< 1 Tarihi 21 >
1 Sai Shaiɗan ya tashi gāba da Isra’ila, ya zuga Dawuda ya ƙidaya Isra’ila.
Satan se tint contre Israël, et il excita David à faire le dénombrement d’Israël.
2 Saboda haka Dawuda ya ce wa Yowab da shugabannin mayaƙa, “Ku tafi ku ƙidaya Isra’ilawa daga Beyersheba zuwa Dan. Ku kawo mini labarin saboda in san su nawa ne.”
Et David dit à Joab et aux chefs du peuple: « Allez, comptez Israël depuis Bersabée jusqu’à Dan, et faites-moi un rapport, afin que je sache leur nombre. »
3 Amma Yowab ya amsa ya ce, “Ubangiji ya riɓaɓɓanya mayaƙansa fiye da sau ɗari. Ranka yă daɗe sarki, dukansu ba bayin shugabana ba ne? Me ya sa ranka yă daɗe yake so yă yi haka? Me zai sa ka kawo laifi a kan Isra’ila?”
Joab répondit: « Que Yahweh ajoute à son peuple cent fois ce qu’il y en a! O roi, monseigneur, ne sont-ils pas tous esclaves de mon seigneur? Pourquoi donc mon seigneur demande-t-il cela? Pourquoi faire venir le péché sur Israël? »
4 Amma sarki ya nace a kan maganar da ya yi wa Yowab. Sai Yowab ya tashi ya tafi cikin dukan Isra’ila, ya kewaye sa’an nan ya dawo Urushalima.
Mais la parole du roi prévalut contre Joab. Joab partit et parcourut tout Israël, et il revint à Jérusalem.
5 Yowab ya ba labarin yawan mayaƙan wa Dawuda. A cikin Isra’ila akwai mutum miliyon da dubu ɗari ɗaya waɗanda za su iya riƙe takobi, haɗe da dubu ɗari huɗu da saba’in a Yahuda.
Et Joab remit à David le rôle du dénombrement du peuple: il y avait dans tout Israël onze cent mille hommes tirant l’épée, et en Juda quatre cent soixante-dix mille hommes tirant l’épée.
6 Amma Yowab bai haɗa da mutanen Lawi da na Benyamin a ƙidayar ba, domin bai ji daɗin umarnin sarki ba.
Il ne fit pas le dénombrement de Lévi et de Benjamin au milieu d’eux, car l’ordre du roi répugnait à Joab.
7 Wannan umarnin mugu ne a gaban Allah; saboda haka ya hukunta Isra’ila.
Dieu vit de mauvais œil cette affaire, et il frappa Israël.
8 Sai Dawuda ya ce wa Allah, “Na yi zunubi ƙwarai ta wurin yin wannan. Yanzu, na roƙe ka, ka ɗauke laifin bawanka. Na yi wauta sosai.”
Et David dit à Dieu: « J’ai commis un grand péché en faisant cela. Maintenant, ôtez, je vous prie, l’iniquité de votre serviteur, car j’ai tout à fait agi en insensé. »
9 Sai Ubangiji ya ce wa Gad, mai duba na Dawuda,
Yahweh parla à Gad, le voyant de David, en ces termes:
10 “Tafi ka faɗa wa Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce ina ba ka abubuwa uku. Ka zaɓi ɗaya daga cikinsu don in aikata a kanka.’”
