< 1 Tarihi 19 >
1 Ana nan, sai Nahash sarkin Ammonawa ya mutu, sai ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Après cela, Nachash, roi des enfants d'Ammon, mourut, et son fils régna à sa place.
2 Dawuda ya yi tunani, “Zan nuna jinƙai ga Hanun ɗan Nahash, domin mahaifinsa ya nuna alheri gare ni.” Saboda haka Dawuda ya aika da tawaga don yă yi wa Hanun ta’aziyya game da mahaifinsa. Sa’ad da mutanen Dawuda suka iso wurin Hanun a ƙasar Ammonawa don su ta’azantar da shi,
David dit: « Je ferai preuve de bonté envers Hanoun, fils de Nahash, car son père a fait preuve de bonté envers moi. » David envoya donc des messagers pour le consoler au sujet de son père. Les serviteurs de David vinrent au pays des enfants d'Ammon auprès de Hanun pour le consoler.
3 sai manyan Ammonawa suka ce wa Hanun, “Kana tsammani Dawuda yana girmama mahaifinka ne da ya aika mutanen nan wurinka su ta’azantar da kai? Ba mutanensa sun zo ne su bincika su kuma leƙi ƙasar su tumɓuke ta ba?”
Mais les princes des enfants d'Ammon dirent à Hanun: « Crois-tu que David honore ton père, en t'envoyant des consolateurs? Ses serviteurs ne sont-ils pas venus vers toi pour fouiller, renverser et épier le pays? »
4 Saboda haka Hanun ya kama mutanen Dawuda, ya yi musu aski, ya yayyanka rigunansu a daidai ɗuwawunsu, sa’an nan ya sallame su.
Hanun prit donc les serviteurs de David, les rasa, coupa leurs vêtements par le milieu, au niveau des fesses, et les renvoya.
5 Da wani ya zo ya faɗa wa Dawuda game da mutanen, sai ya aiki’yan aika su sadu da su, gama an ƙasƙantar da su ainun. Sarki ya ce, “Ku zauna a Yeriko har sai gemunku sun yi girma, sa’an nan ku dawo.”
Puis des gens allèrent raconter à David comment les hommes avaient été traités. Il envoya à leur rencontre, car les hommes étaient très humiliés. Le roi leur dit: « Restez à Jéricho jusqu'à ce que votre barbe ait poussé, et revenez ensuite. »
6 Sa’ad da Ammonawa suka gane cewa sun zama abin wurin a kafan hancin Dawuda, Hanun da Ammonawa suka aika da talenti dubu na azurfa don su yi haya da kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙi daga Aram-Naharayim, Aram Ma’aka da Zoba.
Lorsque les fils d'Ammon virent qu'ils s'étaient rendus odieux à David, Hanun et les fils d'Ammon envoyèrent mille talents d'argent pour louer des chars et des cavaliers de Mésopotamie, d'Aram-Maaca et de Tsoba.
7 Suka yi hayar kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙi dubu talatin da biyu, da kuma sarkin Ma’aka tare da mayaƙansa, waɗanda suka zo suka kafa sansani kusa da Medeba, yayinda Ammonawa suka tattaru daga garuruwansu suka fita yaƙi.
Ils louèrent ainsi pour eux-mêmes trente-deux mille chars, et le roi de Maaca avec son peuple, qui vint camper près de Medeba. Les enfants d'Ammon se rassemblèrent de leurs villes et vinrent au combat.
8 Da jin haka, Dawuda ya aiki Yowab tare da dukan mayaƙa masu yaƙi.
David l'apprit, et il envoya Joab avec toute l'armée des vaillants hommes.
9 Ammonawa suka fito suka ja dāgā a ƙofar birninsu, yayinda sarakunan da suka zo, su kansu suka ware suna a fili.
Les fils d'Ammon sortirent, et se rangèrent en bataille à la porte de la ville; et les rois qui étaient venus étaient seuls dans les champs.
10 Yowab ya ga cewa akwai dāgā a gabansa da bayansa; sai ya zaɓi waɗansu mayaƙa mafi kyau a Isra’ila ya sa su a kan Arameyawa.
