< 1 Tarihi 20 >
1 Da bazara, a lokacin da sarakuna kan tafi yaƙi, Yowab ya jagorance mayaƙa. Ya lalatar da ƙasar Ammonawa ya kuma tafi Rabba ya yi mata kwanto, amma Dawuda ya zauna a Urushalima. Yowab ya yaƙi Rabba, ya kuma bar ta kango.
Forsothe it was doon after the ende of a yeer, in that tyme wherinne kyngis ben wont to go forth to batels, Joab gederide the oost, and the strengthe of chyualrie, and he wastide the lond of the sones of Amon, and yede, and bisegide Rabath; forsothe Dauid dwellide in Jerusalem, whanne Joab smoot Rabath, and distriede it.
2 Dawuda ya ɗauki rawani daga kan sarkinsu, nauyinsa ya kai talenti na zinariya, aka kuma yi masa ado da duwatsu masu daraja, sai Dawuda kuwa ya sa a kansa. Ya kuma kwashi ganima mai yawa daga birnin
Forsothe Dauid took the coroun of Melchon fro his heed, and foond therynne the weiyt of gold a talent, and moost precious iemmes, and he made therof a diademe to hym silf; also he took ful many spuylis of the citee.
3 ya kuma fitar da mutanen da suke can, ya sa su aiki da zartuna da makamai masu kaifi da kuma gatura. Dawuda ya yi haka da dukan garuruwan Ammonawa. Sa’an nan Dawuda da mayaƙansa gaba ɗaya suka koma Urushalima.
Sotheli he ledde out the puple that was therynne, and made breris, `ethir instrumentis bi whiche cornes ben brokun, and sleddis, and irone charis, to passe on hem, so that alle men weren kit in to dyuerse partis, and weren al to-brokun; Dauid dide thus to alle the `cytees of the sones of Amon, and turnede ayen with al his puple in to Jerusalem.
4 Ana nan, sai yaƙi ya ɓarke a Gezer tsakanin Isra’ila da Filistiyawa. Sai Sibbekai mutumin Husha ya kashe Siffai, ɗaya daga cikin zuriyar Refahiyawa, ta haka kuma aka ci Filistiyawa da yaƙi.
Aftir these thingis a batel was maad in Gazer ayens Filisteis, wherynne Sobochai Vsachites slow Saphai of the kyn of Raphym, and mekide hem.
5 Yaƙi kuma ya sāke tashi tsakanin Isra’ilawa da Filistiyawa, Elhanan ɗan Yayir ya kashe Lahmi ɗan’uwan Goliyat mutumin Gat, wanda yake riƙe da māshi mai sandan masaƙa.
Also another batel was don ayens Filisteis, in which a man youun of God, the sone of forest, a man of Bethleem, killide Goliath of Geth, the brother of giauntis, of whos schaft the tre was as the beem of webbis.
6 Aka sāke yin wani yaƙin kuma, wanda ya faru a Gat, akwai wani ƙaton mutum mai yatsotsi shida a kowane hannu da kuma yatsotsi shida a kowace ƙafa, yatsotsi ashirin da huɗu ke nan. Shi ma daga zuriyar Rafa ce.
But also another batel bifelde in Geth, in which a ful long man was, hauynge sixe fyngris, that is, togidere foure and twenti, and he was gendrid of the generacioun of Raphaym;
7 Sa’ad da ya yi wa Isra’ila ba’a, sai Yonatan ɗan Shimeya, ɗan’uwan Dawuda ya kashe shi.
he blasfemyde Israel, and Jonathan, the sone of Samaa, brother of Dauid, killide hym.
8 Waɗannan su ne zuriyar Rafa a Gat, Dawuda da mutanensa sun kashe su.
These ben the sones of Raphaym in Geth, that felden doun in the hond of Dauid and of hise seruauntis.