< 1 Tarihi 2 >

1 Waɗannan su ne’ya’yan Isra’ila maza. Ruben, Simeyon, Lawi, Yahuda, Issakar, Zebulun,
Éstos son los hijos de Israel: Rubén, Simeón, Leví, Judá, Isacar, Zabulón,
2 Dan, Yusuf, Benyamin, Naftali, Gad da Asher.
Dan, José, Benjamín, Neftalí, Gad y Aser.
3 ’Ya’yan Yahuda maza su ne, Er, Onan da Shela. Waɗannan mutum uku Bat-shuwa mutuniyar Kan’ana ce ta haifa masa. Er, ɗan farin Yahuda mugu ne a gaban Ubangiji, saboda haka Ubangiji ya kashe shi.
Hijos de Judá: Er, Onán y Sela. Estos tres le nacieron de la hija de Súa, cananea. Pero Er, primogénito de Judá, fue perverso ante Yavé, Quien lo mató.
4 Tamar, surukar Yahuda, ta haifa masa Ferez da Zera. Yahuda ya haifi’ya’ya maza biyar ne.
Tamar su nuera le dio a luz a Fares y a Zera. Todos los hijos de Judá fueron cinco.
5 ’Ya’yan Ferez maza su ne, Hezron da Hamul.
Hijos de Fares: Hezrón y Hamul.
6 ’Ya’yan Zera maza su ne, Zimri, Etan, Heman, Kalkol da Darda, su biyar ne.
Hijos de Zera: Zimri, Etán, Hemán, Calcol y Dara. Todos los hijos de Judá fueron cinco.
7 ’Ya’yan Karmi maza su ne, Akar wanda ya kawo masifa wa Isra’ila ta wurin yin abin da aka haramta.
Hijo de Carmi fue Acán, perturbador de Israel, porque transgredió en cuanto a lo maldito.
8 Ɗan Etan shi ne, Azariya.
Hijo de Etán: Azarías.
9 ’Ya’ya maza da aka haifa wa Hezron su ne, Yerameyel, Ram da Kaleb.
Los hijos que le nacieron a Hezrón: Jerameel, Ram y Quelubai.
10 Ram shi ne mahaifin Amminadab, Amminadab kuwa shi ne mahaifin Nashon, shugaban mutanen Yahuda.
Ram engendró a Aminadab, y Aminadab engendró a Naasón, jefe de los hijos de Judá.
11 Nashon shi ne mahaifin Salma, Salma shi ne mahaifin Bowaz,
Naasón engendró a Salmón, y Salmón engendró a Booz.
12 Bowaz shi ne mahaifin Obed kuma Obed shi ne mahaifin Yesse.
Booz engendró a Obed, y Obed engendró a Isaí.
13 Yesse shi ne mahaifin. Eliyab ɗan farinsa, ɗansa na biyu shi ne Abinadab, na ukun Shimeya,
Isaí engendró a Eliab su primogénito, el segundo Abinadab, el tercero Simea,
14 na huɗun Netanel, na biyar Raddai,
el cuarto Natanael, el quinto Radai,
15 na shidan Ozem na bakwai kuma Dawuda.
el sexto Ozem, el séptimo David,
16 ’Yan’uwansu mata su ne Zeruhiya da Abigiyel.’Ya’yan Zeruhiya maza guda uku su ne Abishai, Yowab da Asahel.
de los cuales Sarvia y Abigail fueron hermanas. Los hijos de Sarvia fueron tres: Abisai, Joab y Asael.
17 Abigiyel ita ce mahaifiyar Amasa, wanda mahaifinsa shi ne Yeter mutumin Ishmayel.
Abigail dio a luz a Amasa, cuyo padre fue Jeter ismaelita.
18 Kaleb ɗan Hezron ya haifi yara ta wurin matarsa Azuba (da kuma ta wurin Yeriyot). Waɗannan su ne’ya’yan Azuba maza. Yesher, Shobab da Ardon.
Caleb, hijo de Hezrón, engendró a Jeriot de su esposa Azuba. Los hijos de ella fueron Jeser, Sobab y Ardón.
19 Da Azuba ta mutu, Kaleb ya auri Efrat, wadda ta haifa masa Hur.
Al morir Azuba, Caleb tomó como esposa a Efrata, la cual dio a luz a Hur.
