< 1 Tarihi 19 >
1 Ana nan, sai Nahash sarkin Ammonawa ya mutu, sai ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Et il arriva, après cela, que Nakhash, roi des fils d’Ammon, mourut; et son fils régna à sa place.
2 Dawuda ya yi tunani, “Zan nuna jinƙai ga Hanun ɗan Nahash, domin mahaifinsa ya nuna alheri gare ni.” Saboda haka Dawuda ya aika da tawaga don yă yi wa Hanun ta’aziyya game da mahaifinsa. Sa’ad da mutanen Dawuda suka iso wurin Hanun a ƙasar Ammonawa don su ta’azantar da shi,
Et David dit: J’userai de bonté envers Hanun, fils de Nakhash, car son père a usé de bonté envers moi. Et David envoya des messagers pour le consoler au sujet de son père. Et les serviteurs de David arrivèrent dans le pays des fils d’Ammon, vers Hanun, pour le consoler.
3 sai manyan Ammonawa suka ce wa Hanun, “Kana tsammani Dawuda yana girmama mahaifinka ne da ya aika mutanen nan wurinka su ta’azantar da kai? Ba mutanensa sun zo ne su bincika su kuma leƙi ƙasar su tumɓuke ta ba?”
Et les chefs des fils d’Ammon dirent à Hanun: Est-ce, à tes yeux, pour honorer ton père que David t’a envoyé des consolateurs? N’est-ce pas pour reconnaître et détruire et explorer le pays, que ses serviteurs sont venus vers toi?
4 Saboda haka Hanun ya kama mutanen Dawuda, ya yi musu aski, ya yayyanka rigunansu a daidai ɗuwawunsu, sa’an nan ya sallame su.
Et Hanun prit les serviteurs de David, et les fit raser, et fit couper leurs vêtements par le milieu jusqu’au bas des reins, et les renvoya.
5 Da wani ya zo ya faɗa wa Dawuda game da mutanen, sai ya aiki’yan aika su sadu da su, gama an ƙasƙantar da su ainun. Sarki ya ce, “Ku zauna a Yeriko har sai gemunku sun yi girma, sa’an nan ku dawo.”
Et on alla, et on informa David au sujet de ces hommes; et il envoya à leur rencontre, car les hommes étaient très confus. Et le roi dit: Habitez à Jéricho jusqu’à ce que votre barbe ait poussé, alors vous reviendrez.
6 Sa’ad da Ammonawa suka gane cewa sun zama abin wurin a kafan hancin Dawuda, Hanun da Ammonawa suka aika da talenti dubu na azurfa don su yi haya da kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙi daga Aram-Naharayim, Aram Ma’aka da Zoba.
Et les fils d’Ammon virent qu’ils s’étaient mis en mauvaise odeur auprès de David; et Hanun et les fils d’Ammon envoyèrent 1 000 talents d’argent pour prendre à leur solde, de la Mésopotamie, et de la Syrie de Maaca, et de Tsoba, des chars et des cavaliers.
7 Suka yi hayar kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙi dubu talatin da biyu, da kuma sarkin Ma’aka tare da mayaƙansa, waɗanda suka zo suka kafa sansani kusa da Medeba, yayinda Ammonawa suka tattaru daga garuruwansu suka fita yaƙi.
Et ils prirent à leur solde 32 000 hommes de chars, et le roi de Maaca avec son peuple; et ils vinrent et campèrent devant Médeba. Et les fils d’Ammon s’assemblèrent de leurs villes, et vinrent pour combattre.
8 Da jin haka, Dawuda ya aiki Yowab tare da dukan mayaƙa masu yaƙi.
Et David l’apprit, et il envoya Joab et toute l’armée, les hommes forts.
9 Ammonawa suka fito suka ja dāgā a ƙofar birninsu, yayinda sarakunan da suka zo, su kansu suka ware suna a fili.
Et les fils d’Ammon sortirent, et se rangèrent en bataille à l’entrée de la ville; et les rois qui étaient venus étaient à part dans la campagne.
