< 1 Tarihi 20 >

1 Da bazara, a lokacin da sarakuna kan tafi yaƙi, Yowab ya jagorance mayaƙa. Ya lalatar da ƙasar Ammonawa ya kuma tafi Rabba ya yi mata kwanto, amma Dawuda ya zauna a Urushalima. Yowab ya yaƙi Rabba, ya kuma bar ta kango.
Or il arriva l'armée suivante, au temps que les Rois font leur sortie, que Joab conduisit le gros de l'armée, et ravagea le pays des enfants de Hammon; puis il alla assiéger Rabba, tandis que David demeurait à Jérusalem; et Joab battit Rabba, et la détruisit.
2 Dawuda ya ɗauki rawani daga kan sarkinsu, nauyinsa ya kai talenti na zinariya, aka kuma yi masa ado da duwatsu masu daraja, sai Dawuda kuwa ya sa a kansa. Ya kuma kwashi ganima mai yawa daga birnin
Et David prit la couronne de dessus la tête de leur Roi, et il trouva qu'elle pesait un talent d'or, et il y avait des pierres précieuses; et on la mit sur la tête de David, qui emmena un fort grand butin de la ville.
3 ya kuma fitar da mutanen da suke can, ya sa su aiki da zartuna da makamai masu kaifi da kuma gatura. Dawuda ya yi haka da dukan garuruwan Ammonawa. Sa’an nan Dawuda da mayaƙansa gaba ɗaya suka koma Urushalima.
Il emmena aussi le peuple qui y était, et les scia avec des scies, et avec des herses de fer et de scies. David traita de la sorte toutes les villes des enfants de Hammon; puis il s'en retourna avec tout le peuple à Jérusalem.
4 Ana nan, sai yaƙi ya ɓarke a Gezer tsakanin Isra’ila da Filistiyawa. Sai Sibbekai mutumin Husha ya kashe Siffai, ɗaya daga cikin zuriyar Refahiyawa, ta haka kuma aka ci Filistiyawa da yaƙi.
Il arriva après cela que la guerre continua à Guézer contre les Philistins; [et] alors Sibbecaï le Husathite frappa Sippaï, qui était des enfants de Rapha, et ils furent abaissés.
5 Yaƙi kuma ya sāke tashi tsakanin Isra’ilawa da Filistiyawa, Elhanan ɗan Yayir ya kashe Lahmi ɗan’uwan Goliyat mutumin Gat, wanda yake riƙe da māshi mai sandan masaƙa.
Il y eut encore une autre guerre contre les Philistins, dans laquelle Elhanan fils de Jahir frappa Lahmi, frère de Goliath Guittien, qui avait une hallebarde dont la hampe était comme l'ensuble d'un tisserand.
6 Aka sāke yin wani yaƙin kuma, wanda ya faru a Gat, akwai wani ƙaton mutum mai yatsotsi shida a kowane hannu da kuma yatsotsi shida a kowace ƙafa, yatsotsi ashirin da huɗu ke nan. Shi ma daga zuriyar Rafa ce.
Il y eut encore une autre guerre à Gath, où se trouva un homme de grande stature, qui avait six doigts à chaque main, et [six orteils] à chaque pied, de sorte qu'il en avait en tout vingt-quatre; et il était aussi de la race de Rapha.
7 Sa’ad da ya yi wa Isra’ila ba’a, sai Yonatan ɗan Shimeya, ɗan’uwan Dawuda ya kashe shi.
Et il défia Israël; mais Jonathan, fils de Simha frère de David, le tua.
8 Waɗannan su ne zuriyar Rafa a Gat, Dawuda da mutanensa sun kashe su.
Ceux-là naquirent à Gath; ils étaient de la race de Rapha, et ils moururent par les mains de David, et par les mains de ses serviteurs.

< 1 Tarihi 20 >