20 Hur shi ne mahaifin Uri, Uri kuma shi ne mahaifin Bezalel.
Hur engendró a Uri, y Uri a Bezaleel.
21 Daga baya, Hezron ya kwana da’yar Makir mahaifin Gileyad (ya aure ta sa’ad da take da shekara sittin), ta haifa masa Segub.
Después Hezrón se unió a la hija de Maquir, padre de Galaad, a la cual tomó cuando él tenía 60 años, y ella dio a luz a Segub.
22 Segub shi ne mahaifin Yayir, wanda ya yi mulkin garuruwa uku a Gileyad.
Segub engendró a Jaír, quien poseyó 23 ciudades en la tierra de Galaad.
23 (Amma Geshur da Aram suka ƙwace Hawwot Yayir da kuma Kenat tare da ƙauyukan kewayenta, garuruwa sittin.) Dukan waɗannan su ne zuriyar Makir mahaifin Gileyad.
Pero Gesur y Aram tomaron las aldeas de Jaír, y Kenat y sus aldeas: 60 pueblos. Todas éstas las tomaron los hijos de Maquir, padre de Galaad.
24 Bayan Hezron ya mutu a Kaleb Efrata, sai Abiya matar Hezron ta haifa masa Asshur mahaifin Tekowa.
Después que Hezrón murió en Caleb-efrata, Abías, esposa de Hezrón, dio a luz a Asur, padre de Tecoa.
25 ’Ya’yan Yerameyel maza, ɗan farin Hezron su ne, Ram shi ne ɗan fari, sai Buna, Oren, Ozem da Ahiya.
Los hijos de Jerameel, primogénito de Hezrón, fueron: Ram, su primogénito, Buna, Orén, Ozem y Ahías.
26 Yerameyel yana da wata mata, wadda sunanta Atara; ita ce mahaifiyar Onam.
Jerameel tuvo otra mujer llamada Atara, que fue madre de Onam.
27 ’Ya’yan Ram maza ɗan farin Yerameyel su ne, Ma’az, Yamin da Eker.
Hijos de Ram, primogénito de Jerameel: Maaz, Jamín y Equer.
28 ’Ya’yan Onam maza su ne, Shammai da Yada.’Ya’yan Shammai maza su ne, Nadab da Abishur.
Hijos de Onam: Samai y Jada. Hijos de Samai: Nadab y Abisur.
29 Sunan matar Abishur ita ce Abihayil, wadda ta haifa masa Aban da Molid.
El nombre de la esposa de Abisur fue Abihail, la cual dio a luz a Ahbán y a Molid.
30 ’Ya’yan Nadab maza su ne, Seled da Affayim. Seled ya mutu babu yara.
Hijos de Nadab: Seled y Apaim. Seled murió sin hijos.
31 Ɗan Affayim shi ne, Ishi, wanda shi ne mahaifin Sheshan. Sheshan shi ne mahaifin Alai.
Isi fue hijo de Apaim, y Sesán, hijo de Isi, e hijo de Sesán, Ahlai.
32 ’Ya’yan Yada maza, ɗan’uwan Shammai su ne, Yeter da Yonatan. Yeter ya mutu babu yara.
Hijos de Jada, hermano de Samai: Jeter y Jonatán. Jeter murió sin hijos.
33 ’Ya’yan Yonatan maza su ne, Felet da Zaza. Waɗannan su ne zuriyar Yerameyel.
Hijos de Jonatán: Pelet y Zaza. Tales fueron los descendientes de Jerameel.
34 Sheshan ba shi da’ya’ya maza, sai’ya’ya mata kawai. Yana da bawa mutumin Masar mai suna Yarha.
Sesán no tuvo hijos, sino hijas. Pero Sesán tenía un esclavo egipcio llamado Jarha.
35 Sheshan ya ba da’yarsa aure ga bawansa Yarha, ta kuwa haifa masa Attai.
A éste, Sesán dio su hija como esposa, y ella dio a luz a Atai.
