< 1 Tarihi 21 >

1 Sai Shaiɗan ya tashi gāba da Isra’ila, ya zuga Dawuda ya ƙidaya Isra’ila.
Sotheli Sathan roos ayens Israel, and stiride Dauid for to noumbre Israel.
2 Saboda haka Dawuda ya ce wa Yowab da shugabannin mayaƙa, “Ku tafi ku ƙidaya Isra’ilawa daga Beyersheba zuwa Dan. Ku kawo mini labarin saboda in san su nawa ne.”
And Dauid seide to Joab, and to the princes of the puple, Go ye, and noumbre Israel fro Bersabe til to Dan, and brynge ye the noumbre to me, that Y wite.
3 Amma Yowab ya amsa ya ce, “Ubangiji ya riɓaɓɓanya mayaƙansa fiye da sau ɗari. Ranka yă daɗe sarki, dukansu ba bayin shugabana ba ne? Me ya sa ranka yă daɗe yake so yă yi haka? Me zai sa ka kawo laifi a kan Isra’ila?”
And Joab answeride, The Lord encresse his puple an hundrid fold more than thei ben; my lord the kyng, whether alle ben not thi seruauntis? Whi sekith my lord this thing, that schal be arettid in to synne to Israel?
4 Amma sarki ya nace a kan maganar da ya yi wa Yowab. Sai Yowab ya tashi ya tafi cikin dukan Isra’ila, ya kewaye sa’an nan ya dawo Urushalima.
But the word of the kyng hadde more the maistrie; and Joab yede out, and cumpasside al Israel, and turnede ayen in to Jerusalem.
5 Yowab ya ba labarin yawan mayaƙan wa Dawuda. A cikin Isra’ila akwai mutum miliyon da dubu ɗari ɗaya waɗanda za su iya riƙe takobi, haɗe da dubu ɗari huɗu da saba’in a Yahuda.
And he yaf to Dauid the noumbre of hem, which he hadde cumpassid; and al the noumbre of Israel was foundun a thousynde thousande, and an hundrid thousynde of men, drawynge out swerd; forsothe of Juda weren thre hundrid thousynde, and seuenti thousynde of werriouris.
6 Amma Yowab bai haɗa da mutanen Lawi da na Benyamin a ƙidayar ba, domin bai ji daɗin umarnin sarki ba.
For Joab noumbride not Leuy and Beniamyn, for ayens his wille he dide the comaundement of the kyng.
7 Wannan umarnin mugu ne a gaban Allah; saboda haka ya hukunta Isra’ila.
Forsothe that that was comaundid displeside the Lord, and he smoot Israel.
8 Sai Dawuda ya ce wa Allah, “Na yi zunubi ƙwarai ta wurin yin wannan. Yanzu, na roƙe ka, ka ɗauke laifin bawanka. Na yi wauta sosai.”
And Dauid seide to God, Y synnede greetli that Y wolde do this; Y biseche, do thou awey the wickidnesse of thi seruaunt, for Y dide folili.
9 Sai Ubangiji ya ce wa Gad, mai duba na Dawuda,
And the Lord spak to Gad, the profete of Dauid,
10 “Tafi ka faɗa wa Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce ina ba ka abubuwa uku. Ka zaɓi ɗaya daga cikinsu don in aikata a kanka.’”
and seide, Go thou, and speke to Dauid, and seie to him, The Lord seith these thingis, Y yeue to thee the chesyng of thre thingis; chese thou oon which thou wolt, that Y do to thee.
