< 1 Tarihi 17 >
1 Bayan Dawuda ya zauna a fadansa, sai ya ce wa annabi Natan, “Ga ni, ina zama a fadar da aka yi da al’ul, yayinda akwatin alkawarin Ubangiji yana a ƙarƙashin tenti.”
And it came to pass, when David dwelt in his house, that David said to Nathan the prophet: 'Lo, I dwell in a house of cedar, but the ark of the covenant of the LORD dwelleth under curtains.'
2 Natan ya amsa wa Dawuda ya ce, “Duk abin da kake tunani a zuciya, ka yi, gama Allah yana tare da kai.”
And Nathan said unto David: 'Do all that is in thy heart; for God is with thee.'
3 A daren nan maganar Allah ta zo wa Natan cewa,
And it came to pass the same night, that the word of God came to Nathan, saying:
4 “Ka tafi ka faɗa wa bawana Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce ba kai ba ne za ka gida mini gidan da zan zauna a ciki.
'Go and tell David My servant: Thus saith the LORD: Thou shalt not build Me a house to dwell in;
5 Ban taɓa zama a gida daga ranar da na fito da Isra’ila daga Masar ba har wa yau. Na yi ta yawo daga gefen da aka kafa tenti zuwa wani, daga wannan wuri zuwa wancan.
for I have not dwelt in a house since the day that I brought up Israel, unto this day; but have gone from tent to tent, and from one tabernacle to another.
6 Duk inda na tafi tare da Isra’ilawa, na taɓa ce wa wani daga cikin shugabanninsu waɗanda na umarta su yi kiwon mutanena, “Don me ba ku gida mini gidan al’ul ba?”’
In all places wherein I have walked among all Israel, spoke I a word with any of the judges of Israel, whom I commanded to feed My people, saying: Why have ye not built Me a house of cedar?
7 “Yanzu, ka faɗa wa bawana Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, na ɗauke ka daga makiyaya da kuma daga bin garke, don ka zama mai mulki a bisa mutanena Isra’ila.
Now therefore thus shalt thou say unto My servant David: Thus saith the LORD of hosts: I took thee from the sheepcote, from following the sheep, that thou shouldest be prince over My people Israel;
8 Na kasance tare da kai ko’ina ka tafi, na kuma yanke dukan abokan gābanka a gabanka. Yanzu zan sa sunanka kamar sunayen mutane mafi girma na duniya.
and I have been with thee whithersoever thou wentest, and have cut off all thine enemies from before thee; and I will make thee a name, like unto the name of the great ones that are in the earth.
9 Zan kuma tanada wuri domin mutanena Isra’ila, zan kuma kafa su saboda za su kasance da gidan kansu ba kuwa za a ƙara damunsu ba. Mugayen mutane ba za su ƙara zaluntar su ba, yadda suka yi da farko
And I will appoint a place for My people Israel, and will plant them, that they may dwell in their own place, and be disquieted no more; neither shall the children of wickedness waste them any more, as at the first,
10 da kuma suka yi tun lokacin da na sa shugabanni a bisa mutanen Isra’ila. Zan rinjaye dukan abokan gābanka. “‘Na furta maka cewa Ubangiji zai gina maka gida,
even from the day that I commanded judges to be over My people Israel; and I will subdue all thine enemies. Moreover I tell thee that the LORD will build thee a house.
11 sa’ad da kwanakinka suka ƙare ka kuma tafi don ka kasance da kakanninka, zan tā da ɗaya cikin’ya’yanka maza, daga zuriyarka yă gāje ka, zan kuma kafa mulkinka.
And it shall come to pass, when thy days are fulfilled that thou must go to be with thy fathers, that I will set up thy seed after thee, who shall be of thy sons; and I will establish his kingdom.
12 Shi ne zai gina gida domina, zan kuma kafa sarautarsa har abada.
He shall build Me a house, and I will establish his throne for ever.
13 Zan zama Ubansa, zai kuma zama ɗana. Ba zan taɓa ɗauke ƙaunata daga gare shi, kamar yadda na ɗauke ta daga wanda ya riga ka ba.
I will be to him for a father, and he shall be to Me for a son; and I will not take My mercy away from him, as I took it from him that was before thee;
14 Zan sa shi a bisa gidana da mulkina har abada; kujerar sarautarsa za tă kahu har abada.’”
but I will settle him in My house and in My kingdom for ever; and his throne shall be established for ever.'