36 Attai shi ne mahaifin Natan, Natan shi ne mahaifin Zabad,
Atai engendró a Natán, Natán a Zabad,
37 Zabad shi ne mahaifin Eflal, Eflal shi ne mahaifin Obed,
Zabad a Eflal, Eflal a Obed,
38 Obed shi ne mahaifin Yehu, Yehu shi ne mahaifin Azariya,
Obed a Jehú, Jehú a Azarías,
39 Azariya shi ne mahaifin Helez, Helez shi ne mahaifin Eleyasa,
Azarías a Heles, Heles a Elasa,
40 Eleyasa shi ne mahaifin Sismai, Sismai shi ne mahaifin Shallum
Elasa a Sismai, Sismai a Salum,
41 Shallum shi ne mahaifin Yekamiya, Yekamiya kuma shi ne mahaifin Elishama.
Salum a Jecamías, y Jecamías a Elisama.
42 ’Ya’yan Kaleb maza, ɗan’uwan Yerameyel su ne, Mesha ɗan farinsa, wanda shi ne mahaifin Zif, da ɗansa Maresha, wanda shi ne mahaifin Hebron.
Hijos de Caleb, hermano de Jerameel: Mesa su primogénito, que fue el padre de Zif, y los hijos de Maresa, padre de Hebrón.
43 ’Ya’yan Hebron maza su ne, Kora, Taffuwa, Rekem da Shema.
Hijos de Hebrón: Coré, Tapúa, Requem y Sema.
44 Shema shi ne mahaifin Raham, Raham kuma shi ne mahaifin Yorkeyam. Rekem shi ne mahaifin Shammai.
Sema engendró a Raham, padre de Jorcoam, y Requem engendró a Samai.
45 Ɗan Shammai shi ne Mawon, Mawon kuma shi ne mahaifin Bet-Zur.
Maón fue hijo de Samai, y Maón padre de Bet-sur.
46 Efa ƙwarƙwarar Kaleb ita ce mahaifiyar Haran, Moza da Gazez. Haran shi ne mahaifin Gazez.
Efa, concubina de Caleb, dio a luz a Harán, Mosa y Gazez. Harán engendró a Gazez.
47 ’Ya’yan Yadai maza su ne, Regem, Yotam, Geshan, Felet, Efa da Sha’af.
Hijos de Jahdai: Regem, Jotam, Gesam, Pelet, Efa y Saaf.
48 Ma’aka ƙwarƙwarar Kaleb ita ce mahaifiyar Sheber da Tirhana.
Maaca, concubina de Caleb, dio a luz a Seber y Tirhana.
49 Ta kuma haifi Sha’af mahaifin Madmanna da kuma Shewa, mahaifin Makbena da Gibeya.’Yar Kaleb ita ce Aksa.
También dio a luz a Saaf, padre de Madmana, y a Seva, padre de Macbena, y padre de Gibea; y Acsa fue hija de Caleb.
50 Waɗannan su ne zuriyar Kaleb.’Ya’yan Hur maza, ɗan farin Efrata su ne, Shobal mahaifin Kiriyat Yeyarim,
Éstos fueron los hijos de Caleb: hijos de Hur, primogénito de Efrata: Sobal, padre de Quiriat-jearim,
51 Salma mahaifin Betlehem, da kuma Haref mahaifin Bet-Gader.
Salma, padre de Belén, y Haref, padre de Bet-gader.
52 Zuriyar Shobal mahaifin Kiriyat Yeyarim su ne, Harowe, rabin Manahatiyawa,
Hijos de Sobal, padre de Quiriat-jearim: Haroe, la mitad de los manahetitas.
53 kuma gidan Kiriyat Yeyarim su ne, Itrayawa, Futiyawa, Shumatiyawa da Mishratiyawa. Daga waɗannan ne Zoratiyawa da Eshtawoliyawa suka fito.
Familias de Quiriat-jearim: los itritas, los futitas, los sumatitas y los misraítas, de los cuales salieron los zoratitas y los estaolitas.
54 Zuriyar Salma su ne, Betlehem, Netofawa, Atrot Bet Yowab, rabin Manahatiyawa, Zoriyawa,
Hijos de Salma: Belén, y los netofatitas, Atrot-beth-joab, y Hazi-hammanahti, zoraíta.
55 kuma gidan marubuta waɗanda suke zama a Yabez su ne, Tiratiyawa, Shimeyatiyawa da Sukatiyawa. Waɗannan su ne Keniyawa waɗanda suka zo daga Hammat, mahaifin gidan Rekab.
Las familias de los escribas que habitaban en Jabes: los tirateos, los simeateos y los sucateos, los cuales son los ceneos, que proceden de Hamat, padre de la casa de Recab.

< 1 Tarihi 2 >