< 1 Tarihi 16 >
1 Suka fa kawo akwatin alkawarin Allah, suka sa a cikin tentin da Dawuda ya kafa dominsa, suka kuma miƙa hadayun ƙonawa da hadayu na salama a gaban Allah.
Då de båro Guds ark in, satte de honom uti tabernaklet, som David honom beredt hade; och offrade bränneoffer och tackoffer för Gudi.
2 Bayan Dawuda ya gama miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama, sai ya albarkaci mutane a cikin sunan Ubangiji.
Och då David hade fullkomnat bränneoffren och tackoffren, välsignade han folket i Herrans Namn;
3 Sa’an nan ya ba da dunƙulen burodi da wainar dabino da kuma kauɗar zabibi ga kowane mutumin Isra’ila namiji da ta mace.
Och utskifte hvarjom och enom i Israel, både man och qvinno, ett stycke bröd, och kött, och ett mätt vin.
4 Ya sa Lawiyawa su yi hidima a gaban akwatin alkawarin Ubangiji, su ɗaukaka, su gode, su kuma yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Och han satte inför Herrans ark några Leviter till tjenare, att de skulle prisa, tacka och lofva Herran Israels Gud;
5 Asaf shi ne babba, sai Zakariya na biye, sa’an nan Ya’aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Mattitiya, Eliyab, Benahiya, Obed-Edom da Yehiyel. Su ne za su kaɗa molaye, da garayu, Asaf kuwa zai buga ganguna,
Nämliga Assaph den första, Zacharia den andra, Jegiel, Semiramoth, Jehiel, Mattithia, Eliab, Benaja, ObedEdom; och Jegiel med psaltare och harpor; men Assaph med klingande cymbaler;
6 Benahiya da Yahaziyel firistoci za su busa ƙahoni kullum a gaban akwatin alkawarin Allah.
Och Benaja och Jahasiel, Presterna, med trummeter, alltid för Guds förbunds ark.
7 A wannan rana, da farko, Dawuda ya sa Asaf da’yan’uwansa su rera wannan zabura ta yabo ga Ubangiji.
På den tiden beställde David i förstone att tacka Herranom, genom Assaph och hans bröder:
8 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku yi shelar sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
Tacker Herranom, prediker hans Namn; förkunner ibland folken hans verk.
9 Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan ayyukan banmamakinsa.
Sjunger honom, speler, och taler om all hans under.
10 Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
Lofver hans helga Namn; deras hjerta fröjde sig, som söka Herran.
11 Ku dogara ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
Söker efter Herran, och efter hans magt; söker hans ansigte alltid.
12 Ku tuna ayyukan banmamakin da ya aikata, mu’ujizansa da kuma hukuntai da ya yanke,
Tänker på hans under, som han gjort hafver; på hans under, och hans ord;
13 Ya ku zuriyar Isra’ila bayinsa, Ya ku’ya’yan Yaƙub maza, zaɓaɓɓunsa.
I Israels hans tjenares säd, I Jacobs hans utkorades barn.
14 Shi ne Ubangiji Allahnmu; hukuntansa suna a cikin dukan duniya.
Han är Herren vår Gud, han dömer i allo verldene.
15 Yakan tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
Kommer ihåg hans förbund evinnerliga; hvad han utlofvat hafver i tusende slägter;
16 alkawarin da ya yi wa Ibrahim rantsuwar da ya yi ga Ishaku.
Hvilket han gjort hafver med Abraham, och hans ed med Isaac.
17 Ya tabbatar da shi ga Yaƙub kamar ƙa’ida, ga Isra’ila kamar madawwamin alkawari.
Och han satte det Jacob till en rätt, och Israel till ett evigt förbund,
18 “Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana kamar rabon da za ka gāda.”
Och sade: Jag skall gifva dig Canaans land, edar arfvedels lott.
19 Sa’ad da suke kima, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
Då de få och ringa voro, och främlingar derinne;
20 suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga wannan mulki zuwa wancan.
Och de drogo ifrå det ena folket till det andra, och utur ett rike bort till ett annat folk;
21 Bai bar wani ya zalunce su ba; saboda su ya tsawata wa sarakuna.
Han lät ingen göra dem skada; och för deras skull straffade han Konungar;
22 “Kada ku taɓa shafaffuna; kada ku yi wa annabawana lahani.”
Kommer icke vid mina smorda; och görer intet ondt mina Propheter.
23 Ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
Sjunger Herranom all land; förkunner dageliga hans salighet.
24 Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, ayyukansa masu al’ajabai a cikin mutane.
Förtäljer ibland Hedningarna hans härlighet; och hans under ibland folken.
25 Gama Ubangiji mai girma ne ya kuma cancanci yabo; dole a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
Ty Herren är stor, och fast loflig; och underlig öfver alla gudar.
26 Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ya yi sammai.
