< 1 Tarihi 16 >
1 Suka fa kawo akwatin alkawarin Allah, suka sa a cikin tentin da Dawuda ya kafa dominsa, suka kuma miƙa hadayun ƙonawa da hadayu na salama a gaban Allah.
So they brought the ark of God, and set it in the midst of the tent, which David had pitched for it: and they offered holocausts, and peace offerings before God.
2 Bayan Dawuda ya gama miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama, sai ya albarkaci mutane a cikin sunan Ubangiji.
And when David had made an end of offering holocausts, and peace offerings, he blessed the people in the name of the Lord.
3 Sa’an nan ya ba da dunƙulen burodi da wainar dabino da kuma kauɗar zabibi ga kowane mutumin Isra’ila namiji da ta mace.
And he divided to all and every one, both men and women, a loaf of bread, and a piece of roasted beef, and flour fried with oil.
4 Ya sa Lawiyawa su yi hidima a gaban akwatin alkawarin Ubangiji, su ɗaukaka, su gode, su kuma yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila.
And he appointed Levites to minister before the ark of the Lord, and to remember his works, and to glorify, and praise the Lord God of Israel.
5 Asaf shi ne babba, sai Zakariya na biye, sa’an nan Ya’aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Mattitiya, Eliyab, Benahiya, Obed-Edom da Yehiyel. Su ne za su kaɗa molaye, da garayu, Asaf kuwa zai buga ganguna,
Asaph the chief, and next after him Zacharias: moreover Jahiel, and Semiramoth, and Jehiel, and Mathathias, and Eliab, and Banaias, and Obededom: and Jehiel over the instruments of psaltery, and harps: and Asaph sounded with cymbals:
6 Benahiya da Yahaziyel firistoci za su busa ƙahoni kullum a gaban akwatin alkawarin Allah.
But Banaias, and Jaziel the priests, to sound the trumpet continually before the ark of the covenant of the Lord.
7 A wannan rana, da farko, Dawuda ya sa Asaf da’yan’uwansa su rera wannan zabura ta yabo ga Ubangiji.
In that day David made Asaph the chief to give praise to the Lord with his brethren.
8 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku yi shelar sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
Praise ye the Lord, and call upon his name: make known his doings among the nations.
9 Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan ayyukan banmamakinsa.
Sing to him, yea, sing praises to him: and relate all his wondrous works.
10 Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
Praise ye his holy name: let the heart I of them rejoice, that seek the Lord.
11 Ku dogara ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
Seek ye the Lord, and his power: seek ye his face evermore.
12 Ku tuna ayyukan banmamakin da ya aikata, mu’ujizansa da kuma hukuntai da ya yanke,
Remember his wonderful works, which he hath done: his signs, and the judgments of his mouth.
13 Ya ku zuriyar Isra’ila bayinsa, Ya ku’ya’yan Yaƙub maza, zaɓaɓɓunsa.
O ye seed of Israel his servants, ye children of Jacob his chosen.
14 Shi ne Ubangiji Allahnmu; hukuntansa suna a cikin dukan duniya.
He is the Lord our God: his judgments are in all the earth.
15 Yakan tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
Remember for ever his covenant: the word, which he commanded to a thousand generations.
16 alkawarin da ya yi wa Ibrahim rantsuwar da ya yi ga Ishaku.
The covenant which he made with Abraham: and his oath to Isaac.
17 Ya tabbatar da shi ga Yaƙub kamar ƙa’ida, ga Isra’ila kamar madawwamin alkawari.
And he appointed the same to Jacob for a precept: and to Israel for an everlasting covenant:
18 “Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana kamar rabon da za ka gāda.”
Saying: To thee will I give the land of Chanaan: the lot of your inheritance.
19 Sa’ad da suke kima, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
When they were but a small number: very few and sojourners in it.
20 suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga wannan mulki zuwa wancan.
And they passed from nation to nation: and from a kingdom to another people.
21 Bai bar wani ya zalunce su ba; saboda su ya tsawata wa sarakuna.
He suffered no man to do them wrong: and reproved kings for their sake.
22 “Kada ku taɓa shafaffuna; kada ku yi wa annabawana lahani.”
Touch not my anointed: and do no evil to my prophets.
23 Ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
Sing ye to the Lord, all the earth: shew forth from day to day his salvation.
24 Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, ayyukansa masu al’ajabai a cikin mutane.
Declare his glory among the Gentiles: his wonders among all people.
25 Gama Ubangiji mai girma ne ya kuma cancanci yabo; dole a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
For the Lord is great and exceedingly to be praised: and he is to be feared above all gods.