« Va et parle à David en ces termes: Ainsi parle Yahweh: Je pose devant toi trois choses; choisis-en une, et je te la ferai. »
11 Saboda haka Gad ya tafi wurin Dawuda ya ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka yi zaɓi,
Gad vint vers David et lui dit: « Ainsi parle Yahweh: Choisis,
12 shekara uku na yunwa, wata uku na shan ɗibga a gaban abokan gābanka, sa’ad da za su bi suna kakkashe ku, ko kuwa kwana uku na takobin Ubangiji, ranakun annoba a cikin ƙasar, mala’ikan Ubangiji zai hallaka kowane sashe na Isra’ila.’ Yanzu sai ka yanke shawara yadda zan amsa wa wanda ya aiko ni.”
ou trois années de famine, ou trois mois durant lesquels tu seras emporté devant tes adversaires et atteint par le glaive de tes ennemis, ou trois jours durant lesquels le glaive de Yahweh et la peste seront dans le pays, et l’ange de Yahweh opérera la destruction dans tout le territoire d’Israël. Maintenant, vois ce que je dois répondre à celui qui m’envoie. »
13 Dawuda ya ce wa Gad, “Na shiga uku. Bari in fāɗa a hannuwan Ubangiji, gama jinƙansa yana da girma sosai; amma kada ka bari in fāɗa a hannuwan mutane.”
David dit à Gad: « Je suis dans une cruelle angoisse. Ah! que je tombe entre les mains de Yahweh, car ses miséricordes sont très grandes, et que je ne tombe pas entre les mains des hommes! »
14 Sai Ubangiji ya aiko da annoba a kan Isra’ila, mutane duba saba’in na Isra’ila suka mutu.
Et Yahweh envoya une peste en Israël, et il tomba soixante-dix mille hommes en Israël.
15 Allah kuwa ya aiki mala’ika yă hallaka Urushalima. Amma yayinda mala’ikan yana gab da yin haka, sai Ubangiji ya gani ya kuma yi nadama saboda masifar, sai ya ce wa mala’ikan wanda yake hallaka mutane, “Ya isa! Janye hannunka.” Mala’ikan Ubangiji kuwa yana tsaye a masussukar Ornan mutumin Yebus.
Et Dieu envoya un ange à Jérusalem pour la détruire; et pendant qu’il détruisait, Yahweh vit et se repentit de ce mal, et il dit à l’ange qui détruisait: « Assez! retire maintenant ta main. » L’ange de Yahweh se tenait près de l’aire d’Ornan, le Jésubéen.
16 Sai Dawuda ya ɗaga ido ya ga mala’ikan Ubangiji tsaye tsakanin sama da duniya, da takobi a zāre a hannunsa ya miƙa a kan Urushalima. Sai Dawuda da dattawa, saye da rigunan makoki suka fāɗi rubda jiki.
David, ayant levé les yeux, vit l’ange de Yahweh se tenant entre la terre et le ciel, et ayant à la main son épée nue, tournée contre Jérusalem. Alors David et les anciens, couverts de sacs, tombèrent sur leur visage.
17 Dawuda ya ce wa Allah, “Ba ni ba ne na umarta a ƙidaya mayaƙan? Ni ne wanda ya yi zunubin da kuma abin da ba daidai ba. Waɗannan dai tumaki ne. Me suka yi? Ya Ubangiji Allahna, bari hannunka ya fāɗi a kaina da kuma iyalina, amma kada ka bar wannan annoba ya kasance a kan mutanenka.”
Et David dit à Dieu: « N’est-ce pas moi qui ai dit de faire le dénombrement du peuple? C’est moi qui ai péché et qui ai fait le mal; mais celles-là, ces brebis, qu’ont-elles fait? Yahweh, mon Dieu, que votre main soit donc sur moi et sur la maison de mon père, mais non sur votre peuple pour sa ruine. »
18 Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya umarci Gad yă faɗa wa Dawuda yă haura yă gina bagade wa Ubangiji a masussukar Ornan mutumin Yebus.
L’ange de Yahweh ordonna à Gad de dire à David de monter pour élever un autel à Yahweh sur l’aire d’Ornan, le Jébuséen.
19 Saboda haka Dawuda ya haura cikin biyayya ga maganar da Allah ya yi da sunan Ubangiji.
David monta, selon la parole de Gad qu’il avait dite au nom de Yahweh.
20 Yayinda Ornan yake sussukar alkama, sai ya juya ya ga mala’ika;’ya’yansa maza guda huɗu da suke tare da shi suka ɓuya.
