< 1 Tarihi 21 >

1 Sai Shaiɗan ya tashi gāba da Isra’ila, ya zuga Dawuda ya ƙidaya Isra’ila.
Ja saatana seisoi Israelia vastaan ja kehoitti Davidin lukemaan Israelia.
2 Saboda haka Dawuda ya ce wa Yowab da shugabannin mayaƙa, “Ku tafi ku ƙidaya Isra’ilawa daga Beyersheba zuwa Dan. Ku kawo mini labarin saboda in san su nawa ne.”
Ja David sanoi Joabille ja kansan ylimmäisille: menkäät ja lukekaat Israel Bersebasta Daniin saakka, ja tuokaat minulle, että minä tietäisin heidän lukunsa.
3 Amma Yowab ya amsa ya ce, “Ubangiji ya riɓaɓɓanya mayaƙansa fiye da sau ɗari. Ranka yă daɗe sarki, dukansu ba bayin shugabana ba ne? Me ya sa ranka yă daɗe yake so yă yi haka? Me zai sa ka kawo laifi a kan Isra’ila?”
Joab sanoi: Herra enentäköön kansansa sata kertaa suuremmaksi kuin se nyt on. Herrani kuningas, eikö nämät kaikki ole herrani palveliat? miksi siis herrani kysyy sitä? miksi se tulis synniksi Israelille?
4 Amma sarki ya nace a kan maganar da ya yi wa Yowab. Sai Yowab ya tashi ya tafi cikin dukan Isra’ila, ya kewaye sa’an nan ya dawo Urushalima.
Mutta kuninkaan sana voitti Joabin. Ja Joab meni ja vaelsi koko Israelin ympäri, ja tuli Jerusalemiin.
5 Yowab ya ba labarin yawan mayaƙan wa Dawuda. A cikin Isra’ila akwai mutum miliyon da dubu ɗari ɗaya waɗanda za su iya riƙe takobi, haɗe da dubu ɗari huɗu da saba’in a Yahuda.
Ja Joab antoi Davidille luetun kansan luvun: ja koko Israelissa oli yksitoistakymmentä kertaa satatuhatta miestä, jotka miekkaa ulos vetivät. Ja Juudassa neljäsataa tuhatta ja seitsemänkymmentä tuhatta miekan vetävää miestä.
6 Amma Yowab bai haɗa da mutanen Lawi da na Benyamin a ƙidayar ba, domin bai ji daɗin umarnin sarki ba.
Mutta Leviä ja BenJaminia ei hän näiden sekaan lukenut; sillä Joab kauhistui kuninkaan sanasta.
7 Wannan umarnin mugu ne a gaban Allah; saboda haka ya hukunta Isra’ila.
Mutta asia oli paha Jumalan silmäin edessä; ja hän löi Israelin.
8 Sai Dawuda ya ce wa Allah, “Na yi zunubi ƙwarai ta wurin yin wannan. Yanzu, na roƙe ka, ka ɗauke laifin bawanka. Na yi wauta sosai.”
Ja David sanoi Jumalalle: minä olen raskaasti syntiä tehnyt, että minä sen tehnyt olen: mutta ota palvelias vääryys pois; sillä minä olen sangen tyhmästi tehnyt.
9 Sai Ubangiji ya ce wa Gad, mai duba na Dawuda,
Ja Herra puhui Gadille, Davidin näkiälle, sanoen:
10 “Tafi ka faɗa wa Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce ina ba ka abubuwa uku. Ka zaɓi ɗaya daga cikinsu don in aikata a kanka.’”
Mene ja puhu Davidille, sanoen: näin sanoo Herra: kolme minä panen sinun etees: valitse yksi niistä, ja minä teen sen sinulle.
11 Saboda haka Gad ya tafi wurin Dawuda ya ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka yi zaɓi,
Ja kuin Gad tuli Davidin tykö, sanoi hän hänelle: näin sanoo Herra: valitse sinulles:
12 shekara uku na yunwa, wata uku na shan ɗibga a gaban abokan gābanka, sa’ad da za su bi suna kakkashe ku, ko kuwa kwana uku na takobin Ubangiji, ranakun annoba a cikin ƙasar, mala’ikan Ubangiji zai hallaka kowane sashe na Isra’ila.’ Yanzu sai ka yanke shawara yadda zan amsa wa wanda ya aiko ni.”
