< 1 Tarihi 17 >

1 Bayan Dawuda ya zauna a fadansa, sai ya ce wa annabi Natan, “Ga ni, ina zama a fadar da aka yi da al’ul, yayinda akwatin alkawarin Ubangiji yana a ƙarƙashin tenti.”
And it was just when he dwelt David in house his and he said David to Nathan the prophet here! I [am] dwelling in [the] house of cedar and [the] ark of [the] covenant of Yahweh [is] under tent curtains.
2 Natan ya amsa wa Dawuda ya ce, “Duk abin da kake tunani a zuciya, ka yi, gama Allah yana tare da kai.”
And he said Nathan to David all that [is] in heart your do for God [is] with you.
3 A daren nan maganar Allah ta zo wa Natan cewa,
And it was in the night that and it came [the] word of God to Nathan saying.
4 “Ka tafi ka faɗa wa bawana Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce ba kai ba ne za ka gida mini gidan da zan zauna a ciki.
Go and you will say to David servant my thus he says Yahweh not you you will build for me the house to dwell in.
5 Ban taɓa zama a gida daga ranar da na fito da Isra’ila daga Masar ba har wa yau. Na yi ta yawo daga gefen da aka kafa tenti zuwa wani, daga wannan wuri zuwa wancan.
For not I have dwelt in a house since the day when I brought up Israel until the day this and I have been from tent to tent and from tabernacle.
6 Duk inda na tafi tare da Isra’ilawa, na taɓa ce wa wani daga cikin shugabanninsu waɗanda na umarta su yi kiwon mutanena, “Don me ba ku gida mini gidan al’ul ba?”’
In every where I went about in all Israel ¿ a word did I speak with one of [the] judges of Israel whom I commanded to shepherd people my saying why? not have you built for me a house of cedar.
7 “Yanzu, ka faɗa wa bawana Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, na ɗauke ka daga makiyaya da kuma daga bin garke, don ka zama mai mulki a bisa mutanena Isra’ila.
And therefore thus you will say to servant my to David. Thus he says Yahweh of hosts I I took you from the pasture from after the flock to be ruler over people my Israel.
8 Na kasance tare da kai ko’ina ka tafi, na kuma yanke dukan abokan gābanka a gabanka. Yanzu zan sa sunanka kamar sunayen mutane mafi girma na duniya.
And I was with you in every where you went and I cut off all enemies your from before you and I will make for you a name like [the] name of the great [people] who [are] on the earth.
9 Zan kuma tanada wuri domin mutanena Isra’ila, zan kuma kafa su saboda za su kasance da gidan kansu ba kuwa za a ƙara damunsu ba. Mugayen mutane ba za su ƙara zaluntar su ba, yadda suka yi da farko
And I will establish a place for people my Israel and I will plant it and it will dwell in place its and not it will be agitated again and not they will repeat [the] sons of injustice to consume it just as at the former [time].
10 da kuma suka yi tun lokacin da na sa shugabanni a bisa mutanen Isra’ila. Zan rinjaye dukan abokan gābanka. “‘Na furta maka cewa Ubangiji zai gina maka gida,
And from days when I appointed judges over people my Israel and I will subdue all enemies your and I have told to you and a house he will build for you Yahweh.
11 sa’ad da kwanakinka suka ƙare ka kuma tafi don ka kasance da kakanninka, zan tā da ɗaya cikin’ya’yanka maza, daga zuriyarka yă gāje ka, zan kuma kafa mulkinka.
And it will be that they have been completed days your to go with ancestors your and I will raise up offspring your after you who he will be one of descendants your and I will establish kingdom his.
12 Shi ne zai gina gida domina, zan kuma kafa sarautarsa har abada.
He he will build for me a house and I will establish throne his until perpetuity.
13 Zan zama Ubansa, zai kuma zama ɗana. Ba zan taɓa ɗauke ƙaunata daga gare shi, kamar yadda na ɗauke ta daga wanda ya riga ka ba.
I I will become of him a father and he he will become of me a son and covenant loyalty my not I will remove from with him just as I removed [it] from [the one] who he was before you.
