< 1 Tarihi 20 >

1 Da bazara, a lokacin da sarakuna kan tafi yaƙi, Yowab ya jagorance mayaƙa. Ya lalatar da ƙasar Ammonawa ya kuma tafi Rabba ya yi mata kwanto, amma Dawuda ya zauna a Urushalima. Yowab ya yaƙi Rabba, ya kuma bar ta kango.
Au renouvellement de l’année, époque où les rois entrent en campagne, Joab se mit à la tête de l’armée et porta le ravage dans le pays des Ammonites. Il mit le siège devant Rabba tandis que David restait à Jérusalem, se rendit maître de la ville et la détruisit.
2 Dawuda ya ɗauki rawani daga kan sarkinsu, nauyinsa ya kai talenti na zinariya, aka kuma yi masa ado da duwatsu masu daraja, sai Dawuda kuwa ya sa a kansa. Ya kuma kwashi ganima mai yawa daga birnin
David enleva de la tête du roi des Ammonites sa couronne, pesant un kikkar d’or et ornée de pierres précieuses, et qui passa sur la tête de David. Il emporta le butin de la ville en très grande quantité.
3 ya kuma fitar da mutanen da suke can, ya sa su aiki da zartuna da makamai masu kaifi da kuma gatura. Dawuda ya yi haka da dukan garuruwan Ammonawa. Sa’an nan Dawuda da mayaƙansa gaba ɗaya suka koma Urushalima.
Il emmena le peuple qui s’y trouvait, le condamna à la scie, aux herses de fer et aux haches; et il en usa de même à l’égard de toutes les villes des Ammonites. Puis David, avec toute l’armée, rentra à Jérusalem.
4 Ana nan, sai yaƙi ya ɓarke a Gezer tsakanin Isra’ila da Filistiyawa. Sai Sibbekai mutumin Husha ya kashe Siffai, ɗaya daga cikin zuriyar Refahiyawa, ta haka kuma aka ci Filistiyawa da yaƙi.
Plus tard survint, à Ghézer, une guerre avec les Philistins; c’est alors que Sibbekkaï, de Houcha, battit Sippaï, un des descendants de Rapha, dont le pouvoir fut abattu.
5 Yaƙi kuma ya sāke tashi tsakanin Isra’ilawa da Filistiyawa, Elhanan ɗan Yayir ya kashe Lahmi ɗan’uwan Goliyat mutumin Gat, wanda yake riƙe da māshi mai sandan masaƙa.
Une autre guerre eut lieu avec les Philistins, dans laquelle Elhanan, fils de Yaïr, abattit Lahmi, frère de Goliath de Gath (le bois de sa lance ressemblait à l’ensouple du tisserand).
6 Aka sāke yin wani yaƙin kuma, wanda ya faru a Gat, akwai wani ƙaton mutum mai yatsotsi shida a kowane hannu da kuma yatsotsi shida a kowace ƙafa, yatsotsi ashirin da huɗu ke nan. Shi ma daga zuriyar Rafa ce.
Une autre guerre eut lieu à Gath, où figura un homme de haute taille, qui avait six doigts à chaque main, six à chaque pied, en tout vingt-quatre, et qui, lui aussi, était issu de Rapha.
7 Sa’ad da ya yi wa Isra’ila ba’a, sai Yonatan ɗan Shimeya, ɗan’uwan Dawuda ya kashe shi.
Il défia Israël et fut tué par Jonathan, fils de Chimea et neveu de David.
8 Waɗannan su ne zuriyar Rafa a Gat, Dawuda da mutanensa sun kashe su.
Tous ceux-ci étaient nés au Rapha dans Gath; tous périrent par la main de David et par celle de ses serviteurs.

< 1 Tarihi 20 >