< 1 Tarihi 18 >

1 Ana nan sai Dawuda ya ci Filistiyawa ya kuma rinjaye su, ya ƙwace Gat da ƙauyukan kewayenta daga mulkin Filistiyawa.
And it came to pass after this, that David smote the Philistines, and humbled them; and he took Gath and its dependent towns out of the hand of the Philistines.
2 Dawuda ya kuma ci Mowabawa, suka zama bayinsa suka kuma biya haraji.
And he smote Moab, and the Moabites became David's servants, bringing presents.
3 Ban da haka, Dawuda ya yaƙi Hadadezer sarkin Zoba, har can Hamat, sa’ad da ya je don yă kafa mulkinsa a wajen Kogin Yuferites.
David also smote Hadar'ezer the king of Zobah, at Chamath, as he went to establish his dominion at the river Euphrates.
4 Dawuda ya kame keken yaƙinsa dubu ɗaya, da mahayan kekunan yaƙi dubu bakwai da sojojin kafa guda dubu ashirin. Ya yayyanke dukan agaran dawakansa, amma ya bar dawakai da suka isa jan kekunan yaƙi ɗari.
And David captured from him a thousand chariots, and seven thousand horsemen, and twenty thousand men on foot; and David hamstringed all the chariot-teams, but reserved of them a hundred chariot-teams.
5 Da Arameyawan Damaskus suka zo su taimaki Hadadezer sarkin Zoba, sai Dawuda ya bugi dubu ashirin da biyunsu.
And the Syrians of Damascus came to aid Hadar'ezer the king of Zobah, when David slew of the Syrians two and twenty thousand men.
6 Ya sa ƙungiyoyin sojoji a masarautar Arameyawan Damaskus. Arameyawan kuwa suka zama bayinsa, suka kuma kawo haraji. Ubangiji ya ba Dawuda nasara a ko’ina da ya tafi.
Then did David put [garrisons] in Syria of Damascus, and the Syrians became unto David servants, bringing presents. And the Lord helped David withersoever he went.
7 Dawuda ya kwashe garkuwoyin zinariyan da shugabannin sojojin Hadadezer suke riƙe, ya kawo su Urushalima.
And David took the quivers of gold that were on the servants of Hadar'ezer, and brought them to Jerusalem.
8 Daga Teba da Kun, garuruwan da suke ƙarƙashin Hadadezer, Dawuda ya kwashe tagulla da yawa sosai, wanda Solomon ya yi amfani don yă yi Tekun tagulla, ginshiƙai da kuma kayayyakin tagulla dabam-dabam.
And from Tibchath, and from Kun, cities of Hadar'ezer, did David take exceedingly much copper; thereof made Solomon the copper sea, and the pillars, and the vessels of copper.
9 Sa’ad da Towu sarkin Hamat ya ji cewa Dawuda ya ci mayaƙan Hadadezer sarkin Zoba gaba ɗaya,
And when To'u the king of Chamath heard that David had smitten all the host of Hadar'ezer the king of Zobah:
10 sai ya aiki ɗansa Hadoram zuwa wurin Sarki Dawuda yă gaishe shi yă kuma yi masa barka da nasara a yaƙi a kan Hadadezer, wanda yake yaƙi da Towu. Hadoram ya kawo kowane irin kayayyakin zinariya da na azurfa da na tagulla.
Then did he send Hadoram his son unto king David, to ask him after his well-being, and to bless him, because he had fought against Hadar'ezer, and smitten him: for Hadar'ezer had been engaged in wars with To'u; and [he had with him] all manner of vessels of gold and silver and copper.
11 Sarki Dawuda ya miƙa waɗannan kayayyakin ga Ubangiji, kamar yadda ya yi da azurfa da kuma zinariyan da ya kwaso daga dukan waɗannan al’ummai. Edom da Mowab, Ammonawa da Filistiyawa, da kuma Amalek.
Also these did king David sanctify unto the Lord, with the silver and the gold that he had carried away from all the nations, from Edom, and from Moab, and from the children of 'Ammon, and from the Philistines, and from 'Amalek.
12 Abishai ɗan Zeruhiya ya bugi mutanen Edom dubu goma sha takwas a Kwarin Gishiri.
And Abshai the son of Zeruyah smote of the Edomites in the valley of salt eighteen thousand [men].
13 Ya sa ƙungiyoyin sojoji a Edom, dukan mutanen Edom kuwa suka zama bayin Dawuda. Ubangiji ya ba Dawuda nasara a ko’ina da ya tafi.
And he put garrisons in Edom, and all the Edomites became servants unto David. And the Lord helped David withersoever he went.
14 Dawuda ya yi mulki a bisa dukan Isra’ila, yana yin abin da yake daidai da kuma gaskiya saboda dukan mutanensa.
And David reigned over all Israel, and he did what is just and right unto all his people.
15 Yowab ɗan Zeruhiya shi ne shugaban mayaƙa; Yehoshafat ɗan Ahilud shi ne marubuci;
And Joab the son of Zeruyah was over the army, and Jehoshaphat the son of Achilud, recorder.
16 Zadok ɗan Ahitub da Abimelek ɗan Abiyatar su ne firistoci; Shafsha shi ne magatakarda;
And Zadok the son of Achitub, and Abimelech the son of Ebyathar, were [the] priests; and Shavsha was scribe;
17 Benahiya ɗan Yehohiyada shi ne shugaban Keretawa da Feletiyawa;’ya’yan Dawuda maza su ne manyan ma’aikata a gefen sarki.
And Benayahu the son of Jehoyada' was over the Kerethites and the Pelethites; and the sons of David were the first at the side of the king.

< 1 Tarihi 18 >