< 1 Tarihi 19 >

1 Ana nan, sai Nahash sarkin Ammonawa ya mutu, sai ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Or il arriva après cela que Nahas Roi des enfants de Hammon mourut, et son fils régna en sa place.
2 Dawuda ya yi tunani, “Zan nuna jinƙai ga Hanun ɗan Nahash, domin mahaifinsa ya nuna alheri gare ni.” Saboda haka Dawuda ya aika da tawaga don yă yi wa Hanun ta’aziyya game da mahaifinsa. Sa’ad da mutanen Dawuda suka iso wurin Hanun a ƙasar Ammonawa don su ta’azantar da shi,
Et David dit: J'userai de gratuité envers Hanun, fils de Nahas; car son père a usé de gratuité envers moi. Ainsi David envoya des messagers pour le consoler sur la mort de son père; et les serviteurs de David vinrent au pays des enfants de Hammon vers Hanun pour le consoler.
3 sai manyan Ammonawa suka ce wa Hanun, “Kana tsammani Dawuda yana girmama mahaifinka ne da ya aika mutanen nan wurinka su ta’azantar da kai? Ba mutanensa sun zo ne su bincika su kuma leƙi ƙasar su tumɓuke ta ba?”
Mais les principaux d'entre les enfants de Hammon dirent à Hanun: Penses-tu que ce soit pour honorer ton père que David t'a envoyé des consolateurs? n'est-ce pas pour examiner exactement et épier le pays, afin de le détruire, que ses serviteurs sont venus vers toi?
4 Saboda haka Hanun ya kama mutanen Dawuda, ya yi musu aski, ya yayyanka rigunansu a daidai ɗuwawunsu, sa’an nan ya sallame su.
Hanun donc prit les serviteurs de David, et les fit raser, et fit couper leurs habits par le milieu jusqu'aux hanches, puis il les renvoya.
5 Da wani ya zo ya faɗa wa Dawuda game da mutanen, sai ya aiki’yan aika su sadu da su, gama an ƙasƙantar da su ainun. Sarki ya ce, “Ku zauna a Yeriko har sai gemunku sun yi girma, sa’an nan ku dawo.”
Et ils s'en allèrent, et le firent savoir par [le moyen] de quelques personnes à David, qui envoya au devant d'eux; car ces hommes-là étaient fort confus. Et le Roi leur manda: Demeurez à Jérico jusqu'à ce que votre barbe soit recrue; et alors vous retournerez.
6 Sa’ad da Ammonawa suka gane cewa sun zama abin wurin a kafan hancin Dawuda, Hanun da Ammonawa suka aika da talenti dubu na azurfa don su yi haya da kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙi daga Aram-Naharayim, Aram Ma’aka da Zoba.
Or les enfants de Hammon voyant qu'ils s'étaient mis en mauvaise odeur auprès de David, Hanun et eux envoyèrent mille talents d'argent, pour prendre à leurs dépens des chariots et des gens de cheval de Mésopotamie, et de Syrie, de Mahaca, et de Tsoba.
7 Suka yi hayar kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙi dubu talatin da biyu, da kuma sarkin Ma’aka tare da mayaƙansa, waɗanda suka zo suka kafa sansani kusa da Medeba, yayinda Ammonawa suka tattaru daga garuruwansu suka fita yaƙi.
Et ils levèrent à leurs frais pour eux trente-deux mille hommes, [et] des chariots, et le Roi de Mahaca avec son peuple qui vinrent, et se campèrent devant Médeba. Les Hammonites aussi s'assemblèrent de leurs villes, et vinrent pour combattre.
8 Da jin haka, Dawuda ya aiki Yowab tare da dukan mayaƙa masu yaƙi.
Ce que David ayant appris, il envoya Joab, et ceux de toute l'armée qui étaient les plus vaillants.
9 Ammonawa suka fito suka ja dāgā a ƙofar birninsu, yayinda sarakunan da suka zo, su kansu suka ware suna a fili.
Et les enfants de Hammon sortirent, et rangèrent leur armée en bataille à l'entrée de la ville, et les Rois qui étaient venus, étaient à part dans la campagne.
