< 1 Tarihi 21 >

1 Sai Shaiɗan ya tashi gāba da Isra’ila, ya zuga Dawuda ya ƙidaya Isra’ila.
And the Accuser stood up against Israel, and incited David to count Israel.
2 Saboda haka Dawuda ya ce wa Yowab da shugabannin mayaƙa, “Ku tafi ku ƙidaya Isra’ilawa daga Beyersheba zuwa Dan. Ku kawo mini labarin saboda in san su nawa ne.”
And David said to Joab, and to the princes of the people, Go, number Israel from Beer-sheba' even to Dan, and bring their number to me, that I may know it.
3 Amma Yowab ya amsa ya ce, “Ubangiji ya riɓaɓɓanya mayaƙansa fiye da sau ɗari. Ranka yă daɗe sarki, dukansu ba bayin shugabana ba ne? Me ya sa ranka yă daɗe yake so yă yi haka? Me zai sa ka kawo laifi a kan Isra’ila?”
Then said Joab, May the Lord add unto his people, how many soever they be, a hundred-fold more: are they not all, my lord the king, my lord's servants? why then will my lord require this thing? why shall it be a cause of guiltiness for Israel?
4 Amma sarki ya nace a kan maganar da ya yi wa Yowab. Sai Yowab ya tashi ya tafi cikin dukan Isra’ila, ya kewaye sa’an nan ya dawo Urushalima.
Nevertheless the king's word remained firm against Joab; and Joab went out, and moved about throughout all Israel, and came [back] to Jerusalem.
5 Yowab ya ba labarin yawan mayaƙan wa Dawuda. A cikin Isra’ila akwai mutum miliyon da dubu ɗari ɗaya waɗanda za su iya riƙe takobi, haɗe da dubu ɗari huɗu da saba’in a Yahuda.
And Joab gave up the sum of the number of the people unto David: and there were [in] all Israel a thousand times thousand and one hundred thousand men that drew the sword: and [of] Judah were four hundred and seventy thousand men that drew the sword.
6 Amma Yowab bai haɗa da mutanen Lawi da na Benyamin a ƙidayar ba, domin bai ji daɗin umarnin sarki ba.
But Levi and Benjamin did he not count among them: for the king's word was abominable to Joab.
7 Wannan umarnin mugu ne a gaban Allah; saboda haka ya hukunta Isra’ila.
And this thing was displeasing in the eyes of God, and he smote Israel.
8 Sai Dawuda ya ce wa Allah, “Na yi zunubi ƙwarai ta wurin yin wannan. Yanzu, na roƙe ka, ka ɗauke laifin bawanka. Na yi wauta sosai.”
And David said unto God, I have sinned greatly, because I have done this thing; but now, I beseech thee, cause the iniquity of thy servant to pass away; for I have acted very foolishly.
9 Sai Ubangiji ya ce wa Gad, mai duba na Dawuda,
And the Lord spoke unto Gad, David's seer, saying,
10 “Tafi ka faɗa wa Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce ina ba ka abubuwa uku. Ka zaɓi ɗaya daga cikinsu don in aikata a kanka.’”
Go and speak unto David, saying, Thus hath said the Lord, Three things do I offer thee: choose for thyself one of them, and I will do it unto thee.
11 Saboda haka Gad ya tafi wurin Dawuda ya ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka yi zaɓi,
So Gad came to David, and said unto him, Thus hath said the Lord, Select for thyself,
12 shekara uku na yunwa, wata uku na shan ɗibga a gaban abokan gābanka, sa’ad da za su bi suna kakkashe ku, ko kuwa kwana uku na takobin Ubangiji, ranakun annoba a cikin ƙasar, mala’ikan Ubangiji zai hallaka kowane sashe na Isra’ila.’ Yanzu sai ka yanke shawara yadda zan amsa wa wanda ya aiko ni.”
Whether there shall be three years famine; or three months, to be destroyed before thy adversaries, so that the sword of thy enemies overtake thee; or that during three days the sword of the Lord, even the pestilence, shall be in the land, and an angel of the Lord destroying throughout all the boundaries of Israel? And now reflect what word I shall bring back to him that hath sent me.
13 Dawuda ya ce wa Gad, “Na shiga uku. Bari in fāɗa a hannuwan Ubangiji, gama jinƙansa yana da girma sosai; amma kada ka bari in fāɗa a hannuwan mutane.”
And David said unto Gad, I am in a great strait: let me fall then into the hand of the Lord; for his mercies are very great; but let me not fall into the hand of man.
14 Sai Ubangiji ya aiko da annoba a kan Isra’ila, mutane duba saba’in na Isra’ila suka mutu.
So the Lord sent a pestilence in Israel, and there fell of Israel seventy thousand men.
15 Allah kuwa ya aiki mala’ika yă hallaka Urushalima. Amma yayinda mala’ikan yana gab da yin haka, sai Ubangiji ya gani ya kuma yi nadama saboda masifar, sai ya ce wa mala’ikan wanda yake hallaka mutane, “Ya isa! Janye hannunka.” Mala’ikan Ubangiji kuwa yana tsaye a masussukar Ornan mutumin Yebus.
And God sent an angel unto Jerusalem to destroy it; but as he was destroying, the Lord looked on, and he bethought himself of the evil, and said to the angel that destroyed, It is enough: now stay thy hand. And the angel of the Lord was standing by the threshing-floor of Ornan the Jebusite.