Taikka kolme nälkävuotta, taikka kolmen kuukauden pako vihollistes edessä ja vainollises miekan edessä, että se on käsittävä sinun, eli kolmeksi päiväksi Herran miekka ja ruttotauti maalle, niin että Herran enkeli kadottaa kaikki Israelin rajoilla. Niin ajattele siis nyt, mitä minun pitää häntä vastaamaan, joka minun on lähettänyt.
13 Dawuda ya ce wa Gad, “Na shiga uku. Bari in fāɗa a hannuwan Ubangiji, gama jinƙansa yana da girma sosai; amma kada ka bari in fāɗa a hannuwan mutane.”
David sanoi Gadille: minulla on suuri ahdistus; kuitenkin tahdon minä langeta Herran käsiin, sillä hänen laupiutensa on sangen suuri, en tahdo langeta ihmisten käsiin.
14 Sai Ubangiji ya aiko da annoba a kan Isra’ila, mutane duba saba’in na Isra’ila suka mutu.
Ja Herra antoi ruttotaudin tulla Israeliin, niin että Israelista lankesi seitsemänkymmentä tuhatta miestä.
15 Allah kuwa ya aiki mala’ika yă hallaka Urushalima. Amma yayinda mala’ikan yana gab da yin haka, sai Ubangiji ya gani ya kuma yi nadama saboda masifar, sai ya ce wa mala’ikan wanda yake hallaka mutane, “Ya isa! Janye hannunka.” Mala’ikan Ubangiji kuwa yana tsaye a masussukar Ornan mutumin Yebus.
Ja Jumala lähetti enkelin Jerusalemiin hukuttamaan sitä; ja hukuttaissa katsoi Herra siihen ja katui sitä pahaa, ja sanoi enkelille, joka hukutti: nyt on kyllä, pidä kätes ylös! Mutta Herran enkeli seisoi Ornanin Jebusilaisen riihen tykönä.
16 Sai Dawuda ya ɗaga ido ya ga mala’ikan Ubangiji tsaye tsakanin sama da duniya, da takobi a zāre a hannunsa ya miƙa a kan Urushalima. Sai Dawuda da dattawa, saye da rigunan makoki suka fāɗi rubda jiki.
Ja David nosti silmänsä ja sai nähdä Herran enkelin seisovan maan ja taivaan välillä, ja ulosvedetyn miekan hänen kädessänsä ojennetun Jerusalemin päälle. Niin lankesi David ja vanhimmat kasvoillensa, puetetut säkeillä.
17 Dawuda ya ce wa Allah, “Ba ni ba ne na umarta a ƙidaya mayaƙan? Ni ne wanda ya yi zunubin da kuma abin da ba daidai ba. Waɗannan dai tumaki ne. Me suka yi? Ya Ubangiji Allahna, bari hannunka ya fāɗi a kaina da kuma iyalina, amma kada ka bar wannan annoba ya kasance a kan mutanenka.”
Ja David sanoi Jumalalle: enkö minä se ole, joka annoin lukea kansan? minä se olen, joka syntiä tein ja aivan pahoin tein. Mitä nämät lampaat tehneet ovat? Herra Jumalani, anna kätes olla minun ja minun isäni huoneen päälle, ja ei sinun kansalles vaivaksi.
18 Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya umarci Gad yă faɗa wa Dawuda yă haura yă gina bagade wa Ubangiji a masussukar Ornan mutumin Yebus.
Ja Herran enkeli sanoi Gadille että hän sanois Davidille, että David menis ja rakentais Herralle alttarin Ornanin Jebusilaisen riiheen.
19 Saboda haka Dawuda ya haura cikin biyayya ga maganar da Allah ya yi da sunan Ubangiji.
Ja David meni Gadin sanan jälkeen, jonka hän Herran nimeen puhunut oli.
