< 1 Tarihi 21 >

1 Sai Shaiɗan ya tashi gāba da Isra’ila, ya zuga Dawuda ya ƙidaya Isra’ila.
Satan loh Israel a thoh thil tih Israel tae hamla David a vueh.
2 Saboda haka Dawuda ya ce wa Yowab da shugabannin mayaƙa, “Ku tafi ku ƙidaya Isra’ilawa daga Beyersheba zuwa Dan. Ku kawo mini labarin saboda in san su nawa ne.”
Te dongah David loh Joab taeng neh pilnam mangpa rhoek taengah, “Cet uh lamtah Israel he Beersheba lamloh Dan duela tae uh. Te phoeiah kai taengla ha puen uh lamtah a hlangmi te ka ming van eh,” a ti nah.
3 Amma Yowab ya amsa ya ce, “Ubangiji ya riɓaɓɓanya mayaƙansa fiye da sau ɗari. Ranka yă daɗe sarki, dukansu ba bayin shugabana ba ne? Me ya sa ranka yă daɗe yake so yă yi haka? Me zai sa ka kawo laifi a kan Isra’ila?”
Tedae Joab loh, “BOEIPA loh a pilnam te a pueh yakhat la a thap bitko. Ka boei manghai aw, amih boeih te ka boei taengah sal la a om uh moenih a? Ka boeipa loh balae tih he he a hue. Balae tih Israel soah dumlai la a om eh?” a ti.
4 Amma sarki ya nace a kan maganar da ya yi wa Yowab. Sai Yowab ya tashi ya tafi cikin dukan Isra’ila, ya kewaye sa’an nan ya dawo Urushalima.
Tedae manghai kah ol loh Joab te a khum a la. Te dongah Joab te nong tih Israel tom te a pha phoeiah Jerusalem la pawk.
5 Yowab ya ba labarin yawan mayaƙan wa Dawuda. A cikin Isra’ila akwai mutum miliyon da dubu ɗari ɗaya waɗanda za su iya riƙe takobi, haɗe da dubu ɗari huɗu da saba’in a Yahuda.
Te phoeiah Joab loh pilnam hlangboel hlangmi te David taengla a paek. Te vaengah Israel boeih te cunghang aka pom thai hlang thawng thawng khat neh thawng yakhat om. Judah kah cunghang aka pom hlang he thawng ya li neh thawng sawmrhih lo.
6 Amma Yowab bai haɗa da mutanen Lawi da na Benyamin a ƙidayar ba, domin bai ji daɗin umarnin sarki ba.
Tedae manghai ol loh Joab te a tuei dongah Levi neh Benjamin tah amih lakli ah nuen sak pawh.
7 Wannan umarnin mugu ne a gaban Allah; saboda haka ya hukunta Isra’ila.
He ol he Pathen mik ah a lolh dongah Israel te a ngawn.
8 Sai Dawuda ya ce wa Allah, “Na yi zunubi ƙwarai ta wurin yin wannan. Yanzu, na roƙe ka, ka ɗauke laifin bawanka. Na yi wauta sosai.”
David loh Pathen taengah, “He kah hno ka saii he bahoeng ka tholh coeng. Na sal kathaesainah he khuen mai laeh, ka pavai tangkik dongah ni,” a ti nah.
9 Sai Ubangiji ya ce wa Gad, mai duba na Dawuda,
Te vaengah BOEIPA loh David kah khohmu Gad te a voek tih,
10 “Tafi ka faɗa wa Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce ina ba ka abubuwa uku. Ka zaɓi ɗaya daga cikinsu don in aikata a kanka.’”
Cet lamtah David te thui pah. BOEIPA loh he ni a thui. Kai loh nang te pathum kan doe tih te khuikah pakhat te namah ham tuek lamtah nang taengah kan saii eh?,’ ti nah,” a ti nah.
11 Saboda haka Gad ya tafi wurin Dawuda ya ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka yi zaɓi,
Te phoeiah Gad te David taengla pawk tih amah te, “BOEIPA loh a thui he namah ham doe laeh.
12 shekara uku na yunwa, wata uku na shan ɗibga a gaban abokan gābanka, sa’ad da za su bi suna kakkashe ku, ko kuwa kwana uku na takobin Ubangiji, ranakun annoba a cikin ƙasar, mala’ikan Ubangiji zai hallaka kowane sashe na Isra’ila.’ Yanzu sai ka yanke shawara yadda zan amsa wa wanda ya aiko ni.”