16 Sai Dawuda ya ɗaga ido ya ga mala’ikan Ubangiji tsaye tsakanin sama da duniya, da takobi a zāre a hannunsa ya miƙa a kan Urushalima. Sai Dawuda da dattawa, saye da rigunan makoki suka fāɗi rubda jiki.
And David lifted up his eyes, and saw the angel of the Lord standing between the earth and the heavens, with his sword drawn in his hand, stretched out over Jerusalem. Then fell David, with the elders wrapt in sackcloth, upon their faces.
17 Dawuda ya ce wa Allah, “Ba ni ba ne na umarta a ƙidaya mayaƙan? Ni ne wanda ya yi zunubin da kuma abin da ba daidai ba. Waɗannan dai tumaki ne. Me suka yi? Ya Ubangiji Allahna, bari hannunka ya fāɗi a kaina da kuma iyalina, amma kada ka bar wannan annoba ya kasance a kan mutanenka.”
And David said unto God, Was it not I that ordered to count the people? and I am the one that have sinned and have done evil indeed; but these sheep, what have they done? O Lord my God, let thy hand, I pray thee, be against me, and against my father's house, but not against thy people, that there should be a plague.
18 Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya umarci Gad yă faɗa wa Dawuda yă haura yă gina bagade wa Ubangiji a masussukar Ornan mutumin Yebus.
And the angel of the Lord spoke to Gad to say to David, that David should go up, to erect an altar unto the Lord on the threshing-floor of Ornan the Jebusite.
19 Saboda haka Dawuda ya haura cikin biyayya ga maganar da Allah ya yi da sunan Ubangiji.
And David went up by the word of Gad, which he had spoken in the name of the Lord.
20 Yayinda Ornan yake sussukar alkama, sai ya juya ya ga mala’ika;’ya’yansa maza guda huɗu da suke tare da shi suka ɓuya.
And when Ornan turned back, and saw the angel, then did he and his four sons with him hide themselves. Now Ornan was threshing wheat.
21 Sai Dawuda ya kusato, sa’ad da Ornan ya duba sai ya gan shi, ya bar masussukar ya rusuna a gaban Dawuda da fuskarsa har ƙasa.
And as David came up to Ornan, Ornan looked up and saw David; and he went out of the threshing-floor, and bowed himself to David with his face to the ground.
22 Dawuda ya ce wa Ornan, “Ka ba ni masussukarka saboda in gina bagade wa Ubangiji, don annobar da take kan mutane tă daina. Ka sayar mini ita a cikakken kuɗinta.”
Then said David to Ornan, “Grant me the site of this threshing-floor, that I may build thereon an altar unto the Lord: for the full price shalt thou give it unto me, so that the plague may be stayed from the people.”
23 Ornan ya ce wa Dawuda, “Ka karɓa! Bari ranka yă daɗe, sarki yă yi duk abin da ya ga ya yi masa kyau. Duba, zan ba da shanu domin hadaya ta ƙonawa, da itacen sussuka, da kuma alkama domin hadaya ta gari. Zan ba da dukan wannan.”
And Ornan said unto David, Take it for thyself, and let my lord the king do what is good in his eyes: lo, I give the oxen for burnt-offerings, and the threshing-rollers for wood, and the wheat for the meat-offering; the whole do I give [thee].
24 Amma Sarki Dawuda ya amsa wa Ornan ya ce, “A’a, na nace zan biya cikakken kuɗinta. Ba zan karɓi abinka kawai don Ubangiji ba, ko in miƙa hadaya ta ƙonawar da ba tă ci mini wani abu ba.”
And king David said to Ornan, No: but I will surely buy it at the full value; for I will not take what is thine for the Lord, so as to offer burnt-offerings without paying therefore.
25 Saboda haka Dawuda ya biya Ornan shekel ɗari shida na zinariya saboda wurin.
So David gave to Ornan for the place six hundred shekels of gold by weight.
26 Dawuda ya gina bagade wa Ubangiji a can ya kuma miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama, Ubangiji kuwa ya amsa masa ta wurin wuta daga sama a kan bagaden hadaya ta ƙonawa.
And David built there an altar unto the Lord, and offered burnt-offerings and peace-offerings, and he called on the Lord: and he answered him from heaven by fire upon the altar of burnt-offering.
27 Sa’an nan Ubangiji ya yi magana ga mala’ikan, ya kuma mayar da takobinsa a kube.
And the Lord spoke to the angel, and he put back his sword into its sheath.
28 A lokacin, sa’ad da Dawuda ya ga cewa Ubangiji ya amsa masa a masussukar Ornan mutumin Yebus, sai ya miƙa hadayu a can.
At that time when David saw that the Lord had answered him on the threshing-floor of Ornan the Jebusite, then did he sacrifice there.
29 Tabanakul na Ubangiji da Musa ya yi a hamada, da kuma bagaden hadaya ta ƙonawa a lokacin suna a tudun Gibeyon.
But the tabernacle of the Lord, which Moses had made in the wilderness, and the altar of the burnt-offering, were at that time in the high-place at Gib'on.
30 Amma Dawuda bai iya zuwa gabansa don yă yi tambaya ga Allah ba, gama yana jin tsoron takobin mala’ikan Ubangiji.
But David was not able to go before it to inquire of God; for he was afraid because of the sword of the angel of the Lord.

< 1 Tarihi 21 >