< 1 Tarihi 20 >

1 Da bazara, a lokacin da sarakuna kan tafi yaƙi, Yowab ya jagorance mayaƙa. Ya lalatar da ƙasar Ammonawa ya kuma tafi Rabba ya yi mata kwanto, amma Dawuda ya zauna a Urushalima. Yowab ya yaƙi Rabba, ya kuma bar ta kango.
Kwathi entwasa, ngesikhathi sokuphuma kwezimpi zamakhosi ukuyakulwa, uJowabi wakhokhela amabutho ayehlomile. Watshaya wabhuqa ilizwe lama-Amoni waze wayavimbezela ilizwe laseRabha, kodwa uDavida wasala eJerusalema. UJowabi wahlasela iRabha wayitshiya ingamanxiwa.
2 Dawuda ya ɗauki rawani daga kan sarkinsu, nauyinsa ya kai talenti na zinariya, aka kuma yi masa ado da duwatsu masu daraja, sai Dawuda kuwa ya sa a kansa. Ya kuma kwashi ganima mai yawa daga birnin
UDavida wathatha umqhele owawusekhanda lenkosi yabo isisindo sawo sasilithalenta legolide, uceciswe ngamatshe aligugu, umqhele wasufakwa ekhanda likaDavida. Wathatha impango enengi kakhulu kulelodolobho,
3 ya kuma fitar da mutanen da suke can, ya sa su aiki da zartuna da makamai masu kaifi da kuma gatura. Dawuda ya yi haka da dukan garuruwan Ammonawa. Sa’an nan Dawuda da mayaƙansa gaba ɗaya suka koma Urushalima.
njalo abantu ababelapho wabasusa wabasa lapho ababezasebenza khona gadalala ngamasaha, ngamapiki ensimbi kanye lamahloka. Lokhu uDavida wakwenza kuwo wonke amadolobho ama-Amoni. Kwathi uDavida ngokwakhe kanye lamabutho akhe wonke babuyela eJerusalema.
4 Ana nan, sai yaƙi ya ɓarke a Gezer tsakanin Isra’ila da Filistiyawa. Sai Sibbekai mutumin Husha ya kashe Siffai, ɗaya daga cikin zuriyar Refahiyawa, ta haka kuma aka ci Filistiyawa da yaƙi.
Ngokuqhubeka kwesikhathi, kwaqhamuka impi yamaFilistiya, eGezeri. Ngalesosikhathi uSibhekhayi umHushathi wabulala uSiphayi, omunye wabosendo lwamaRefayi kwaba yikwehlulwa kwamaFilistiya.
5 Yaƙi kuma ya sāke tashi tsakanin Isra’ilawa da Filistiyawa, Elhanan ɗan Yayir ya kashe Lahmi ɗan’uwan Goliyat mutumin Gat, wanda yake riƙe da māshi mai sandan masaƙa.
Kweyinye impi lamaFilistiya, u-Elihanani indodana kaJayiri wabulala uLahimi umfowabo kaGoliyathi umGithi, owayelomkhonto ololuthi olunjengolomeluki.
6 Aka sāke yin wani yaƙin kuma, wanda ya faru a Gat, akwai wani ƙaton mutum mai yatsotsi shida a kowane hannu da kuma yatsotsi shida a kowace ƙafa, yatsotsi ashirin da huɗu ke nan. Shi ma daga zuriyar Rafa ce.
Kanti njalo kwenye impi, eyalwelwa eGathi, kwakulendoda enkulu kakhulu ileminwe eyisithupha esandleni ngasinye, lamazwane ayisithupha enyaweni ngalunye, sekubalwa konke ndawonye kungamatshumi amabili lane. Laye wayengowosendo lukaRafa.
7 Sa’ad da ya yi wa Isra’ila ba’a, sai Yonatan ɗan Shimeya, ɗan’uwan Dawuda ya kashe shi.
Ngokuchothoza kwakhe abako-Israyeli, uJonathani indodana kaShimeya, umfowabo kaDavida, wambulala.
8 Waɗannan su ne zuriyar Rafa a Gat, Dawuda da mutanensa sun kashe su.
Laba ngabosendo lukaRafa eGathi, njalo bafela ezandleni zikaDavida lamabutho akhe.

< 1 Tarihi 20 >