< 1 Tarihi 17 >

1 Bayan Dawuda ya zauna a fadansa, sai ya ce wa annabi Natan, “Ga ni, ina zama a fadar da aka yi da al’ul, yayinda akwatin alkawarin Ubangiji yana a ƙarƙashin tenti.”
Pripetilo se je torej, medtem ko je David sedel v svoji hiši, da je David rekel preroku Natánu: »Glej, jaz prebivam v cedrovi hiši, toda skrinja Gospodove zaveze ostaja pod zavesami.«
2 Natan ya amsa wa Dawuda ya ce, “Duk abin da kake tunani a zuciya, ka yi, gama Allah yana tare da kai.”
Potem je Natán rekel Davidu: »Stôri vse, kar je v tvojem srcu, kajti Bog je s teboj.«
3 A daren nan maganar Allah ta zo wa Natan cewa,
Iste noči se je pripetilo, da je Božja beseda prišla k Natánu, rekoč:
4 “Ka tafi ka faɗa wa bawana Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce ba kai ba ne za ka gida mini gidan da zan zauna a ciki.
»Pojdi in povej mojemu služabniku Davidu: ›Tako govori Gospod: ›Ti mi ne boš gradil hiše, da prebivam v njej,
5 Ban taɓa zama a gida daga ranar da na fito da Isra’ila daga Masar ba har wa yau. Na yi ta yawo daga gefen da aka kafa tenti zuwa wani, daga wannan wuri zuwa wancan.
kajti nisem prebival v hiši od dne, ko sem Izraela privedel gor, do današnjega dne, temveč sem šel od šotora k šotoru in od enega šotorskega svetišča k drugemu.
6 Duk inda na tafi tare da Isra’ilawa, na taɓa ce wa wani daga cikin shugabanninsu waɗanda na umarta su yi kiwon mutanena, “Don me ba ku gida mini gidan al’ul ba?”’
Kjerkoli sem hodil z vsem Izraelom, sem mar spregovoril besedo kateremukoli izmed Izraelovih sodnikov, ki sem jim zapovedal, da pasejo moje ljudstvo, rekoč: ›Zakaj mi niste zgradili cedrove hiše?‹
7 “Yanzu, ka faɗa wa bawana Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, na ɗauke ka daga makiyaya da kuma daga bin garke, don ka zama mai mulki a bisa mutanena Isra’ila.
Zdaj boš torej tako povedal mojemu služabniku Davidu: ›Tako govori Gospod nad bojevniki: ›Vzel sem te iz staje za ovce, celó od sledenja ovcam, da bi bil vladar nad mojim ljudstvom Izraelom,
8 Na kasance tare da kai ko’ina ka tafi, na kuma yanke dukan abokan gābanka a gabanka. Yanzu zan sa sunanka kamar sunayen mutane mafi girma na duniya.
in s teboj sem bil kjerkoli si hodil in pred teboj sem iztrebil vse tvoje sovražnike in ti naredil ime, podobno imenu velikih mož, ki so na zemlji.
9 Zan kuma tanada wuri domin mutanena Isra’ila, zan kuma kafa su saboda za su kasance da gidan kansu ba kuwa za a ƙara damunsu ba. Mugayen mutane ba za su ƙara zaluntar su ba, yadda suka yi da farko
Prav tako bom določil kraj za svoje ljudstvo Izrael in jih zasadil in bodo prebivali na svojem kraju in ne bodo več seljeni niti jih ne bodo več pustošili otroci zlobnosti kakor poprej
10 da kuma suka yi tun lokacin da na sa shugabanni a bisa mutanen Isra’ila. Zan rinjaye dukan abokan gābanka. “‘Na furta maka cewa Ubangiji zai gina maka gida,
in odkar sem zapovedal sodnikom, naj bodo nad mojim ljudstvom Izraelom. Poleg tega bom podjarmil vse tvoje sovražnike. Nadalje ti povem še, da ti bo Gospod zgradil hišo.
11 sa’ad da kwanakinka suka ƙare ka kuma tafi don ka kasance da kakanninka, zan tā da ɗaya cikin’ya’yanka maza, daga zuriyarka yă gāje ka, zan kuma kafa mulkinka.
Zgodilo se bo, ko bodo tvoji dnevi pretekli, da moraš oditi, da boš s svojimi očeti, da bom obudil tvoje seme za teboj, ki bo izmed tvojih sinov in jaz bom utrdil njegovo kraljestvo.
12 Shi ne zai gina gida domina, zan kuma kafa sarautarsa har abada.
Zgradil mi bo hišo in njegov prestol bom utrdil na veke.
13 Zan zama Ubansa, zai kuma zama ɗana. Ba zan taɓa ɗauke ƙaunata daga gare shi, kamar yadda na ɗauke ta daga wanda ya riga ka ba.