15 Natan ya faɗa wa Dawuda dukan kalmomin wahayin nan.
According to all these words, and according to all this vision, so did Nathan speak unto David.
16 Sai Sarki Dawuda ya shiga ya zauna a gaban Ubangiji ya ce, “Wane ne ni, ya Ubangiji Allah, kuma wane ne iyalina, da ka kawo ni har zuwa nan?
Then David the king went in, and sat before the LORD; and he said: 'Who am I, O LORD God, and what is my house, that Thou hast brought me thus far?
17 Kuma sai ka ce wannan bai isa ba a idonka, ya Allah, ka yi magana game da nan gaba na gidan bawanka. Ka dube ni sai ka ce ni ne mafi ɗaukaka cikin mutane, ya Ubangiji Allah.
And this was a small thing in Thine eyes, O God; but Thou hast spoken of Thy servant's house for a great while to come, and hast regarded me after the manner of a man of high degree, O LORD God.
18 “Me kuma Dawuda zai ce maka saboda girmamawar da ka yi wa bawanka? Gama ka san bawanka,
What can David say yet more unto Thee concerning the honour which is done to Thy servant? for Thou knowest Thy servant.
19 Ya Ubangiji. Gama saboda bawanka da kuma bisa ga nufinka, ka yi wannan babban abu, ka kuma sanar da dukan manyan alkawura.
O LORD, for Thy servant's sake, and according to Thine own heart, hast Thou wrought all this greatness, to make known all these great things.
20 “Babu wani kamar ka, ya Ubangiji, babu kuma Allah sai kai, kamar yadda muka ji da kunnuwanmu.
O LORD, there is none like Thee, neither is there any God beside Thee, according to all that we have heard with our ears.
21 Wane ne kuma yake kamar mutanenka Isra’ila, al’umma guda a duniya wadda Allahnta ya fita don yă fanshi mutane wa kansa, ya kuma yi suna wa kansa, ya kuma aikata manyan abubuwa masu banmamaki masu banrazana ta wurin korin al’ummai daga gaban mutanenka, waɗanda ka fansa daga Masar?
And who is like Thy people Israel, a nation one in the earth, whom God went to redeem unto Himself for a people, to make Thee a name by great and tremendous things, in driving out nations from before Thy people, whom Thou didst redeem out of Egypt.
22 Ka mai da mutanenka Isra’ila na kanka har abada, kuma kai, ya Ubangiji, ka zama Allahnsu.
For Thy people Israel didst Thou make Thine own people for ever; and Thou, LORD, becamest their God.
23 “Yanzu kuwa, Ubangiji, bari alkawarin da ka yi game da bawanka da gidansa yă kahu har abada. Yi kamar yadda ka yi alkawari,
And now, O LORD, let the word that Thou hast spoken concerning Thy servant, and concerning his house, be established for ever, and do as Thou hast spoken.
24 saboda zai kahu kuma sunanka zai zama mai girma har abada. Sa’an nan mutane za su ce, ‘Ubangiji Maɗaukaki, Allah a bisa Isra’ila, Allahn Isra’ila ne!’ Kuma gidan bawanka Dawuda zai kahu a gabanka.
Yea, let it be established, and let Thy name be magnified for ever, that it may be said: The LORD of hosts is the God of Israel, even a God to Israel; and the house of David Thy servant shall be established before Thee.
25 “Kai, Allahna, ka bayyana ga bawanka cewa za ka gina gida dominsa. Ta haka bawanka ya sami ƙarfin gwiwa ya yi addu’a gare ka.
For Thou, O my God, hast revealed to Thy servant that Thou wilt build him a house; therefore hath Thy servant taken heart to pray before Thee.
26 Ya Ubangiji, kai ne Allah! Ka yi alkawari abubuwa masu kyau wa bawanka.
And now, O LORD, Thou alone art God, and hast promised this good thing unto Thy servant;
27 Yanzu ka ji daɗi don ka albarkace gidan bawanka, don yă ci gaba har abada a gabanka; gama kai, ya Ubangiji, ka albarkace shi, ya kuma sami albarka ke nan har abada.”
and now it hath pleased Thee to bless the house of Thy servant, that it may continue for ever before Thee; for Thou, O LORD, hast blessed, and so let Thy servant be blessed for ever.'