Khokha kum thum nim, na rhal mikhmuh lamloh hla thum na khoengvoep uh tih na thunkha kah cunghang loh n'kae te nim? Hnin thum khuiah BOEIPA kah cunghang neh diklai ah duektahaw la BOEIPA puencawn loh Israel kah khorhi tom ah a phae te nim? Mebang khaw hmu lamtah kai taengla ol ham mael laeh,” a ti nah.
13 Dawuda ya ce wa Gad, “Na shiga uku. Bari in fāɗa a hannuwan Ubangiji, gama jinƙansa yana da girma sosai; amma kada ka bari in fāɗa a hannuwan mutane.”
David loh Gad taengah kai he puen ka cak tangkik coeng. A haidamnah he a len tangkik dongah BOEIPA kut ah ka tla mai eh. Tedae hlang kut ah tah ka tla boel eh?,” a ti nah.
14 Sai Ubangiji ya aiko da annoba a kan Isra’ila, mutane duba saba’in na Isra’ila suka mutu.
Te dongah BOEIPA loh Israel soah duektahaw a paek tih Israel hlang thawng sawmrhih cungku.
15 Allah kuwa ya aiki mala’ika yă hallaka Urushalima. Amma yayinda mala’ikan yana gab da yin haka, sai Ubangiji ya gani ya kuma yi nadama saboda masifar, sai ya ce wa mala’ikan wanda yake hallaka mutane, “Ya isa! Janye hannunka.” Mala’ikan Ubangiji kuwa yana tsaye a masussukar Ornan mutumin Yebus.
Te phoeiah Pathen loh Jerusalem phae hamla puencawn a tueih. Tedae a phae te BOEIPA loh a hmuh tanglang vaengah tah boethae khaw damti. Te dongah khopuei aka phae puencawn te, “Temah laeh saeh, na kut yuek laeh,” a ti nah. Te vaengah BOEIPA kah puencawn te Jebusi Ornan kah cangtilhmuen ah pai.
16 Sai Dawuda ya ɗaga ido ya ga mala’ikan Ubangiji tsaye tsakanin sama da duniya, da takobi a zāre a hannunsa ya miƙa a kan Urushalima. Sai Dawuda da dattawa, saye da rigunan makoki suka fāɗi rubda jiki.
David loh a mik a huel vaengah diklai laklo neh vaan laklo ah aka pai BOEIPA puencawn te a hmuh. Te long te a kut dongah a cunghang a muk tih Jerusalem te a nuen. Te dongah David neh a ham rhoek tah a maelhmai ah tlamhni neh a khuk uh tih bakop uh.
17 Dawuda ya ce wa Allah, “Ba ni ba ne na umarta a ƙidaya mayaƙan? Ni ne wanda ya yi zunubin da kuma abin da ba daidai ba. Waɗannan dai tumaki ne. Me suka yi? Ya Ubangiji Allahna, bari hannunka ya fāɗi a kaina da kuma iyalina, amma kada ka bar wannan annoba ya kasance a kan mutanenka.”
David loh Pathen taengah, “Pilnam tae ham aka thui te kai moenih a? Anih te kai ka tholh sak dongah ka thae tah ka thae coeng. Tedae he boiva rhoek loh balae a saii uh? Ka Pathen BOEIPA aw, na kut te kamah so neh a pa kah imkhui soah tla mai saeh. Tedae na pilnam te lucik neh ben boel mai,” a ti nah.
18 Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya umarci Gad yă faɗa wa Dawuda yă haura yă gina bagade wa Ubangiji a masussukar Ornan mutumin Yebus.
Te daengah BOEIPA kah puencawn loh Gad te, “David te thui pah, David te BOEIPA kah hmueihtuk suem hamla Jebusi Ornan kah cangtilhmuen ah cet saeh,” a ti nah.
19 Saboda haka Dawuda ya haura cikin biyayya ga maganar da Allah ya yi da sunan Ubangiji.
Te dongah David khaw BOEIPA ming neh a thui Gad ol bangla cet.
20 Yayinda Ornan yake sussukar alkama, sai ya juya ya ga mala’ika;’ya’yansa maza guda huɗu da suke tare da shi suka ɓuya.
