< 1 Tarihi 16 >
1 Suka fa kawo akwatin alkawarin Allah, suka sa a cikin tentin da Dawuda ya kafa dominsa, suka kuma miƙa hadayun ƙonawa da hadayu na salama a gaban Allah.
And they brought in the ark of God, and set it in the midst of the tent that David had pitched for it. And they offered burnt offerings and peace offerings before God.
2 Bayan Dawuda ya gama miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama, sai ya albarkaci mutane a cikin sunan Ubangiji.
And when David had made an end of offering the burnt offering and the peace offerings, he blessed the people in the name of Jehovah.
3 Sa’an nan ya ba da dunƙulen burodi da wainar dabino da kuma kauɗar zabibi ga kowane mutumin Isra’ila namiji da ta mace.
And he dealt to every one of Israel, both man and woman, to every one a loaf of bread, and a portion of flesh, and a cake of raisins.
4 Ya sa Lawiyawa su yi hidima a gaban akwatin alkawarin Ubangiji, su ɗaukaka, su gode, su kuma yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila.
And he appointed certain of the Levites to minister before the ark of Jehovah, and to celebrate and to thank and praise Jehovah, the God of Israel:
5 Asaf shi ne babba, sai Zakariya na biye, sa’an nan Ya’aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Mattitiya, Eliyab, Benahiya, Obed-Edom da Yehiyel. Su ne za su kaɗa molaye, da garayu, Asaf kuwa zai buga ganguna,
Asaph the chief, and second to him Zechariah, Jeiel, and Shemiramoth, and Jehiel, and Mattithiah, and Eliab, and Benaiah, and Obed-edom, and Jeiel, with psalteries and with harps, and Asaph with cymbals, sounding aloud,
6 Benahiya da Yahaziyel firistoci za su busa ƙahoni kullum a gaban akwatin alkawarin Allah.
and Benaiah and Jahaziel the priests with trumpets continually, before the ark of the covenant of God.
7 A wannan rana, da farko, Dawuda ya sa Asaf da’yan’uwansa su rera wannan zabura ta yabo ga Ubangiji.
Then on that day David first ordained to give thanks to Jehovah by the hand of Asaph and his brothers.
8 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku yi shelar sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
O give thanks to Jehovah. Call upon his name. Make known his doings among the peoples.
9 Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan ayyukan banmamakinsa.
Sing to him. Sing praises to him. Talk ye of all his marvelous works.
10 Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
Glory ye in his holy name. Let the heart of those who seek Jehovah rejoice.
11 Ku dogara ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
Seek ye Jehovah and his strength. Seek his face evermore.
12 Ku tuna ayyukan banmamakin da ya aikata, mu’ujizansa da kuma hukuntai da ya yanke,
Remember his marvelous works that he has done, his wonders, and the judgments of his mouth,
13 Ya ku zuriyar Isra’ila bayinsa, Ya ku’ya’yan Yaƙub maza, zaɓaɓɓunsa.
O ye seed of Israel his servant, ye sons of Jacob, his chosen ones.
14 Shi ne Ubangiji Allahnmu; hukuntansa suna a cikin dukan duniya.
He is Jehovah our God. His judgments are in all the earth.
15 Yakan tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
Remember his covenant forever, the word which he commanded to a thousand generations,
16 alkawarin da ya yi wa Ibrahim rantsuwar da ya yi ga Ishaku.
the covenant which he made with Abraham, and his oath to Isaac,
17 Ya tabbatar da shi ga Yaƙub kamar ƙa’ida, ga Isra’ila kamar madawwamin alkawari.
and confirmed the same to Jacob for a statute, to Israel for an everlasting covenant,
18 “Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana kamar rabon da za ka gāda.”
saying, To thee I will give the land of Canaan, the lot of your inheritance,
19 Sa’ad da suke kima, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
when ye were but a few men in number, yea, very few, and sojourners in it,
20 suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga wannan mulki zuwa wancan.
and they went about from nation to nation, and from one kingdom to another people.
21 Bai bar wani ya zalunce su ba; saboda su ya tsawata wa sarakuna.
He allowed no man to do them wrong. Yea, he reproved kings for their sakes,
22 “Kada ku taɓa shafaffuna; kada ku yi wa annabawana lahani.”
saying, Touch not my anointed ones, and do my prophets no harm.
23 Ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
Sing to Jehovah, all the earth. Show forth his salvation from day to day.
24 Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, ayyukansa masu al’ajabai a cikin mutane.
Declare his glory among the nations, his marvelous works among all the peoples.
25 Gama Ubangiji mai girma ne ya kuma cancanci yabo; dole a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
For great is Jehovah, and greatly to be praised. He also is to be feared above all gods.