20 Yayinda Ornan yake sussukar alkama, sai ya juya ya ga mala’ika;’ya’yansa maza guda huɗu da suke tare da shi suka ɓuya.
Vaan kuin Ornan käänsi itsensä ja näki neljän poikansa kanssa enkelin, lymyttivät he heitänsä; sillä Ornan tappoi nisuja.
21 Sai Dawuda ya kusato, sa’ad da Ornan ya duba sai ya gan shi, ya bar masussukar ya rusuna a gaban Dawuda da fuskarsa har ƙasa.
Kuin David meni Ornanin tykö, näki Ornan ja havaitsi Davidin, ja meni riihestä ulos ja lankesi kasvoillensa Davidin eteen maahan.
22 Dawuda ya ce wa Ornan, “Ka ba ni masussukarka saboda in gina bagade wa Ubangiji, don annobar da take kan mutane tă daina. Ka sayar mini ita a cikakken kuɗinta.”
Ja David sanoi Ornanille: anna minulle sen riihen sia, rakentaakseni siihen Herralle alttarin; anna se minulle täyden rahan edestä, että vitsaus lakkais kansasta.
23 Ornan ya ce wa Dawuda, “Ka karɓa! Bari ranka yă daɗe, sarki yă yi duk abin da ya ga ya yi masa kyau. Duba, zan ba da shanu domin hadaya ta ƙonawa, da itacen sussuka, da kuma alkama domin hadaya ta gari. Zan ba da dukan wannan.”
Ja Ornan sanoi Davidille: ota sinulles ja tee, herrani kuningas, kuin sinulle kelpaa. Katso, minä annan myös härkiä polttouhriksi ja aseita puiksi, ja nisuja ruokauhriksi: kaikki minä annan.
24 Amma Sarki Dawuda ya amsa wa Ornan ya ce, “A’a, na nace zan biya cikakken kuɗinta. Ba zan karɓi abinka kawai don Ubangiji ba, ko in miƙa hadaya ta ƙonawar da ba tă ci mini wani abu ba.”
Mutta kuningas David sanoi Ornanille: ei niin, vaan minä tahdon peräti ostaa sen täydellä rahalla; sillä en minä ota sitä, mikä sinun on, Herralle ja tee polttouhria maksamata.
25 Saboda haka Dawuda ya biya Ornan shekel ɗari shida na zinariya saboda wurin.
Niin David antoi Ornanille sen sian edestä kuudensadan siklin painon kultaa.
26 Dawuda ya gina bagade wa Ubangiji a can ya kuma miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama, Ubangiji kuwa ya amsa masa ta wurin wuta daga sama a kan bagaden hadaya ta ƙonawa.
Ja David rakensi siinä Herralle alttarin ja uhrasi polttouhria ja kiitosuhria, ja rukoili Herraa; ja hän kuuli hänen tulella taivaasta polttouhrin alttarilla.
27 Sa’an nan Ubangiji ya yi magana ga mala’ikan, ya kuma mayar da takobinsa a kube.
Ja Herra sanoi enkelille, että hän pistäis miekkansa tuppeensa.
28 A lokacin, sa’ad da Dawuda ya ga cewa Ubangiji ya amsa masa a masussukar Ornan mutumin Yebus, sai ya miƙa hadayu a can.
Kuin David näki Herran kuulleeksi häntä Ornanin Jebusilaisen riihessä, uhrasi hän siellä.
29 Tabanakul na Ubangiji da Musa ya yi a hamada, da kuma bagaden hadaya ta ƙonawa a lokacin suna a tudun Gibeyon.
Sillä Herran maja, jonka Moses oli tehnyt korvessa, ja polttouhrin alttari olivat silloin Gibeonin korkeudella.
30 Amma Dawuda bai iya zuwa gabansa don yă yi tambaya ga Allah ba, gama yana jin tsoron takobin mala’ikan Ubangiji.
Ja ei David taitanut mennä sen eteen kysymään Jumalaa; sillä hän oli peljästynyt Herran enkelin miekkaa.

< 1 Tarihi 21 >