, mai duba na Dawuda,
Et le Seigneur parla à Gad le voyant, et il lui dit:
10 “Tafi ka faɗa wa Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce ina ba ka abubuwa uku. Ka zaɓi ɗaya daga cikinsu don in aikata a kanka.’”
Pars et adresse-toi à David, disant: Voici ce que dit le Seigneur: Je t'apporte trois choses; choisis pour toi l'une d'elles, et tu l'auras.
11 Saboda haka Gad ya tafi wurin Dawuda ya ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka yi zaɓi,
Gad alla trouver David, et il lui dit: Voici ce que dit le Seigneur: Choisis pour toi,
12 shekara uku na yunwa, wata uku na shan ɗibga a gaban abokan gābanka, sa’ad da za su bi suna kakkashe ku, ko kuwa kwana uku na takobin Ubangiji, ranakun annoba a cikin ƙasar, mala’ikan Ubangiji zai hallaka kowane sashe na Isra’ila.’ Yanzu sai ka yanke shawara yadda zan amsa wa wanda ya aiko ni.”
Ou trois ans de famine, ou trois mois pendant lesquels tu fuiras devant tes ennemis qui te détruiront par le glaive, ou trois jours de mort causée par l'épée du Seigneur en toute cette terre, et par l'ange exterminateur parcourant tout l'héritage d'Israël: vois donc ce que je dois répondre à Celui qui m'envoie te répéter sa parole.
13 Dawuda ya ce wa Gad, “Na shiga uku. Bari in fāɗa a hannuwan Ubangiji, gama jinƙansa yana da girma sosai; amma kada ka bari in fāɗa a hannuwan mutane.”
Et David dit à Gad: Le choix des trois parts m'est cruel; mais j'aime mieux me livrer aux mains du Seigneur, parce qu'il a eu souvent compassion de moi; je ne tomberai point dans les mains des hommes.
14 Sai Ubangiji ya aiko da annoba a kan Isra’ila, mutane duba saba’in na Isra’ila suka mutu.
Et le Seigneur envoya la mort en Israël, et soixante-dix mille hommes d'Israël périrent.
15 Allah kuwa ya aiki mala’ika yă hallaka Urushalima. Amma yayinda mala’ikan yana gab da yin haka, sai Ubangiji ya gani ya kuma yi nadama saboda masifar, sai ya ce wa mala’ikan wanda yake hallaka mutane, “Ya isa! Janye hannunka.” Mala’ikan Ubangiji kuwa yana tsaye a masussukar Ornan mutumin Yebus.
Le Seigneur envoya aussi l'ange à Jérusalem pour l'exterminer, et comme il frappait, le Seigneur le vit et se repentit de tout ce mal, et il dit à l'ange exterminateur: C'est assez, arrête ta main. Or, l'ange du Seigneur était auprès de l'aire d'Orna le Jébuséen.
16 Sai Dawuda ya ɗaga ido ya ga mala’ikan Ubangiji tsaye tsakanin sama da duniya, da takobi a zāre a hannunsa ya miƙa a kan Urushalima. Sai Dawuda da dattawa, saye da rigunan makoki suka fāɗi rubda jiki.
David, ayant levé les yeux, vit l'ange du Seigneur se tenant entre la terre et le ciel; il avait à la main son épée nue, et il l'étendait sur Jérusalem. Et David et les anciens couverts de cilices tombèrent la face contre terre.
17 Dawuda ya ce wa Allah, “Ba ni ba ne na umarta a ƙidaya mayaƙan? Ni ne wanda ya yi zunubin da kuma abin da ba daidai ba. Waɗannan dai tumaki ne. Me suka yi? Ya Ubangiji Allahna, bari hannunka ya fāɗi a kaina da kuma iyalina, amma kada ka bar wannan annoba ya kasance a kan mutanenka.”
Et David dit à Dieu: N'est-ce pas moi qui ai prescrit de faire le dénombrement du peuple? C'est moi qui suis le coupable; j'ai grandement péché. Mais ces brebis qu'ont-elles fait? Seigneur mon Dieu, que votre main soit contre moi et contre la maison de mon père; qu'elle épargne ce peuple qui périt, ô Seigneur.
18 Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya umarci Gad yă faɗa wa Dawuda yă haura yă gina bagade wa Ubangiji a masussukar Ornan mutumin Yebus.