10 Yowab ya ga cewa akwai dāgā a gabansa da bayansa; sai ya zaɓi waɗansu mayaƙa mafi kyau a Isra’ila ya sa su a kan Arameyawa.
Et Joab vit que le front de la bataille était contre lui, devant et derrière; et il choisit des hommes de toute l’élite d’Israël, et les rangea contre les Syriens;
11 Ya sa sauran mutanen a ƙarƙashin kulawar Abishai ɗan’uwansa, aka sa a kan Ammonawa.
et le reste du peuple, il le plaça sous la main d’Abishaï, son frère, et ils se rangèrent contre les fils d’Ammon.
12 Yowab ya ce, “In Arameyawa suka fi ni ƙarfi, sai ka kawo mini ɗauke da ni; amma in Ammonawa sun fi ka ƙarfi, sai in kawo maka ɗauke.
Et il dit: Si les Syriens sont plus forts que moi, tu me seras en aide; et si les fils d’Ammon sont plus forts que toi, je t’aiderai.
13 Ka yi ƙarfin hali bari mu yi yaƙi da jaruntaka saboda mutanenmu da biranen Allahnmu. Ubangiji zai yi abin da ya ga ya yi masa kyau.”
Sois fort, et fortifions-nous à cause de notre peuple et à cause des villes de notre Dieu; et que l’Éternel fasse ce qui est bon à ses yeux.
14 Sai Yowab da ƙungiyoyin mayaƙan da suke tare da shi suka matso don su yi yaƙi da Arameyawa, Arameyawan kuwa suka gudu a gabansa.
Et Joab s’approcha, et le peuple qui était avec lui, au-devant des Syriens, pour livrer bataille; et ils s’enfuirent devant lui.
15 Sa’ad da Ammonawa suka ga Arameyawa suna gudu, sai su ma suka guda a gaban ɗan’uwansa Abishai suka shiga cikin birni. Sai Yowab ya koma Urushalima.
Et quand les fils d’Ammon virent que les Syriens s’étaient enfuis, ils s’enfuirent, eux aussi, devant Abishaï, son frère, et rentrèrent dans la ville. Et Joab vint à Jérusalem.
16 Bayan Arameyawa suka ga cewa Isra’ila sun ci su da yaƙi, sai suka aiki’yan aika suka sa aka kawo Arameyawan da suke hayen Kogi waɗanda Shobak shugaban mayaƙan Hadadezer yake shugabanta.
Et quand les Syriens virent qu’ils étaient battus devant Israël, ils envoyèrent des messagers, et firent sortir les Syriens qui étaient au-delà du fleuve; et Shophac, chef de l’armée d’Hadarézer, était à leur tête.
17 Sa’ad da aka faɗa wa Dawuda wannan, sai tattara dukan Isra’ila ya haye Urdun; ya tafi wurinsu ya kuwa ja dāgā ɗaura da su. Dawuda ya ja dāgārsa don yă sadu da Arameyawa a yaƙi, su kuwa suka yi yaƙi da shi.
Et cela fut rapporté à David, et il assembla tout Israël, et passa le Jourdain, et vint à eux, et se rangea [en bataille] contre eux. Et David se rangea en bataille contre les Syriens; et ils se battirent avec lui.
18 Amma Arameyawa suka gudu a gaban Isra’ila, mutanen Dawuda kuwa suka kashe masu hawan keken yaƙinsu dubu bakwai da sojojin ƙasa dubu arba’in. Ya kuma kashe Shobak shugaban mayaƙansu.
Et les Syriens s’enfuirent de devant Israël; et David tua aux Syriens 7 000 chars, et 40 000 hommes de pied, et il mit à mort Shophac, chef de l’armée.
19 Da abokan tarayyar Hadadezer suka ga Isra’ila sun ci su da yaƙi, sai suka nemi salama da Dawuda suka kuma zama bayinsa. Saboda haka Arameyawa ba su ƙara yarda su taimaki Ammonawa ba.
Et les serviteurs d’Hadarézer virent qu’ils étaient battus devant Israël, et ils firent la paix avec David, et le servirent. Et les Syriens ne voulurent plus aider les fils d’Ammon.