< 1 Tarihi 19 >

1 Ana nan, sai Nahash sarkin Ammonawa ya mutu, sai ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Kwasekusithi emva kwalokho uNahashi inkosi yamaAmoni wafa, indodana yakhe yasisiba yinkosi esikhundleni sakhe.
2 Dawuda ya yi tunani, “Zan nuna jinƙai ga Hanun ɗan Nahash, domin mahaifinsa ya nuna alheri gare ni.” Saboda haka Dawuda ya aika da tawaga don yă yi wa Hanun ta’aziyya game da mahaifinsa. Sa’ad da mutanen Dawuda suka iso wurin Hanun a ƙasar Ammonawa don su ta’azantar da shi,
UDavida wasesithi: Ngizamenzela umusa uHanuni indodana kaNahashi, ngoba uyise wangenzela umusa. UDavida wasethuma izithunywa ukuyamduduza ngoyise. Izinceku zikaDavida zasezifika elizweni labantwana bakoAmoni kuHanuni ukumduduza.
3 sai manyan Ammonawa suka ce wa Hanun, “Kana tsammani Dawuda yana girmama mahaifinka ne da ya aika mutanen nan wurinka su ta’azantar da kai? Ba mutanensa sun zo ne su bincika su kuma leƙi ƙasar su tumɓuke ta ba?”
Kodwa iziphathamandla zabantwana bakoAmoni zathi kuHanuni: Kambe uDavida uyamhlonipha uyihlo emehlweni akho, ngoba ethume abaduduzi kuwe? Izinceku zakhe kazizanga kuwe yini ukuphenya lokuchitha lokuhlola ilizwe?
4 Saboda haka Hanun ya kama mutanen Dawuda, ya yi musu aski, ya yayyanka rigunansu a daidai ɗuwawunsu, sa’an nan ya sallame su.
Ngakho uHanuni wathatha izinceku zikaDavida wazigela waquma izembatho zazo kungxenye kuze kube sezibunu zazo, waziyekela zahamba.
5 Da wani ya zo ya faɗa wa Dawuda game da mutanen, sai ya aiki’yan aika su sadu da su, gama an ƙasƙantar da su ainun. Sarki ya ce, “Ku zauna a Yeriko har sai gemunku sun yi girma, sa’an nan ku dawo.”
Basebehamba bamtshela uDavida ngalawomadoda; wasethuma ukuwahlangabeza, ngoba amadoda ayelenhloni kakhulu; inkosi yasisithi: Hlalani eJeriko zize zihlume izindevu zenu, beselibuya.
6 Sa’ad da Ammonawa suka gane cewa sun zama abin wurin a kafan hancin Dawuda, Hanun da Ammonawa suka aika da talenti dubu na azurfa don su yi haya da kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙi daga Aram-Naharayim, Aram Ma’aka da Zoba.
Abantwana bakoAmoni sebebonile ukuthi sebelevumba kuDavida, uHanuni labantwana bakoAmoni bathumela amathalenta esiliva ayinkulungwane ukuziqhatshela izinqola labagadi bamabhiza eMesopotamiya leSiriya-Mahaka leZoba.
7 Suka yi hayar kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙi dubu talatin da biyu, da kuma sarkin Ma’aka tare da mayaƙansa, waɗanda suka zo suka kafa sansani kusa da Medeba, yayinda Ammonawa suka tattaru daga garuruwansu suka fita yaƙi.
Basebeziqhatshela inqola ezizinkulungwane ezingamatshumi amathathu lambili lenkosi yeMahaka labantu bayo; basebesiza bamisa inkamba phambi kweMedeba; abantwana bakoAmoni basebebuthana bevela emizini yabo, beza empini.
8 Da jin haka, Dawuda ya aiki Yowab tare da dukan mayaƙa masu yaƙi.
UDavida esezwile wathuma uJowabi lebutho lonke lamaqhawe.
9 Ammonawa suka fito suka ja dāgā a ƙofar birninsu, yayinda sarakunan da suka zo, su kansu suka ware suna a fili.
Abantwana bakoAmoni basebephuma bahlela impi esangweni lomuzi, lamakhosi ayezile ayewodwa egangeni.
10 Yowab ya ga cewa akwai dāgā a gabansa da bayansa; sai ya zaɓi waɗansu mayaƙa mafi kyau a Isra’ila ya sa su a kan Arameyawa.