26 Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ya yi sammai.
For all the gods of the peoples are idols. But Jehovah made the heavens.
27 Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da farin ciki suna a wurin zamansa.
Honor and majesty are before him. Strength and gladness are in his place.
28 Ku yabi Ubangiji, ku iyalan al’ummai, ku yabi ɗaukaka da ƙarfin Ubangiji,
Ascribe to Jehovah, ye kindred of the peoples. Ascribe to Jehovah glory and strength.
29 ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa. Ku kawo hadaya ku kuma zo gabansa; ku yi wa Ubangiji sujada cikin darajar tsarkinsa.
Ascribe to Jehovah the glory due to his name. Bring an offering, and come before him. Worship Jehovah in holy array.
30 Ku yi rawar jiki a gabansa, ya ku duniya duka! Duniya ta kahu sosai; ba za tă jijjigu ba.
Tremble before him, all the earth. The world also is established that it cannot be moved.
31 Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari su ce a cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki!”
Let the heavens be glad, and let the earth rejoice. And let them say among the nations, Jehovah reigns.
32 Bari teku da kome da yake cikinsa su yi ruri; bari gonaki da kome a cikinsu su yi farin ciki!
Let the sea roar, and the fullness of it. Let the field exult, and all that is therein.
33 Sa’an nan itatuwan jeji za su rera, za su rera don farin ciki a gaban Ubangiji, gama ya zo don yă hukunta duniya.
Then shall the trees of the wood sing for joy before Jehovah, for he comes to judge the earth.
34 Ku yi godiya ga Ubangiji, gama shi nagari ne; ƙaunarsa madawwamiya ce.
O give thanks to Jehovah, for he is good, for his loving kindness is forever.
35 Ku yi kuka, ku ce, “Cece mu, ya Allah Mai Cetonmu; tara mu ka kuma cece mu daga al’ummai, don mu yi godiya ga sunanka mai tsarki, don mu ɗaukaka a cikin yabonka.”
And say ye, Save us, O God of our salvation. And gather us together and deliver us from the nations, to give thanks to thy holy name, and to triumph in thy praise.
36 Yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Sai dukan mutane suka ce, “Amin.” Suka kuma “Yabi Ubangiji.”
Blessed be Jehovah, the God of Israel, from everlasting even to everlasting. And all the people said, Truly, and praised Jehovah.
37 Dawuda ya bar Asaf da’yan’uwansa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji don su yi hidima a can kullum, bisa ga tsari na kowace rana.
So he left there, before the ark of the covenant of Jehovah, Asaph and his brothers, to minister before the ark continually, as every day's work required,
38 Ya kuma bar Obed-Edom da’yan’uwansa sittin da takwas don su yi hidima tare. Obed-Edom ɗan Yedutun da Hosa kuma, su ne matsaran ƙofofi.
and Obed-edom with their sixty-eight brothers. And Obed-edom the son of Jeduthun and Hosah were to be porters,
39 Dawuda ya bar Zadok firist da’yan’uwansa firistoci a gaban tabanakul na Ubangiji a tudun da yake a Gibeyon
and Zadok the priest, and his brothers the priests, before the tabernacle of Jehovah in the high place that was at Gibeon,
40 don su miƙa hadayun ƙonawa ga Ubangiji a kan bagaden hadaya ta ƙonawa kullum, da safe da kuma yamma, bisa ga kome da yake a rubutacce a cikin Dokar Ubangiji, da ya ba wa Isra’ila.
to offer burnt offerings to Jehovah upon the altar of burnt offering continually morning and evening, even according to all that is written in the law of Jehovah, which he commanded to Israel.
41 Tare da su akwai Heman da Yedutun da sauran waɗannan zaɓaɓɓun da aka rubuta sunansu don yin godiya ga Ubangiji, “gama ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
And with them Heman and Jeduthun, and the rest that were chosen, who were mentioned by name, to give thanks to Jehovah because his loving kindness is forever.
42 Heman da Yedutun su ne da hakkin busa ƙahoni da kaɗa kuge da sauran kayan bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe, waɗanda ake amfani da su lokacin da ake rera waƙoƙi masu tsarki.’Ya’yan Yedutun maza, su aka ba wa aikin tsaron ƙofa.
And with them Heman and Jeduthun with trumpets and cymbals for those who should sound aloud, and with instruments for the songs of God, and the sons of Jeduthun to be at the gate.
43 Sa’an nan dukan mutanen suka tashi, kowa ya koma gidansa, Dawuda ya koma gida yă sa wa iyalinsa albarka.
And all the people departed every man to his house. And David returned to bless his house.