Förty alle Hedningars gudar äro afgudar; men Herren hafver gjort himmelen.
27 Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da farin ciki suna a wurin zamansa.
Det står härliga och kosteliga till för honom, och går krafteliga och gladeliga till i hans rum.
28 Ku yabi Ubangiji, ku iyalan al’ummai, ku yabi ɗaukaka da ƙarfin Ubangiji,
Bärer fram Herranom, I folk; bärer fram Herranom äro och magt.
29 ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa. Ku kawo hadaya ku kuma zo gabansa; ku yi wa Ubangiji sujada cikin darajar tsarkinsa.
Bärer fram Herrans Namne äro; bärer fram skänker, och kommer för honom, och tillbeder Herran i heligo prydelse.
30 Ku yi rawar jiki a gabansa, ya ku duniya duka! Duniya ta kahu sosai; ba za tă jijjigu ba.
All verlden frukte för honom; han hafver befäst jordena, så att hon intet röres.
31 Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari su ce a cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki!”
Fröjde sig himmelen, och jorden vare glad; och man må säga ibland Hedningarna, att Herren är rådandes.
32 Bari teku da kome da yake cikinsa su yi ruri; bari gonaki da kome a cikinsu su yi farin ciki!
Hafvet dåne, och hvad deruti är; och marken vare glad, och hvad deruppå är.
33 Sa’an nan itatuwan jeji za su rera, za su rera don farin ciki a gaban Ubangiji, gama ya zo don yă hukunta duniya.
Fröjde sig all trä i skogen för Herranom: ty han kommer till att döma jordena.
34 Ku yi godiya ga Ubangiji, gama shi nagari ne; ƙaunarsa madawwamiya ce.
Tacker Herranom, ty han är god, och hans barmhertighet varar evinnerliga.
35 Ku yi kuka, ku ce, “Cece mu, ya Allah Mai Cetonmu; tara mu ka kuma cece mu daga al’ummai, don mu yi godiya ga sunanka mai tsarki, don mu ɗaukaka a cikin yabonka.”
Och säger: Hjelp oss, Gud vår Frälsare, och församla oss, och hjelp oss ifrå Hedningarna, att vi måge tacka dino helgo Namne, och lofsäga dig.
36 Yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Sai dukan mutane suka ce, “Amin.” Suka kuma “Yabi Ubangiji.”
Lofvad vare Herren Israels Gud, ifrån evighet till evighet; och allt folket säge Amen, och lofve Herran.
37 Dawuda ya bar Asaf da’yan’uwansa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji don su yi hidima a can kullum, bisa ga tsari na kowace rana.
Alltså lät han der för Herrans förbunds ark Assaph och hans bröder, till att tjena inför arken alltid, och hvar dag i sitt dagsverk;
38 Ya kuma bar Obed-Edom da’yan’uwansa sittin da takwas don su yi hidima tare. Obed-Edom ɗan Yedutun da Hosa kuma, su ne matsaran ƙofofi.
Men ObedEdom och hans bröder, åtta och sextio; och ObedEdom, Jeduthuns son, och Hosa till dörravaktare;
39 Dawuda ya bar Zadok firist da’yan’uwansa firistoci a gaban tabanakul na Ubangiji a tudun da yake a Gibeyon
Och Zadok Presten, och hans bröder Presterna, lät han inför Herrans tabernakel, på höjdene i Gibeon;
40 don su miƙa hadayun ƙonawa ga Ubangiji a kan bagaden hadaya ta ƙonawa kullum, da safe da kuma yamma, bisa ga kome da yake a rubutacce a cikin Dokar Ubangiji, da ya ba wa Isra’ila.
Att de dageliga skulle göra Herranom bränneoffer, uppå bränneoffrens altare, om morgon och afton, såsom skrifvet står uti Herrans lag, som han Israel budit hade;
41 Tare da su akwai Heman da Yedutun da sauran waɗannan zaɓaɓɓun da aka rubuta sunansu don yin godiya ga Ubangiji, “gama ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Och med dem Heman och Jeduthun, och de andra utvalda, som vid namn benämnde voro, till att tacka Herranom, att hans barmhertighet varar evinnerliga;
42 Heman da Yedutun su ne da hakkin busa ƙahoni da kaɗa kuge da sauran kayan bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe, waɗanda ake amfani da su lokacin da ake rera waƙoƙi masu tsarki.’Ya’yan Yedutun maza, su aka ba wa aikin tsaron ƙofa.
Och med dem Heman och Jeduthun, med trummeter och cymbaler, till att klinga, och med Guds strängaspel. Men Jeduthuns söner gjorde han till dörravaktare.
43 Sa’an nan dukan mutanen suka tashi, kowa ya koma gidansa, Dawuda ya koma gida yă sa wa iyalinsa albarka.
Alltså drog allt folket sin väg, hvar och en i sitt hus. Drog också David bort till att välsigna sitt hus.