< 1 Tarihi 16 >

1 Suka fa kawo akwatin alkawarin Allah, suka sa a cikin tentin da Dawuda ya kafa dominsa, suka kuma miƙa hadayun ƙonawa da hadayu na salama a gaban Allah.
Trazendo pois a arca de Deus, a puseram no meio da tenda que David lhe tinha armado; e ofereceram holocaustos e sacrifícios pacíficos perante Deus.
2 Bayan Dawuda ya gama miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama, sai ya albarkaci mutane a cikin sunan Ubangiji.
E, acabando David de oferecer os holocaustos e sacrifícios pacíficos, abençoou o povo em nome do Senhor.
3 Sa’an nan ya ba da dunƙulen burodi da wainar dabino da kuma kauɗar zabibi ga kowane mutumin Isra’ila namiji da ta mace.
E repartiu a todos em Israel, tanto a homens como a mulheres, a cada um um pão, e um bom pedaço de carne, e um frasco de vinho.
4 Ya sa Lawiyawa su yi hidima a gaban akwatin alkawarin Ubangiji, su ɗaukaka, su gode, su kuma yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila.
E pôs perante a arca do Senhor alguns dos levitas por ministros; e isto para recordarem, e louvarem, e celebrarem ao Senhor Deus de Israel.
5 Asaf shi ne babba, sai Zakariya na biye, sa’an nan Ya’aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Mattitiya, Eliyab, Benahiya, Obed-Edom da Yehiyel. Su ne za su kaɗa molaye, da garayu, Asaf kuwa zai buga ganguna,
Era Asaph o chefe, e Zacarias o segundo depois dele: Jeiel, e Semiramoth, e Jehiel, e Mattithias, e Eliab, e Benaias, e Obed-edom, e Jeiel, com alaúdes e com harpas; e Asaph se fazia ouvir com címbalos;
6 Benahiya da Yahaziyel firistoci za su busa ƙahoni kullum a gaban akwatin alkawarin Allah.
Também Benaias, e Jahaziel, os sacerdotes, continuamente com trombetas, perante a arca do concerto de Deus.
7 A wannan rana, da farko, Dawuda ya sa Asaf da’yan’uwansa su rera wannan zabura ta yabo ga Ubangiji.
Então naquele mesmo dia entregou David em primeiro lugar o salmo seguinte, para louvarem ao Senhor, pelo ministério de Asaph e de seus irmãos:
8 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku yi shelar sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
Louvai ao Senhor, invocai o seu nome, fazei conhecidos entre os povos os seus feitos.
9 Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan ayyukan banmamakinsa.
Cantai-lhe, salmodiai-lhe, atentamente falai de todas as suas maravilhas.
10 Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
Glóriai-vos no seu santo nome; alegre-se o coração dos que buscam ao Senhor.
11 Ku dogara ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
Buscai ao Senhor, e a sua força; buscai a sua face continuamente.
12 Ku tuna ayyukan banmamakin da ya aikata, mu’ujizansa da kuma hukuntai da ya yanke,
Lembrai-vos das suas maravilhas que tem feito, de seus prodígios, e dos juízos da sua boca.
13 Ya ku zuriyar Isra’ila bayinsa, Ya ku’ya’yan Yaƙub maza, zaɓaɓɓunsa.
Vós, semente de Israel, seus servos, vós, filhos de Jacob, seus eleitos.
14 Shi ne Ubangiji Allahnmu; hukuntansa suna a cikin dukan duniya.
Ele é o Senhor nosso Deus; em toda a terra estão os seus juízos.
15 Yakan tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
Lembrai-vos perpetuamente do seu concerto e da palavra que prescreveu para mil gerações;
16 alkawarin da ya yi wa Ibrahim rantsuwar da ya yi ga Ishaku.
Do concerto que contratou com Abraão, e do seu juramento a Isaac;
17 Ya tabbatar da shi ga Yaƙub kamar ƙa’ida, ga Isra’ila kamar madawwamin alkawari.
O qual também a Jacob ratificou por estatuto, e a Israel por concerto eterno,
18 “Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana kamar rabon da za ka gāda.”
Dizendo: A ti te darei a terra de Canaan, quinhão da vossa herança.
19 Sa’ad da suke kima, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
Sendo vós em pequeno número, poucos homens, e estrangeiros nela.
20 suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga wannan mulki zuwa wancan.
E andaram de nação em nação, e dum reino para outro povo.
21 Bai bar wani ya zalunce su ba; saboda su ya tsawata wa sarakuna.
A ninguém permitiu que os oprimisse, e por amor deles repreendeu reis, dizendo:
22 “Kada ku taɓa shafaffuna; kada ku yi wa annabawana lahani.”
Não toqueis os meus ungidos, e aos meus profetas não façais mal.
23 Ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
Cantai ao Senhor em toda a terra; anunciai de dia em dia a sua salvação.
24 Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, ayyukansa masu al’ajabai a cikin mutane.
Contai entre as nações a sua glória, entre todos os povos as suas maravilhas.
25 Gama Ubangiji mai girma ne ya kuma cancanci yabo; dole a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
Porque grande é o Senhor, e muito para louvar, e mais tremendo é do que todos os deuses.