Ornan, s’étant retourné, vit l’ange, et il se cacha, lui et ses quatre fils: Ornan battait alors du froment.
21 Sai Dawuda ya kusato, sa’ad da Ornan ya duba sai ya gan shi, ya bar masussukar ya rusuna a gaban Dawuda da fuskarsa har ƙasa.
Lorsque David arriva auprès d’Ornan, Ornan regarda et il aperçut David; sortant aussitôt de l’aire, il se prosterna devant David, le visage contre terre.
22 Dawuda ya ce wa Ornan, “Ka ba ni masussukarka saboda in gina bagade wa Ubangiji, don annobar da take kan mutane tă daina. Ka sayar mini ita a cikakken kuɗinta.”
David dit à Ornan: « Cède-moi l’emplacement de l’aire, et j’y bâtirai un autel à Yahweh; cède-le-moi pour sa pleine valeur en argent, pour que la plaie se retire de dessus le peuple. »
23 Ornan ya ce wa Dawuda, “Ka karɓa! Bari ranka yă daɗe, sarki yă yi duk abin da ya ga ya yi masa kyau. Duba, zan ba da shanu domin hadaya ta ƙonawa, da itacen sussuka, da kuma alkama domin hadaya ta gari. Zan ba da dukan wannan.”
Ornan dit à David: « Prends-le, et que mon seigneur le roi fasse ce qu’il trouvera bon. Vois, je donne les bœufs pour l’holocauste, les traîneaux pour le bois, et le froment pour l’oblation; je donne tout cela. »
24 Amma Sarki Dawuda ya amsa wa Ornan ya ce, “A’a, na nace zan biya cikakken kuɗinta. Ba zan karɓi abinka kawai don Ubangiji ba, ko in miƙa hadaya ta ƙonawar da ba tă ci mini wani abu ba.”
Mais le roi David dit à Ornan: « Non! Mais je veux l’acheter contre sa pleine valeur en argent, car je ne prendrai pas ce qui est à toi pour Yahweh, et je n’offrirai pas un holocauste qui ne me coûte rien. »
25 Saboda haka Dawuda ya biya Ornan shekel ɗari shida na zinariya saboda wurin.
David donna à Ornan un poids de six cents sicles d’or pour l’emplacement.
26 Dawuda ya gina bagade wa Ubangiji a can ya kuma miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama, Ubangiji kuwa ya amsa masa ta wurin wuta daga sama a kan bagaden hadaya ta ƙonawa.
Et David bâtit là un autel à Yahweh, et offrit des holocaustes et des sacrifices pacifiques. Il cria vers Yahweh, et Yahweh lui répondit par le feu qui descendit du ciel sur l’autel de l’holocauste.
27 Sa’an nan Ubangiji ya yi magana ga mala’ikan, ya kuma mayar da takobinsa a kube.
Et Yahweh parla à l’ange, et celui-ci remit son épée dans le fourreau.
28 A lokacin, sa’ad da Dawuda ya ga cewa Ubangiji ya amsa masa a masussukar Ornan mutumin Yebus, sai ya miƙa hadayu a can.
En ce temps-là, David, voyant que Yahweh l’avait exaucé dans l’aire d’Ornan, le Jébuséen, y offrait des sacrifices.
29 Tabanakul na Ubangiji da Musa ya yi a hamada, da kuma bagaden hadaya ta ƙonawa a lokacin suna a tudun Gibeyon.
Le tabernacle de Yahweh, que Moïse avait construit au désert, et l’autel des holocaustes étaient en ce temps-là sur le haut lieu de Gabaon.
30 Amma Dawuda bai iya zuwa gabansa don yă yi tambaya ga Allah ba, gama yana jin tsoron takobin mala’ikan Ubangiji.
Mais David ne pouvait pas aller devant cet autel pour honorer Dieu, parce qu’il avait été terrifié par l’épée de l’ange de Yahweh.