Et l'ange du Seigneur dit à Gad de prescrire à David qu'il allât élever un autel au Seigneur dans l'aire d'Orna le Jébuséen.
19 Saboda haka Dawuda ya haura cikin biyayya ga maganar da Allah ya yi da sunan Ubangiji.
Et David sortit, selon la parole que Gad lui avait dite au nom du Seigneur.
20 Yayinda Ornan yake sussukar alkama, sai ya juya ya ga mala’ika;’ya’yansa maza guda huɗu da suke tare da shi suka ɓuya.
Et Orna se retourna, et il vit le roi et quatre de ses fils, tous se cachant, et Orna était à vanner du froment.
21 Sai Dawuda ya kusato, sa’ad da Ornan ya duba sai ya gan shi, ya bar masussukar ya rusuna a gaban Dawuda da fuskarsa har ƙasa.
Et David arriva auprès d'Orna, et Orna, quittant l'aire, se prosterna la face contre terre devant David.
22 Dawuda ya ce wa Ornan, “Ka ba ni masussukarka saboda in gina bagade wa Ubangiji, don annobar da take kan mutane tă daina. Ka sayar mini ita a cikakken kuɗinta.”
Et David dit à Orna: Donne-moi l'emplacement de ton aire, et j'y bâtirai un autel au Seigneur; donne-le-moi à prix d'argent, et le fléau cessera de frapper le peuple.
23 Ornan ya ce wa Dawuda, “Ka karɓa! Bari ranka yă daɗe, sarki yă yi duk abin da ya ga ya yi masa kyau. Duba, zan ba da shanu domin hadaya ta ƙonawa, da itacen sussuka, da kuma alkama domin hadaya ta gari. Zan ba da dukan wannan.”
Et Orna dit à David: Que le roi mon maître prenne et consacre ce que bon lui semble. Voici mes bœufs pour l'holocauste, ma charrue pour le briller, et mon blé pour le sacrifice; je te donne tout.
24 Amma Sarki Dawuda ya amsa wa Ornan ya ce, “A’a, na nace zan biya cikakken kuɗinta. Ba zan karɓi abinka kawai don Ubangiji ba, ko in miƙa hadaya ta ƙonawar da ba tă ci mini wani abu ba.”
Et le roi David dit à Orna: Nullement; certes, j'achèterai toutes ces choses, car elles valent de l'argent; je ne prendrai, pour le Seigneur, rien de ce qui est à toi; je ne présenterai pas au Seigneur un holocauste qui ne me coûte rien.
25 Saboda haka Dawuda ya biya Ornan shekel ɗari shida na zinariya saboda wurin.
David donna donc à Orna, pour son terrain, six cents sicles d'or, au poids du sicle du sanctuaire.
26 Dawuda ya gina bagade wa Ubangiji a can ya kuma miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama, Ubangiji kuwa ya amsa masa ta wurin wuta daga sama a kan bagaden hadaya ta ƙonawa.
Il bâtit l'autel du Seigneur, sur lequel il offrit des holocaustes et des hosties pacifiques; enfin, il cria au Seigneur, et le Seigneur l'exauça; le feu du ciel, descendant sur l'autel de l'holocauste, consuma la victime.
27 Sa’an nan Ubangiji ya yi magana ga mala’ikan, ya kuma mayar da takobinsa a kube.
Et le Seigneur parla à l'ange, et l'ange remit l'épée dans le fourreau.
28 A lokacin, sa’ad da Dawuda ya ga cewa Ubangiji ya amsa masa a masussukar Ornan mutumin Yebus, sai ya miƙa hadayu a can.
Dès lors, David, ayant vu que le Seigneur lui répondait dans l'aire d'Orna le Jébuséen, en fit un lieu de sacrifices.
29 Tabanakul na Ubangiji da Musa ya yi a hamada, da kuma bagaden hadaya ta ƙonawa a lokacin suna a tudun Gibeyon.
Or, en ce temps-là, le tabernacle du Seigneur que Moïse avait fait dans le désert, et l'autel des holocaustes, étaient sur le haut lieu de Gabaon. Par crainte de l'ange exterminateur.
30 Amma Dawuda bai iya zuwa gabansa don yă yi tambaya ga Allah ba, gama yana jin tsoron takobin mala’ikan Ubangiji.
Et David n'avait pu s'y transporter pour prier le Seigneur; il ne s'était point empressé d'y aller, à cause de l'épée de l'ange du Seigneur.

< 1 Tarihi 21 >