26 Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ya yi sammai.
For all the gods of the nations are idols: but the Lord made the heavens.
27 Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da farin ciki suna a wurin zamansa.
Praise and magnificence are before him: strength and joy in his place.
28 Ku yabi Ubangiji, ku iyalan al’ummai, ku yabi ɗaukaka da ƙarfin Ubangiji,
Bring ye to the Lord, O ye families of the nations: bring ye to the Lord glory and empire.
29 ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa. Ku kawo hadaya ku kuma zo gabansa; ku yi wa Ubangiji sujada cikin darajar tsarkinsa.
Give to the Lord glory to his name, bring up sacrifice, and come ye in his sight: and adore the Lord in holy becomingness.
30 Ku yi rawar jiki a gabansa, ya ku duniya duka! Duniya ta kahu sosai; ba za tă jijjigu ba.
Let all the earth be moved at his presence: for he hath founded the world immoveable.
31 Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari su ce a cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki!”
Let the heavens rejoice, and the earth be glad: and let them say among the nations: The Lord hath reigned.
32 Bari teku da kome da yake cikinsa su yi ruri; bari gonaki da kome a cikinsu su yi farin ciki!
Let the sea roar, and the fulness thereof: let the fields rejoice, and all things that are in them.
33 Sa’an nan itatuwan jeji za su rera, za su rera don farin ciki a gaban Ubangiji, gama ya zo don yă hukunta duniya.
Then shall the trees of the wood give praise before the Lord: because he is come to judge the earth.
34 Ku yi godiya ga Ubangiji, gama shi nagari ne; ƙaunarsa madawwamiya ce.
Give ye glory to the Lord, for he is good: for his mercy endureth for ever.
35 Ku yi kuka, ku ce, “Cece mu, ya Allah Mai Cetonmu; tara mu ka kuma cece mu daga al’ummai, don mu yi godiya ga sunanka mai tsarki, don mu ɗaukaka a cikin yabonka.”
And say ye: Save us, O God our saviour: and gather us together, and deliver us from the nations, that we may give glory to thy holy name, and may rejoice in singing thy praises.
36 Yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Sai dukan mutane suka ce, “Amin.” Suka kuma “Yabi Ubangiji.”
Blessed be the Lord the God of Israel from eternity to eternity: and let all the people say Amen, and a hymn to God.
37 Dawuda ya bar Asaf da’yan’uwansa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji don su yi hidima a can kullum, bisa ga tsari na kowace rana.
So he left there before the ark of the covenant of the Lord, Asaph and his brethren to minister in the presence of the ark continually day by day, and in their courses.
38 Ya kuma bar Obed-Edom da’yan’uwansa sittin da takwas don su yi hidima tare. Obed-Edom ɗan Yedutun da Hosa kuma, su ne matsaran ƙofofi.
And Obededom, with his brethren sixty-eight: and Obededom the son of Idithun, and Hosa he appointed to be porters.
39 Dawuda ya bar Zadok firist da’yan’uwansa firistoci a gaban tabanakul na Ubangiji a tudun da yake a Gibeyon
And Sadoc the priest, and his brethren priests, before the tabernacle of the Lord in the high place, which was in Gabaon.
40 don su miƙa hadayun ƙonawa ga Ubangiji a kan bagaden hadaya ta ƙonawa kullum, da safe da kuma yamma, bisa ga kome da yake a rubutacce a cikin Dokar Ubangiji, da ya ba wa Isra’ila.
That they should offer holocausts to the Lord upon the altar of holocausts continually, morning and evening, according to all that is written in the law of the Lord, which he commanded Israel.
41 Tare da su akwai Heman da Yedutun da sauran waɗannan zaɓaɓɓun da aka rubuta sunansu don yin godiya ga Ubangiji, “gama ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
And after him Heman, and Idithun, and the rest that were chosen, every one by his name to give praise to the Lord: because his mercy endureth for ever.
42 Heman da Yedutun su ne da hakkin busa ƙahoni da kaɗa kuge da sauran kayan bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe, waɗanda ake amfani da su lokacin da ake rera waƙoƙi masu tsarki.’Ya’yan Yedutun maza, su aka ba wa aikin tsaron ƙofa.
And Heman and Idithun sounded the trumpet, and played on the cymbals, and all kinds of musical instruments to sing praises to God: and the sons of Idithun he made porters.
43 Sa’an nan dukan mutanen suka tashi, kowa ya koma gidansa, Dawuda ya koma gida yă sa wa iyalinsa albarka.
And all the people returned to their houses: and David to bless also his own house.