< 1 Tarihi 19 >

1 Ana nan, sai Nahash sarkin Ammonawa ya mutu, sai ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Some time later, Nahash, the king of the Ammon people-group, died. Then his son Hanun became their king.
2 Dawuda ya yi tunani, “Zan nuna jinƙai ga Hanun ɗan Nahash, domin mahaifinsa ya nuna alheri gare ni.” Saboda haka Dawuda ya aika da tawaga don yă yi wa Hanun ta’aziyya game da mahaifinsa. Sa’ad da mutanen Dawuda suka iso wurin Hanun a ƙasar Ammonawa don su ta’azantar da shi,
[When] David [heard about that, he] thought [to himself], “Nahash was kind to me, so I will be kind to his son.” So David sent some officials there, to tell Hanun that he was sorry to hear that Hanun’s father [had died]. But when David’s officials came to Hanun in the land where the Ammon people-group lived,
3 sai manyan Ammonawa suka ce wa Hanun, “Kana tsammani Dawuda yana girmama mahaifinka ne da ya aika mutanen nan wurinka su ta’azantar da kai? Ba mutanensa sun zo ne su bincika su kuma leƙi ƙasar su tumɓuke ta ba?”
the leaders of the Ammon people-group said to Hanun, “Do you think that it is really to honor your father that King David is sending these men to say that he is sorry that your father died? [We think that] his men have come to (look around/spy) our city in order to determine how his [army] can conquer us.”
4 Saboda haka Hanun ya kama mutanen Dawuda, ya yi musu aski, ya yayyanka rigunansu a daidai ɗuwawunsu, sa’an nan ya sallame su.
Hanun [believed what they said, so he commanded some soldiers to] seize the officials whom David had sent, and shave off their beards, and [insult them by] cutting off the lower part of their robes, and then send them away. [So his soldiers did that].
5 Da wani ya zo ya faɗa wa Dawuda game da mutanen, sai ya aiki’yan aika su sadu da su, gama an ƙasƙantar da su ainun. Sarki ya ce, “Ku zauna a Yeriko har sai gemunku sun yi girma, sa’an nan ku dawo.”
The officials were greatly humiliated/ashamed. When David found out about what had happened to his officials, he sent some messengers to them to tell them, “Stay at Jericho until your beards have grown again, and then return home.”
6 Sa’ad da Ammonawa suka gane cewa sun zama abin wurin a kafan hancin Dawuda, Hanun da Ammonawa suka aika da talenti dubu na azurfa don su yi haya da kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙi daga Aram-Naharayim, Aram Ma’aka da Zoba.
Then the [leaders of the] Ammon people-group realized that they had greatly insulted [IDM] David. So Hanun and some of his officials sent about (37,000 pounds/34,000 kg.) of silver to hire chariots and chariot-drivers from [the] Aram-Naharaim, Aram-Maacah and Zobah [regions of Syria northeast of Israel].
7 Suka yi hayar kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙi dubu talatin da biyu, da kuma sarkin Ma’aka tare da mayaƙansa, waɗanda suka zo suka kafa sansani kusa da Medeba, yayinda Ammonawa suka tattaru daga garuruwansu suka fita yaƙi.
They hired 32,000 chariots and chariot-drivers, as well as the king of [the] Maacah [region] and his army. They came and set up their tents near Medeba [town in Moab region]. The soldiers from the Ammon people-group also marched out and (stood in their positions/arranged themselves for battle) [at the entrance to their capital city, Rabbah].
8 Da jin haka, Dawuda ya aiki Yowab tare da dukan mayaƙa masu yaƙi.
When David heard about that, he sent Joab and all his army.
9 Ammonawa suka fito suka ja dāgā a ƙofar birninsu, yayinda sarakunan da suka zo, su kansu suka ware suna a fili.
The soldiers of the Ammon people-group came out of their city and lined up for battle at the entrance to [their capital city, Rabbah]. Meanwhile, the other kings who had come [with their armies] stood in their positions in the open fields.