26 Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ya yi sammai.
Porque todos os deuses das nações são vaidades; porém o Senhor fez os céus.
27 Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da farin ciki suna a wurin zamansa.
Magestade e esplendor há diante dele, força e alegria no seu lugar.
28 Ku yabi Ubangiji, ku iyalan al’ummai, ku yabi ɗaukaka da ƙarfin Ubangiji,
Dai ao Senhor, ó famílias das nações, dai ao Senhor glória e força.
29 ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa. Ku kawo hadaya ku kuma zo gabansa; ku yi wa Ubangiji sujada cikin darajar tsarkinsa.
Dai ao Senhor a glória de seu nome; trazei presentes, e vinde perante ele: adorai ao Senhor na beleza da sua santidade.
30 Ku yi rawar jiki a gabansa, ya ku duniya duka! Duniya ta kahu sosai; ba za tă jijjigu ba.
Trema perante ele, trema toda a terra; pois o mundo se afirmará, para que se não abale.
31 Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari su ce a cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki!”
Alegrem-se os céus, e regozije-se a terra; e diga-se entre as nações: O Senhor reina.
32 Bari teku da kome da yake cikinsa su yi ruri; bari gonaki da kome a cikinsu su yi farin ciki!
Brama o mar com a sua plenitude; exulte o campo com tudo o que há nele.
33 Sa’an nan itatuwan jeji za su rera, za su rera don farin ciki a gaban Ubangiji, gama ya zo don yă hukunta duniya.
Então jubilarão as árvores dos bosques perante o Senhor; porquanto vem a julgar a terra.
34 Ku yi godiya ga Ubangiji, gama shi nagari ne; ƙaunarsa madawwamiya ce.
Louvai ao Senhor, porque é bom; pois a sua benignidade dura perpetuamente.
35 Ku yi kuka, ku ce, “Cece mu, ya Allah Mai Cetonmu; tara mu ka kuma cece mu daga al’ummai, don mu yi godiya ga sunanka mai tsarki, don mu ɗaukaka a cikin yabonka.”
E dizei: Salva-nos, ó Deus da nossa salvação, e ajunta-nos, e livra-nos das nações; para que louvemos o teu santo nome, e nos gloriemos do teu louvor.
36 Yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Sai dukan mutane suka ce, “Amin.” Suka kuma “Yabi Ubangiji.”
Louvado seja o Senhor Deus de Israel, de século em século. E todo o povo disse: amém! e louvou ao Senhor.
37 Dawuda ya bar Asaf da’yan’uwansa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji don su yi hidima a can kullum, bisa ga tsari na kowace rana.
Então deixou ali, diante da arca do concerto do Senhor, a Asaph e a seus irmãos, para ministrarem continuamente perante a arca, segundo se ordenara para cada dia.
38 Ya kuma bar Obed-Edom da’yan’uwansa sittin da takwas don su yi hidima tare. Obed-Edom ɗan Yedutun da Hosa kuma, su ne matsaran ƙofofi.
E mais a Obed-edom, com seus irmãos, sessenta e oito: a este Obed-edom, filho de Jeduthun, e a Hosa, ordenou por porteiros.
39 Dawuda ya bar Zadok firist da’yan’uwansa firistoci a gaban tabanakul na Ubangiji a tudun da yake a Gibeyon
E mais a Zadok, o sacerdote, e a seus irmãos, os sacerdotes, diante do tabernáculo do Senhor, no alto que está em Gibeon,
40 don su miƙa hadayun ƙonawa ga Ubangiji a kan bagaden hadaya ta ƙonawa kullum, da safe da kuma yamma, bisa ga kome da yake a rubutacce a cikin Dokar Ubangiji, da ya ba wa Isra’ila.
Para offerecerem ao Senhor os holocaustos sobre o altar dos holocaustos continuamente, pela manhã e à tarde: e isto segundo tudo o que está escrito na lei do Senhor que tinha prescrito a Israel.
41 Tare da su akwai Heman da Yedutun da sauran waɗannan zaɓaɓɓun da aka rubuta sunansu don yin godiya ga Ubangiji, “gama ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
E com eles a Heman, e a Jeduthun, e aos mais escolhidos, que foram apontados pelos seus nomes, para louvarem ao Senhor, porque a sua benignidade dura perpetuamente.
42 Heman da Yedutun su ne da hakkin busa ƙahoni da kaɗa kuge da sauran kayan bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe, waɗanda ake amfani da su lokacin da ake rera waƙoƙi masu tsarki.’Ya’yan Yedutun maza, su aka ba wa aikin tsaron ƙofa.
Com eles pois estavam Heman e Jeduthun, com trombetas e címbalos, para os que se faziam ouvir, e com instrumentos de música de Deus: porém os filhos de Jeduthun estavam à porta.
43 Sa’an nan dukan mutanen suka tashi, kowa ya koma gidansa, Dawuda ya koma gida yă sa wa iyalinsa albarka.
Então se foi todo o povo, cada um para a sua casa: e tornou David, para abençoar a sua casa.

< 1 Tarihi 16 >