11 Saboda haka Gad ya tafi wurin Dawuda ya ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka yi zaɓi,
And whanne Gad was comen to Dauid, he seide to Dauid, The Lord seith these thingis, Chese thou that that thou wolt, ether pestilence thre yeer,
12 shekara uku na yunwa, wata uku na shan ɗibga a gaban abokan gābanka, sa’ad da za su bi suna kakkashe ku, ko kuwa kwana uku na takobin Ubangiji, ranakun annoba a cikin ƙasar, mala’ikan Ubangiji zai hallaka kowane sashe na Isra’ila.’ Yanzu sai ka yanke shawara yadda zan amsa wa wanda ya aiko ni.”
ether that thre monethis thou fle thin enemyes and mow not ascape her swerd, ether that the swerd of the Lord and deeth regne thre daies in the lond, and that the aungel of the Lord slee in alle the coostis of Israel. Now therfor se thou, what Y schal answere to hym that sente me.
13 Dawuda ya ce wa Gad, “Na shiga uku. Bari in fāɗa a hannuwan Ubangiji, gama jinƙansa yana da girma sosai; amma kada ka bari in fāɗa a hannuwan mutane.”
And Dauid seide to Gad, Angwischis oppresse me on ech part, but it is betere to me, that Y falle in to the hondis of the Lord, for his merciful doynges ben manye, than in to the hondis of men.
14 Sai Ubangiji ya aiko da annoba a kan Isra’ila, mutane duba saba’in na Isra’ila suka mutu.
Therfor the Lord sente pestilence in to Israel, and seuenti thousynde of men felden doun of Israel.
15 Allah kuwa ya aiki mala’ika yă hallaka Urushalima. Amma yayinda mala’ikan yana gab da yin haka, sai Ubangiji ya gani ya kuma yi nadama saboda masifar, sai ya ce wa mala’ikan wanda yake hallaka mutane, “Ya isa! Janye hannunka.” Mala’ikan Ubangiji kuwa yana tsaye a masussukar Ornan mutumin Yebus.
Also he sente an aungel in to Jerusalem, that he schulde smyte it; and whanne it was smytun, the Lord siy, and hadde merci on the greetnesse of yuel; and comaundide to the aungel that smoot, It suffisith, now thin hond ceesse. Forsothe the aungel of the Lord stood bisidis the cornfloor of Ornam Jebusey.
16 Sai Dawuda ya ɗaga ido ya ga mala’ikan Ubangiji tsaye tsakanin sama da duniya, da takobi a zāre a hannunsa ya miƙa a kan Urushalima. Sai Dawuda da dattawa, saye da rigunan makoki suka fāɗi rubda jiki.
And Dauid reiside hise iyen, and siy the aungel of the Lord stondynge bitwixe heuene and erthe, and a drawun swerd in his hond, and turnede ayens Jerusalem. And bothe he and the grettere men in birthe weren clothid with heiris, and felden doun lowe on the erthe.
17 Dawuda ya ce wa Allah, “Ba ni ba ne na umarta a ƙidaya mayaƙan? Ni ne wanda ya yi zunubin da kuma abin da ba daidai ba. Waɗannan dai tumaki ne. Me suka yi? Ya Ubangiji Allahna, bari hannunka ya fāɗi a kaina da kuma iyalina, amma kada ka bar wannan annoba ya kasance a kan mutanenka.”
And Dauid seide to the Lord, Whether Y am not that comaundide that the puple schulde be noumbrid? Y it am that synnede, Y it am that dide yuel; what disseruid this floc? My Lord God, Y biseche, thin hond be turned `in to me, and `in to the hows of my fadir; but thi puple be not smytun.
18 Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya umarci Gad yă faɗa wa Dawuda yă haura yă gina bagade wa Ubangiji a masussukar Ornan mutumin Yebus.
Forsothe an aungel of the Lord comaundide Gad, that he schulde seie to Dauid, `that he schulde stie, and bilde an auter to the Lord God in the cornfloor of Ornam Jebusei.
19 Saboda haka Dawuda ya haura cikin biyayya ga maganar da Allah ya yi da sunan Ubangiji.
Therfor Dauid stiede bi the word of Gad, which he spak to hym bi the word of the Lord.
20 Yayinda Ornan yake sussukar alkama, sai ya juya ya ga mala’ika;’ya’yansa maza guda huɗu da suke tare da shi suka ɓuya.