Et Joab, voyant que la bataille était engagée contre lui devant et derrière, choisit quelques-uns de tous les hommes d'élite d'Israël, et les plaça en bataille contre les Syriens.
11 Ya sa sauran mutanen a ƙarƙashin kulawar Abishai ɗan’uwansa, aka sa a kan Ammonawa.
Il remit le reste du peuple entre les mains d'Abishaï, son frère, et ils se rangèrent en bataille contre les fils d'Ammon.
12 Yowab ya ce, “In Arameyawa suka fi ni ƙarfi, sai ka kawo mini ɗauke da ni; amma in Ammonawa sun fi ka ƙarfi, sai in kawo maka ɗauke.
Il dit: « Si les Syriens sont trop forts pour moi, tu m'aideras; mais si les enfants d'Ammon sont trop forts pour toi, je t'aiderai.
13 Ka yi ƙarfin hali bari mu yi yaƙi da jaruntaka saboda mutanenmu da biranen Allahnmu. Ubangiji zai yi abin da ya ga ya yi masa kyau.”
Soyez courageux, et soyons forts pour notre peuple et pour les villes de notre Dieu. Que Yahvé fasse ce qui lui semble bon. »
14 Sai Yowab da ƙungiyoyin mayaƙan da suke tare da shi suka matso don su yi yaƙi da Arameyawa, Arameyawan kuwa suka gudu a gabansa.
Joab et le peuple qui était avec lui s'approchèrent du front des Syriens pour livrer bataille, et ils s'enfuirent devant lui.
15 Sa’ad da Ammonawa suka ga Arameyawa suna gudu, sai su ma suka guda a gaban ɗan’uwansa Abishai suka shiga cikin birni. Sai Yowab ya koma Urushalima.
Lorsque les fils d'Ammon virent que les Syriens s'étaient enfuis, ils s'enfuirent également devant Abischaï, son frère, et entrèrent dans la ville. Puis Joab arriva à Jérusalem.
16 Bayan Arameyawa suka ga cewa Isra’ila sun ci su da yaƙi, sai suka aiki’yan aika suka sa aka kawo Arameyawan da suke hayen Kogi waɗanda Shobak shugaban mayaƙan Hadadezer yake shugabanta.
Lorsque les Syriens virent qu'ils avaient été vaincus par Israël, ils envoyèrent des messagers et appelèrent les Syriens qui étaient au-delà du fleuve, avec à leur tête Shophach, chef de l'armée d'Hadadézer.
17 Sa’ad da aka faɗa wa Dawuda wannan, sai tattara dukan Isra’ila ya haye Urdun; ya tafi wurinsu ya kuwa ja dāgā ɗaura da su. Dawuda ya ja dāgārsa don yă sadu da Arameyawa a yaƙi, su kuwa suka yi yaƙi da shi.
David fut informé de cela, il rassembla tout Israël, passa le Jourdain, vint vers eux et se mit en ordre de bataille contre eux. David se mit en ordre de bataille contre les Syriens, qui combattirent avec lui.
18 Amma Arameyawa suka gudu a gaban Isra’ila, mutanen Dawuda kuwa suka kashe masu hawan keken yaƙinsu dubu bakwai da sojojin ƙasa dubu arba’in. Ya kuma kashe Shobak shugaban mayaƙansu.
Les Syriens prirent la fuite devant Israël, et David tua parmi les Syriens sept mille chars et quarante mille hommes de pied, et il tua aussi Shophach, le chef de l'armée.
19 Da abokan tarayyar Hadadezer suka ga Isra’ila sun ci su da yaƙi, sai suka nemi salama da Dawuda suka kuma zama bayinsa. Saboda haka Arameyawa ba su ƙara yarda su taimaki Ammonawa ba.
Lorsque les serviteurs d'Hadadézer virent qu'ils avaient été vaincus par Israël, ils firent la paix avec David et le servirent. Les Syriens ne voulurent plus aider les enfants d'Ammon.