Ornan a mael vaengah puencawn te a hmuh. Te vaengah a taengkah a capa pali tah thuh uh dae Ornan tah cang a til.
21 Sai Dawuda ya kusato, sa’ad da Ornan ya duba sai ya gan shi, ya bar masussukar ya rusuna a gaban Dawuda da fuskarsa har ƙasa.
David te Ornan taengla pawk tih Ornan loh a paelki vaengah David te a hmuh. Te dongah cangtilhmuen lamloh thoeih tih David taengah a maelhmai te diklai la buluk.
22 Dawuda ya ce wa Ornan, “Ka ba ni masussukarka saboda in gina bagade wa Ubangiji, don annobar da take kan mutane tă daina. Ka sayar mini ita a cikakken kuɗinta.”
David loh Ornan te, “Cangtil hmuen he kai taengah m'pae mai lamtah a soah BOEIPA kah hmueihtuk ka suem mai eh. Te te tangka nen khaw kai he boeih m'pae mai. Te daengah ni lucik he pilnam dong lamloh a cing eh?,” a ti nah.
23 Ornan ya ce wa Dawuda, “Ka karɓa! Bari ranka yă daɗe, sarki yă yi duk abin da ya ga ya yi masa kyau. Duba, zan ba da shanu domin hadaya ta ƙonawa, da itacen sussuka, da kuma alkama domin hadaya ta gari. Zan ba da dukan wannan.”
Ornan loh David taengah, “Namah ham lo lamtah ka boei manghai a mikhmuh ah a then la saii saeh. So lah he, Hmueihhlutnah ham vaito neh thing hamla tloep kam paek bitni. Cang he khaw khocang la boeih kam paek bitni,” a ti nah.
24 Amma Sarki Dawuda ya amsa wa Ornan ya ce, “A’a, na nace zan biya cikakken kuɗinta. Ba zan karɓi abinka kawai don Ubangiji ba, ko in miƙa hadaya ta ƙonawar da ba tă ci mini wani abu ba.”
Tedae manghai David loh Ornan te, “Moenih, tangka la boeih a lai la kan lai eh. Nang taengkah te BOEIPA ham akhaw, hmueihhlutnah nawn ham akhaw a yoe la ka lo mahpawh,” a ti nah.
25 Saboda haka Dawuda ya biya Ornan shekel ɗari shida na zinariya saboda wurin.
Te dongah David loh Ornan te a hmuen phu la sui shekel a khiing ya rhuk a paek.
26 Dawuda ya gina bagade wa Ubangiji a can ya kuma miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama, Ubangiji kuwa ya amsa masa ta wurin wuta daga sama a kan bagaden hadaya ta ƙonawa.
Te phoeiah David loh BOEIPA ham hmueihtuk pahoi a suem tih hmueihhlutnah neh rhoepnah te a nawn. BOEIPA a khue vaengah anih te hmueihtuk sokah hmueihhlutnah dongah vaan lamkah hmai neh a voek.
27 Sa’an nan Ubangiji ya yi magana ga mala’ikan, ya kuma mayar da takobinsa a kube.
Te daengah BOEIPA loh puencawn te a voek tih a cunghang te tuengim khuila a sang.
28 A lokacin, sa’ad da Dawuda ya ga cewa Ubangiji ya amsa masa a masussukar Ornan mutumin Yebus, sai ya miƙa hadayu a can.
Te vaeng tue kah Jebusi Ornan cangtilhmuen ah BOEIPA loh anih a doo te David loh a hmuh van neh pahoi a nawn.
29 Tabanakul na Ubangiji da Musa ya yi a hamada, da kuma bagaden hadaya ta ƙonawa a lokacin suna a tudun Gibeyon.
Moses loh khosoek kah a saii BOEIPA kah dungtlungim neh te vaeng tue kah hmueihhlutnah hmueihtuk tah Gibeon hmuensang ah om pueng.
30 Amma Dawuda bai iya zuwa gabansa don yă yi tambaya ga Allah ba, gama yana jin tsoron takobin mala’ikan Ubangiji.
Tedae BOEIPA puencawn kah cunghang ha loh a let sak coeng dongah David loh a mikhmuh la a caeh ham khaw, Pathen a toem ham coeng thai pawh.

< 1 Tarihi 21 >