Jaz bom njegov oče in on bo moj sin. Svoje milosti ne bom odvzel od njega, kakor sem jo odvzel tistemu, ki je bil pred teboj,
14 Zan sa shi a bisa gidana da mulkina har abada; kujerar sarautarsa za tă kahu har abada.’”
temveč ga bom postavil v svoji hiši in v svojem kraljestvu na veke in njegov prestol bo utrjen na vékomaj.‹«
15 Natan ya faɗa wa Dawuda dukan kalmomin wahayin nan.
Glede na vse te besede in glede na vse to videnje, tako je Natán govoril Davidu.
16 Sai Sarki Dawuda ya shiga ya zauna a gaban Ubangiji ya ce, “Wane ne ni, ya Ubangiji Allah, kuma wane ne iyalina, da ka kawo ni har zuwa nan?
Kralj David je prišel in se usedel pred Gospodom ter rekel: »Kdo sem jaz, oh Gospod Bog in kaj je moja hiša, da si me privedel sèm?
17 Kuma sai ka ce wannan bai isa ba a idonka, ya Allah, ka yi magana game da nan gaba na gidan bawanka. Ka dube ni sai ka ce ni ne mafi ɗaukaka cikin mutane, ya Ubangiji Allah.
Vendar je bila to majhna stvar v tvojih očeh, oh Bog, kajti govoril si tudi o hiši svojega služabnika za oddaljeni čas, ki pride in si se ozrl name glede na stan človeka visoke stopnje, oh Gospod Bog.
18 “Me kuma Dawuda zai ce maka saboda girmamawar da ka yi wa bawanka? Gama ka san bawanka,
Kaj ti lahko David še govori glede časti tvojega služabnika? Kajti poznaš svojega služabnika.
19 Ya Ubangiji. Gama saboda bawanka da kuma bisa ga nufinka, ka yi wannan babban abu, ka kuma sanar da dukan manyan alkawura.
Oh Gospod, zaradi svojega služabnika in glede na svoje lastno srce, si storil vso to veličino v tem, da si dal spoznati vse te velike stvari.
20 “Babu wani kamar ka, ya Ubangiji, babu kuma Allah sai kai, kamar yadda muka ji da kunnuwanmu.
Oh Gospod, nobenega ni podobnega tebi niti ni nobenega Boga poleg tebe, glede na vse, kar smo slišali s svojimi ušesi.
21 Wane ne kuma yake kamar mutanenka Isra’ila, al’umma guda a duniya wadda Allahnta ya fita don yă fanshi mutane wa kansa, ya kuma yi suna wa kansa, ya kuma aikata manyan abubuwa masu banmamaki masu banrazana ta wurin korin al’ummai daga gaban mutanenka, waɗanda ka fansa daga Masar?
Kateri narod na zemlji je podoben tvojemu ljudstvu Izraelu, ki ga je Bog šel odkupit, da postane njegovo lastno ljudstvo, da si si naredil ime veličine in strašnosti s pregonom narodov izpred svojega ljudstva, ki si ga odkupil iz Egipta?
22 Ka mai da mutanenka Isra’ila na kanka har abada, kuma kai, ya Ubangiji, ka zama Allahnsu.
Kajti svojemu ljudstvu Izraelu si storil, da bo tvoje lastno ljudstvo na veke; in ti, Gospod, postajaš njihov Bog.
23 “Yanzu kuwa, Ubangiji, bari alkawarin da ka yi game da bawanka da gidansa yă kahu har abada. Yi kamar yadda ka yi alkawari,
Zato sedaj, Gospod, naj bo stvar, ki si jo govoril glede svojega služabnika in glede njegove hiše, utrjena na veke in stôri, kakor si rekel.
24 saboda zai kahu kuma sunanka zai zama mai girma har abada. Sa’an nan mutane za su ce, ‘Ubangiji Maɗaukaki, Allah a bisa Isra’ila, Allahn Isra’ila ne!’ Kuma gidan bawanka Dawuda zai kahu a gabanka.
Naj bo to celo utrjeno, da bo tvoje ime lahko poveličano na veke, rekoč: › Gospod nad bojevniki je Izraelov Bog, celó Bog Izraelu‹ in naj bo hiša tvojega služabnika Davida utrjena pred teboj.
25 “Kai, Allahna, ka bayyana ga bawanka cewa za ka gina gida dominsa. Ta haka bawanka ya sami ƙarfin gwiwa ya yi addu’a gare ka.
Kajti ti, oh moj Bog, si povedal svojemu služabniku, da mu hočeš zgraditi hišo, zato je tvoj služabnik v svojem srcu našel, da moli pred teboj.
26 Ya Ubangiji, kai ne Allah! Ka yi alkawari abubuwa masu kyau wa bawanka.
In sedaj, Gospod, ti si Bog in to dobroto si obljubil svojemu služabniku.
27 Yanzu ka ji daɗi don ka albarkace gidan bawanka, don yă ci gaba har abada a gabanka; gama kai, ya Ubangiji, ka albarkace shi, ya kuma sami albarka ke nan har abada.”
Zdaj naj ti torej to ugaja, da blagosloviš hišo svojega služabnika, da bo ta lahko pred teboj na veke, kajti ti blagoslavljaš, oh Gospod in to bo blagoslovljeno na veke.«

< 1 Tarihi 17 >