10 Yowab ya ga cewa akwai dāgā a gabansa da bayansa; sai ya zaɓi waɗansu mayaƙa mafi kyau a Isra’ila ya sa su a kan Arameyawa.
Joab saw that there were groups of enemy soldiers in front of his troops and behind his troops. So he selected some of the best Israeli troops and put them in positions to fight against the soldiers of Syria.
11 Ya sa sauran mutanen a ƙarƙashin kulawar Abishai ɗan’uwansa, aka sa a kan Ammonawa.
He appointed his [older] brother Abishai to be the commander of his other soldiers and he told them to (stand in their positions/arrange themselves) in front of [the army of] the Ammon people-group.
12 Yowab ya ce, “In Arameyawa suka fi ni ƙarfi, sai ka kawo mini ɗauke da ni; amma in Ammonawa sun fi ka ƙarfi, sai in kawo maka ɗauke.
Joab said to them, “If the soldiers from Syria are too strong for us to defeat them, then your soldiers must come and help us. But if the soldiers from the Ammon people-group are too strong for you to defeat them, then my soldiers will come and help your men.
13 Ka yi ƙarfin hali bari mu yi yaƙi da jaruntaka saboda mutanenmu da biranen Allahnmu. Ubangiji zai yi abin da ya ga ya yi masa kyau.”
We must be strong/courageous, and fight hard to [defend] our people and our cities (that belong to/where we worship) our God. I will pray that Yahweh will do what he considers to be good.”
14 Sai Yowab da ƙungiyoyin mayaƙan da suke tare da shi suka matso don su yi yaƙi da Arameyawa, Arameyawan kuwa suka gudu a gabansa.
So Joab and his troops [advanced to] fight the army of Syria, and the soldiers from Syria ran away from them.
15 Sa’ad da Ammonawa suka ga Arameyawa suna gudu, sai su ma suka guda a gaban ɗan’uwansa Abishai suka shiga cikin birni. Sai Yowab ya koma Urushalima.
And when the soldiers of the Ammon people-group saw that the soldiers from Syria were running away, they also started to run away from Abishai and his army, and they retreated back inside the city. So Joab [and his army] returned to Jerusalem.
16 Bayan Arameyawa suka ga cewa Isra’ila sun ci su da yaƙi, sai suka aiki’yan aika suka sa aka kawo Arameyawan da suke hayen Kogi waɗanda Shobak shugaban mayaƙan Hadadezer yake shugabanta.
After [the leaders of the army of] Syria realized that they had been defeated by [the army of] Israel, they sent messengers to [another part of Syria on] the east side of the [Euphrates] river, and brought troops from there [to the battle area], with Shophach, the commander of Hadadezer’s army, leading them.
17 Sa’ad da aka faɗa wa Dawuda wannan, sai tattara dukan Isra’ila ya haye Urdun; ya tafi wurinsu ya kuwa ja dāgā ɗaura da su. Dawuda ya ja dāgārsa don yă sadu da Arameyawa a yaƙi, su kuwa suka yi yaƙi da shi.
When David heard about that, he gathered all the Israeli soldiers, and they crossed the Jordan [River]. They advanced and took their battle positions to attack the army of Syria.
18 Amma Arameyawa suka gudu a gaban Isra’ila, mutanen Dawuda kuwa suka kashe masu hawan keken yaƙinsu dubu bakwai da sojojin ƙasa dubu arba’in. Ya kuma kashe Shobak shugaban mayaƙansu.
But the army of Syria ran away from the soldiers of Israel. However, David’s soldiers killed 7,000 of their chariot-drivers and 40,000 other soldiers. They also killed Shophach, their army commander.
19 Da abokan tarayyar Hadadezer suka ga Isra’ila sun ci su da yaƙi, sai suka nemi salama da Dawuda suka kuma zama bayinsa. Saboda haka Arameyawa ba su ƙara yarda su taimaki Ammonawa ba.
When the kings who had been ruled by Hadadezer realized that they had been defeated by the Israeli army, they made peace with David, and agreed to allow him to rule them. So the rulers of Syria did not want to help the rulers of the Ammon people-group any more.

< 1 Tarihi 19 >