Forsothe whanne Ornam hadde `biholde, and hadde seyn the aungel, and hise foure sones `with hym `hadde seyn, thei hidden hem, for in that tyme he threischide whete in the cornfloor.
21 Sai Dawuda ya kusato, sa’ad da Ornan ya duba sai ya gan shi, ya bar masussukar ya rusuna a gaban Dawuda da fuskarsa har ƙasa.
Therfor whanne Dauid cam to Ornam, Ornam bihelde Dauid, and yede forth fro the cornfloor ayens hym, and worschipide hym, lowli on the ground.
22 Dawuda ya ce wa Ornan, “Ka ba ni masussukarka saboda in gina bagade wa Ubangiji, don annobar da take kan mutane tă daina. Ka sayar mini ita a cikakken kuɗinta.”
And Dauid seide to hym, Yyue the place of thi cornfloor to me, that Y bilde ther ynne an auter to the Lord; so that thou take as myche siluer as it is worth, and that the veniaunce ceesse fro the puple.
23 Ornan ya ce wa Dawuda, “Ka karɓa! Bari ranka yă daɗe, sarki yă yi duk abin da ya ga ya yi masa kyau. Duba, zan ba da shanu domin hadaya ta ƙonawa, da itacen sussuka, da kuma alkama domin hadaya ta gari. Zan ba da dukan wannan.”
Forsothe Ornam seide to Dauid, Take thou, and my lord the kyng do what euer thing plesith hym; but also Y yyue oxis in to brent sacrifice, and instrumentis of tree, wherbi cornes ben throischun, in to trees, and wheete in to sacrifice; Y yyue alle thingis wilfully.
24 Amma Sarki Dawuda ya amsa wa Ornan ya ce, “A’a, na nace zan biya cikakken kuɗinta. Ba zan karɓi abinka kawai don Ubangiji ba, ko in miƙa hadaya ta ƙonawar da ba tă ci mini wani abu ba.”
And `Dauid the kyng seide to hym, It schal not be don so, but Y schal yyue siluer as myche as it is worth; for Y owe not take awei fro thee, and offre so to the Lord brent sacrifices freli youun.
25 Saboda haka Dawuda ya biya Ornan shekel ɗari shida na zinariya saboda wurin.
Therfor Dauid yaf to Ornam for the place sixe hundrid siclis of gold of most iust weiyte.
26 Dawuda ya gina bagade wa Ubangiji a can ya kuma miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama, Ubangiji kuwa ya amsa masa ta wurin wuta daga sama a kan bagaden hadaya ta ƙonawa.
And he bildide there an auter to the Lord, and he offride brent sacrifice and pesible sacrifices, and he inwardli clepide God; and God herde hym in fier fro heuene on the auter of brent sacrifice.
27 Sa’an nan Ubangiji ya yi magana ga mala’ikan, ya kuma mayar da takobinsa a kube.
And the Lord comaundide to the aungel, and he turnede his swerd in to the schethe.
28 A lokacin, sa’ad da Dawuda ya ga cewa Ubangiji ya amsa masa a masussukar Ornan mutumin Yebus, sai ya miƙa hadayu a can.
Therfor anoon Dauid siy, that the Lord hadde herd hym in the corn floor of Ornam Jebusey, and he offride there slayn sacrifices.
29 Tabanakul na Ubangiji da Musa ya yi a hamada, da kuma bagaden hadaya ta ƙonawa a lokacin suna a tudun Gibeyon.
Forsothe the tabernacle of the Lord, that Moyses hadde maad in the deseert, and the auter of brent sacrifices, was in that tempest in the hiy place of Gabaon;
30 Amma Dawuda bai iya zuwa gabansa don yă yi tambaya ga Allah ba, gama yana jin tsoron takobin mala’ikan Ubangiji.
and Dauid myyte not go to the auter, to biseche God there, for he was aferd bi ful greet drede, seynge the swerd of the `aungel of the Lord.

< 1 Tarihi 21 >