UJowabi esebonile ukuthi impondo zebutho zimelene laye ngaphambili langemuva, wakhetha kuwo wonke umkhethwa koIsrayeli, wabahlela ukumelana lamaSiriya.
11 Ya sa sauran mutanen a ƙarƙashin kulawar Abishai ɗan’uwansa, aka sa a kan Ammonawa.
Labaseleyo babantu wabanikela esandleni sikaAbishayi umfowabo; basebezihlela ukumelana labantwana bakoAmoni.
12 Yowab ya ce, “In Arameyawa suka fi ni ƙarfi, sai ka kawo mini ɗauke da ni; amma in Ammonawa sun fi ka ƙarfi, sai in kawo maka ɗauke.
Wasesithi: Uba amaSiriya engikhulela, uzakuba lusizo lwami; kodwa uba abantwana bakoAmoni bekukhulela, ngizakusiza.
13 Ka yi ƙarfin hali bari mu yi yaƙi da jaruntaka saboda mutanenmu da biranen Allahnmu. Ubangiji zai yi abin da ya ga ya yi masa kyau.”
Bana lesibindi, siziqinise ngenxa yabantu bakithi langenxa yemizi kaNkulunkulu wethu; leNkosi kayenze okuhle emehlweni ayo.
14 Sai Yowab da ƙungiyoyin mayaƙan da suke tare da shi suka matso don su yi yaƙi da Arameyawa, Arameyawan kuwa suka gudu a gabansa.
UJowabi labantu ababelaye basebesondela phambi kwamaSiriya ukuya empini; asebaleka phambi kwakhe.
15 Sa’ad da Ammonawa suka ga Arameyawa suna gudu, sai su ma suka guda a gaban ɗan’uwansa Abishai suka shiga cikin birni. Sai Yowab ya koma Urushalima.
Abantwana bakoAmoni sebebona ukuthi amaSiriya ayabaleka, babaleka labo phambi kukaAbishayi umfowabo, bangena emzini. UJowabi wasengena eJerusalema.
16 Bayan Arameyawa suka ga cewa Isra’ila sun ci su da yaƙi, sai suka aiki’yan aika suka sa aka kawo Arameyawan da suke hayen Kogi waɗanda Shobak shugaban mayaƙan Hadadezer yake shugabanta.
AmaSiriya esebonile ukuthi atshayiwe phambi kukaIsrayeli athuma izithunywa akhupha amaSiriya ayengaphetsheya komfula. LoShofaki induna yebutho likaHadadezeri wayephambi kwawo.
17 Sa’ad da aka faɗa wa Dawuda wannan, sai tattara dukan Isra’ila ya haye Urdun; ya tafi wurinsu ya kuwa ja dāgā ɗaura da su. Dawuda ya ja dāgārsa don yă sadu da Arameyawa a yaƙi, su kuwa suka yi yaƙi da shi.
Esetsheliwe uDavida, wabuthanisa uIsrayeli wonke, wachapha iJordani, wafika kibo, wahlela ibutho limelene lawo. UDavida esehlele impi ukumelana lamaSiriya, alwa laye.
18 Amma Arameyawa suka gudu a gaban Isra’ila, mutanen Dawuda kuwa suka kashe masu hawan keken yaƙinsu dubu bakwai da sojojin ƙasa dubu arba’in. Ya kuma kashe Shobak shugaban mayaƙansu.
Kodwa amaSiriya abaleka phambi kukaIsrayeli; uDavida wasebulala kumaSiriya abezinqola abazinkulungwane eziyisikhombisa, lamadoda ahamba ngenyawo azinkulungwane ezingamatshumi amane, wabulala loShofaki induna yebutho.
19 Da abokan tarayyar Hadadezer suka ga Isra’ila sun ci su da yaƙi, sai suka nemi salama da Dawuda suka kuma zama bayinsa. Saboda haka Arameyawa ba su ƙara yarda su taimaki Ammonawa ba.
Izinceku zikaHadadezeri sezibonile ukuthi zitshayiwe phambi kukaIsrayeli, zenza ukuthula loDavida, zamsebenzela. Ngakho amaSiriya kawafunanga ukusiza abantwana bakoAmoni futhi.

< 1 Tarihi 19 >