10 Yowab ya ga cewa akwai dāgā a gabansa da bayansa; sai ya zaɓi waɗansu mayaƙa mafi kyau a Isra’ila ya sa su a kan Arameyawa.
Et Joab voyant que l'armée était tournée contre lui, devant et derrière, prit de tous les gens d'élite d'Israël, et les rangea contre les Syriens.
11 Ya sa sauran mutanen a ƙarƙashin kulawar Abishai ɗan’uwansa, aka sa a kan Ammonawa.
Et il donna la conduite du reste du peuple à Abisaï son frère; et on les rangea contre les enfants de Hammon.
12 Yowab ya ce, “In Arameyawa suka fi ni ƙarfi, sai ka kawo mini ɗauke da ni; amma in Ammonawa sun fi ka ƙarfi, sai in kawo maka ɗauke.
Et [Joab lui] dit: Si les Syriens sont plus forts que moi, tu viendras me délivrer; et si les enfants de Hammon sont plus forts que toi, je te délivrerai.
13 Ka yi ƙarfin hali bari mu yi yaƙi da jaruntaka saboda mutanenmu da biranen Allahnmu. Ubangiji zai yi abin da ya ga ya yi masa kyau.”
Sois vaillant, et portons-nous vaillamment pour notre peuple, et pour les villes de notre Dieu; et que l'Eternel fasse ce qui lui semblera bon.
14 Sai Yowab da ƙungiyoyin mayaƙan da suke tare da shi suka matso don su yi yaƙi da Arameyawa, Arameyawan kuwa suka gudu a gabansa.
Alors Joab et le peuple qui était avec lui s'approchèrent pour donner bataille aux Syriens, qui s'enfuirent de devant lui.
15 Sa’ad da Ammonawa suka ga Arameyawa suna gudu, sai su ma suka guda a gaban ɗan’uwansa Abishai suka shiga cikin birni. Sai Yowab ya koma Urushalima.
Et les enfants de Hammon voyant que les Syriens s'en étaient fuis, eux aussi s'enfuirent de devant Abisaï frère de Joab, et rentrèrent dans la ville; et Joab revint à Jérusalem.
16 Bayan Arameyawa suka ga cewa Isra’ila sun ci su da yaƙi, sai suka aiki’yan aika suka sa aka kawo Arameyawan da suke hayen Kogi waɗanda Shobak shugaban mayaƙan Hadadezer yake shugabanta.
Mais les Syriens, qui avaient été battus par ceux d'Israël, envoyèrent des messagers, et firent venir les Syriens qui étaient au delà du fleuve; et Sophach capitaine de l'armée de Hadarhézer les conduisait.
17 Sa’ad da aka faɗa wa Dawuda wannan, sai tattara dukan Isra’ila ya haye Urdun; ya tafi wurinsu ya kuwa ja dāgā ɗaura da su. Dawuda ya ja dāgārsa don yă sadu da Arameyawa a yaƙi, su kuwa suka yi yaƙi da shi.
Ce qui ayant été rapporté à David, il assembla tout Israël, et passa le Jourdain, et alla au devant d'eux, et se rangea en bataille contr'eux. David donc rangea la bataille contre les Syriens, et ils combattirent contre lui.
18 Amma Arameyawa suka gudu a gaban Isra’ila, mutanen Dawuda kuwa suka kashe masu hawan keken yaƙinsu dubu bakwai da sojojin ƙasa dubu arba’in. Ya kuma kashe Shobak shugaban mayaƙansu.
Mais les Syriens s'enfuirent de devant Israël; et David défit sept mille chariots des Syriens, et quarante mille hommes de pied, et il tua Sophach le Chef de l'armée.
19 Da abokan tarayyar Hadadezer suka ga Isra’ila sun ci su da yaƙi, sai suka nemi salama da Dawuda suka kuma zama bayinsa. Saboda haka Arameyawa ba su ƙara yarda su taimaki Ammonawa ba.
Alors les serviteurs de Hadarhézer voyant qu'ils avaient été battus par ceux d'Israël, firent la paix avec David, et lui furent asservis; et les Syriens ne voulurent plus secourir les enfants de Hammon.

< 1 Tarihi 19 >