14 Zan sa shi a bisa gidana da mulkina har abada; kujerar sarautarsa za tă kahu har abada.’”
And I will appoint him in house my and in kingdom my until perpetuity and throne his it will be established until perpetuity.
15 Natan ya faɗa wa Dawuda dukan kalmomin wahayin nan.
According to all the words these and according to all the vision this so he spoke Nathan to David.
16 Sai Sarki Dawuda ya shiga ya zauna a gaban Ubangiji ya ce, “Wane ne ni, ya Ubangiji Allah, kuma wane ne iyalina, da ka kawo ni har zuwa nan?
And he went the king David and he sat before Yahweh and he said who? [am] I O Yahweh God and who? [is] house my that you have brought me to here.
17 Kuma sai ka ce wannan bai isa ba a idonka, ya Allah, ka yi magana game da nan gaba na gidan bawanka. Ka dube ni sai ka ce ni ne mafi ɗaukaka cikin mutane, ya Ubangiji Allah.
And it was small this in view your O God and you have spoken on [the] house of servant your from distant [time] and you have seen me according to [the] order of humankind the going up O Yahweh God.
18 “Me kuma Dawuda zai ce maka saboda girmamawar da ka yi wa bawanka? Gama ka san bawanka,
What? will he add again David to you for honor servant your and you servant your you know.
19 Ya Ubangiji. Gama saboda bawanka da kuma bisa ga nufinka, ka yi wannan babban abu, ka kuma sanar da dukan manyan alkawura.
O Yahweh for sake of servant your and according to heart your you have done all the greatness this by making known all the greatness.
20 “Babu wani kamar ka, ya Ubangiji, babu kuma Allah sai kai, kamar yadda muka ji da kunnuwanmu.
O Yahweh there not [is] like you and there not [is] a God except you in all that we have heard with ears our.
21 Wane ne kuma yake kamar mutanenka Isra’ila, al’umma guda a duniya wadda Allahnta ya fita don yă fanshi mutane wa kansa, ya kuma yi suna wa kansa, ya kuma aikata manyan abubuwa masu banmamaki masu banrazana ta wurin korin al’ummai daga gaban mutanenka, waɗanda ka fansa daga Masar?
And who? [is] like people your Israel a nation one on the earth which he went God to redeem for himself a people to make for yourself a name great things and awesome [deeds] by driving out from before people your which you had redeemed from Egypt nations.
22 Ka mai da mutanenka Isra’ila na kanka har abada, kuma kai, ya Ubangiji, ka zama Allahnsu.
And you made people your Israel - for yourself a people until perpetuity and you O Yahweh you became for them God.
23 “Yanzu kuwa, Ubangiji, bari alkawarin da ka yi game da bawanka da gidansa yă kahu har abada. Yi kamar yadda ka yi alkawari,
And now O Yahweh the word which you have spoken on servant your and on house his let it be established until perpetuity and do just as you have spoken.
24 saboda zai kahu kuma sunanka zai zama mai girma har abada. Sa’an nan mutane za su ce, ‘Ubangiji Maɗaukaki, Allah a bisa Isra’ila, Allahn Isra’ila ne!’ Kuma gidan bawanka Dawuda zai kahu a gabanka.
And it may be established so it may be great name your until perpetuity saying Yahweh of hosts [is] [the] God of Israel God to Israel and [the] house of David servant your [is] established before you.
25 “Kai, Allahna, ka bayyana ga bawanka cewa za ka gina gida dominsa. Ta haka bawanka ya sami ƙarfin gwiwa ya yi addu’a gare ka.
For - you O God my you have uncovered [the] ear of servant your to build for him a house there-fore he has found servant your to pray before you.
26 Ya Ubangiji, kai ne Allah! Ka yi alkawari abubuwa masu kyau wa bawanka.
And now O Yahweh you he [are] God and you have spoken on servant your the good thing this.
27 Yanzu ka ji daɗi don ka albarkace gidan bawanka, don yă ci gaba har abada a gabanka; gama kai, ya Ubangiji, ka albarkace shi, ya kuma sami albarka ke nan har abada.”
And now you have determined to bless [the] house of servant your to be for ever before you for you O Yahweh you have blessed and [it is] blessed for ever.

< 1 Tarihi 17 >